< 1 Sarakuna 21 >
1 Ana nan bayan haka sai waɗannan abubuwa suka faru. Nabot mutumin Yezireyel yana da gonar inabi a Yezireyel, a yankin Samariya, kusa da gidan Sarki Ahab.
Or il arriva après ces choses, que Naboth Jizréhélite, ayant une vigne à Jizréhel, près du palais d'Achab, Roi de Samarie;
2 Sai Ahab ya ce wa Nabot, “Ka ba ni gonar inabinka in yi amfani da ita don kayan lambu, da yake tana kusa da fadana. Zan ba ka wata gonar inabin da ta fi wannan, ko kuma in ka gwammace, sai in biya ka duk abin da ya dace da ita.”
Achab parla à Naboth, et lui dit: Cède-moi ta vigne, afin que j'en fasse un jardin de verdure; car elle est proche de ma maison, et je t'en donnerai pour celle-là une meilleure; ou si cela t'accommode mieux, je t'en donnerai l'argent qu'elle vaut.
3 Amma Nabot ya amsa wa Ahab ya ce, “Ubangiji yă sawwaƙe in ba ka gādon kakannina.”
Mais Naboth répondit à Achab: A Dieu ne plaise que je te cède l'héritage de mes pères!
4 Ahab ya cika da fushi saboda Nabot, mutumin Yezireyel ya ce, “Ba zan ba ka gādon kakannina ba.” Ya kwanta a gadonsa yana zub da hawaye, ya kuma ƙi cin abinci.
Et Achab vint en sa maison tout refrogné et indigné pour la parole que lui avait dite Naboth Jizréhélite, en disant: Je ne te céderai point l'héritage de mes pères; et il se coucha sur son lit, et tourna son visage, et ne mangea rien.
5 Matarsa Yezebel ta shiga ciki ta tambaye shi, ta ce, “Me ya sa ka kumbura? Me ya sa ba za ka ci abinci ba?”
Alors Izebel sa femme entra vers lui, et lui dit: D'où vient que ton esprit est si triste? et pourquoi ne manges-tu point?
6 Sai ya amsa mata, ya ce, “Domin na ce wa Nabot mutumin Yezireyel, ‘Ka sayar mini gonar inabinka; ko kuwa in ka gwammace, zan ba ka wata gonar inabi a maimakonta.’ Amma ya ce, ‘Ba zan ba ka gonar inabina ba.’”
Et il lui répondit: C'est parce qu'ayant parlé à Naboth Jizréhélite, et lui ayant dit: Donne-moi ta vigne pour de l'argent, ou si tu l'aimes mieux, je te donnerai une autre vigne pour celle-là, il m'a dit: Je ne te céderai point ma vigne.
7 Yezebel matarsa ta ce, “Yaya kake yi kamar ba kai ne sarki Isra’ila ba? Tashi ka ci abinci! Ka yi farin ciki. Zan ba ka gonar inabin Nabot mutumin Yezireyel.”
Alors Izebel sa femme lui dit: Serais-tu maintenant Roi sur Israël? Lève-toi, mange quelque chose, et que ton cœur se réjouisse; je te ferai avoir la vigne de Naboth Jizréhélite.
8 Sai ta rubuta wasiƙu a sunan Ahab, ta buga hatiminsa a kansu, sa’an nan ta aika su ga dattawa da manyan gari waɗanda suke zama a birnin da Nabot yake.
Et elle écrivit des Lettres au nom d'Achab, les scella du sceau du Roi, et elle envoya ces Lettres aux Anciens et Magistrats qui étaient dans la ville de Naboth, et qui y demeuraient avec lui.
9 Cikin waɗannan wasiƙu ta rubuta, “Ku yi shelar ranar azumi, ku zaunar da Nabot a wuri mai martaba a cikin mutane.
Et elle écrivit dans ces Lettres ce qui s'ensuit: Publiez le jeûne, et faites tenir Naboth au haut bout du peuple.
10 Amma ku zaunar da waɗansu’yan iska biyu ɗaura da shi, ku sa su ba da shaida cewa ya zagi Allah da sarki. Sa’an nan ku ɗauke shi ku jajjefe shi da dutse sai ya mutu.”
Et faites tenir deux méchants hommes vis-à-vis de lui, et qu'ils témoignent contre lui, en disant: Tu as blasphémé contre Dieu, et [mal parlé] du Roi; puis vous le mènerez dehors, et vous le lapiderez, et qu'il meure.
11 Sai dattawa da manyan gari, waɗanda suke zama a birnin da Nabot yake, suka yi kamar yadda Yezebel ta umarta a cikin wasiƙun da ta rubuta.
Les gens donc de la ville de Naboth, [savoir] les Anciens et les Magistrats qui demeuraient dans sa ville, firent comme Izebel leur avait mandé, [et] selon qu'il était écrit dans les Lettres qu'elle leur avait envoyées.
12 Suka yi shelar azumi, suka kuma zaunar da Nabot a wuri mai martaba a cikin mutane.
Car ils publièrent le jeûne, et firent tenir Naboth au haut bout du peuple.
13 Sa’an nan’yan iska biyu suka zo, suka zauna ɗaura da shi, suka kawo zarge a kan Nabot a gaban mutane, suna cewa, “Nabot ya zagi Allah da sarki.” Saboda haka aka ɗauke shi waje da birnin, aka jajjefe shi da dutse har ya mutu.
Et deux méchants hommes entrèrent, et se tinrent vis-à-vis de lui; et ces méchants hommes témoignèrent contre Naboth en la présence du peuple, en disant: Naboth a blasphémé contre Dieu, et il a [mal parlé] du Roi; puis ils le menèrent hors de la ville, et l'assommèrent de pierres, et il mourut.
14 Sa’an nan suka aika wa Yezebel. “An jajjefe Nabot, ya kuma mutu.”
Après cela ils envoyèrent vers Izebel, pour lui dire: Naboth a été lapidé, et il est mort.
15 Nan da nan sa’ad da Yezebel ta ji cewa an jajjefe Nabot da dutse ya kuma mutu, sai ta ce wa Ahab, “Tashi ka mallaki gonar inabin Nabot mutumin Yezireyel wanda ya ƙi ya sayar maka. Ba shi da rai, ya mutu.”
Et il arriva qu'aussitôt qu'Izebel eut entendu que Naboth avait été lapidé, et qu'il était mort, elle dit à Achab: Lève-toi, mets-toi en possession de la vigne de Naboth Jizréhélite, qui avait refusé de te la donner pour de l'argent; car Naboth n'est plus en vie, mais il est mort.
16 Da Ahab ya ji cewa Nabot ya mutu, sai ya tashi ya gangara don yă mallaki gonar inabin Nabot.
Ainsi dès qu'Achab eut entendu que Naboth était mort, il se leva pour descendre en la vigne de Naboth Jizréhélite, et pour s'en mettre en possession.
17 Sai maganar Ubangiji ta zo wa Iliya mutumin Tishbe.
Alors la parole de l'Eternel fut adressée à Elie Tisbite, en disant:
18 Ta ce, “Gangara don ka sadu da Ahab sarkin Isra’ila, wanda yake mulki a Samariya. Yanzu yana a gonar inabin Nabot, inda ya tafi yă mallake ta.
Lève-toi, descends au devant d'Achab Roi d'Israël, lorsqu'il sera à Samarie; voilà il est dans la vigne de Naboth, où il est descendu pour s'en mettre en possession.
19 Ka ce masa, Ga abin da Ubangiji ya ce, ‘Ba ka kashe mutum ka kuma ƙwace kayansa ba?’ Sa’an nan ka ce masa ga abin da Ubangiji ya ce, ‘A inda karnuka suka lashe jinin Nabot, karnuka za su lashe jininka, I, naka!’”
Et tu lui parleras, en disant: Ainsi a dit l'Eternel: N'as-tu pas tué, et ne t'es-tu pas même mis en possession? Puis tu lui parleras ainsi, et diras: Ainsi a dit l'Eternel: Comme les chiens ont léché le sang de Naboth, les chiens lécheront aussi ton propre sang.
20 Ahab ya ce wa Iliya, “Wato, ka same ni kuma, abokin gābana!” Sai ya amsa ya ce, “Na same ka, domin ka sayar da kanka ga yin mugunta a gaban Ubangiji.
Et Achab dit à Elie: M'as-tu trouvé toi, mon ennemi? Mais il lui répondit: Oui, je t'ai trouvé, parce que tu t'es vendu pour faire ce qui déplaît à l'Eternel.
21 ‘Zan kawo masifa a kanka. Zan kawar da zuriyarka, in kuma yanke daga Ahab kowane ɗa namiji na ƙarshe cikin Isra’ila, bawa ko’yantacce.
Voici je m'en vais amener du mal sur toi, et je t'exterminerai entièrement; et depuis l'homme jusqu'à un chien, je retrancherai ce qui appartient à Achab, tant ce qui est serré, que ce qui est délaissé en Israël.
22 Zan mai da gidanka kamar gida Yerobowam ɗan Nebat, da na Ba’asha ɗan Ahiya, domin ka tsokane ni har na yi fushi, ka kuma sa Isra’ila ya yi zunubi.’
Et je mettrai ta maison au même état que j'ai mis la maison de Jéroboam fils de Nébat, et la maison de Bahasa, fils d'Ahija à cause du péché par lequel tu m'as irrité, et as fait pécher Israël.
23 “Game da Yezebel kuwa Ubangiji ya ce, ‘Karnuka za su cinye Yezebel a katangar Yezireyel.’
L'Eternel parla aussi contre Izebel, disant: Les chiens mangeront Izebel près du rempart de Jizréhel.
24 “Karnuka za su cinye waɗanda suke na Ahab waɗanda suka mutu a cikin birni, tsuntsayen sararin sama kuma za su cinye waɗanda suka mutu a jeji.”
Celui qui appartient à Achab, [et] qui mourra dans la ville, les chiens le mangeront; et celui qui mourra aux champs, les oiseaux des cieux le mangeront.
25 (Babu wani mutum kamar Ahab, wanda ya ba da kansa ga aikata mugunta a gaban Ubangiji. Yezebel matarsa ce ta zuga shi.
En effet il n'y en avait point eu de semblable à Achab, qui se fût vendu pour faire ce qui déplaît à l'Eternel, selon que sa femme Izebel l'induisait.
26 Ya yi abar ƙyama ƙwarai ta wurin bin gumaka, kamar Amoriyawan da Ubangiji ya kora a gaban Isra’ila.)
De sorte qu'il se rendit fort abominable, allant après les dieux de fiente, selon tout ce qu'avaient fait les Amorrhéens que l'Eternel avait chassés de devant les enfants d'Israël.
27 Sa’ad da Ahab ya ji waɗannan kalmomi, sai ya yage rigarsa, ya sa rigunan makoki, ya kuma yi azumi. Ya kwanta a kayan makoki, ya kuma yi tafiya cikin sauƙinkai.
Et il arriva qu'aussitôt qu'Achab eut entendu ces paroles, il déchira ses vêtements, et mit un sac sur sa chair, et jeûna, et il se tenait couché, enveloppé d'un sac, et se traînait en marchant.
28 Sai maganar Ubangiji ta zo wa Iliya mutumin Tishbe, ta ce,
Et la parole de l'Eternel fut adressée à Elie Tisbite, en disant:
29 “Ka lura da yadda Ahab ya ƙasƙantar da kansa a gabana kuwa? Domin ya ƙasƙantar da kansa, ba zan kawo wannan masifa a kwanakinsa ba, amma zan kawo ta a kan gidansa a kwanakin ɗansa.”
N'as-tu pas vu qu'Achab s'est humilié devant moi? [Or] parce qu'il s'est humilié devant moi, je n'amènerai point ce mal en son temps, ce sera aux jours de son fils que j'amènerai ce mal sur sa maison.