< 1 Sarakuna 21 >

1 Ana nan bayan haka sai waɗannan abubuwa suka faru. Nabot mutumin Yezireyel yana da gonar inabi a Yezireyel, a yankin Samariya, kusa da gidan Sarki Ahab.
Forsothe after these wordis, in that tyme, the vyner of Naboth of Jezrael, `that was in Jezrael, was bisidis the paleis of Achab, kyng of Samarye.
2 Sai Ahab ya ce wa Nabot, “Ka ba ni gonar inabinka in yi amfani da ita don kayan lambu, da yake tana kusa da fadana. Zan ba ka wata gonar inabin da ta fi wannan, ko kuma in ka gwammace, sai in biya ka duk abin da ya dace da ita.”
Therfor Achab spak to Naboth, and seide, Yyue thou to me the vyner, that Y make to me a gardyn of wortis, for it is nyy, and nyy myn hows; and Y schal yyue to thee a betere vyner for it; ethir if thou gessist it more profitable to thee, Y schall yyue the prijs of siluer, as myche as it is worth.
3 Amma Nabot ya amsa wa Ahab ya ce, “Ubangiji yă sawwaƙe in ba ka gādon kakannina.”
To whom Naboth answeride, The Lord be merciful to me, that Y yyue not to thee the eritage of my fadris.
4 Ahab ya cika da fushi saboda Nabot, mutumin Yezireyel ya ce, “Ba zan ba ka gādon kakannina ba.” Ya kwanta a gadonsa yana zub da hawaye, ya kuma ƙi cin abinci.
Therfor Acab cam in to his hows, hauynge indignacioun, and gnastyng on the word which Naboth of Jezrael hadde spoke to him, and seide, Y schal not yyue to thee the eritage of my fadirs. And Achab castide doun him silf in to his bed, and turnede awei his face to the wal, and ete not breed.
5 Matarsa Yezebel ta shiga ciki ta tambaye shi, ta ce, “Me ya sa ka kumbura? Me ya sa ba za ka ci abinci ba?”
Forsothe Jezabel, his wijf, entride to hym, and seide to hym, What is this thing, wherof thi soule is maad sory? and whi etist thou not breed?
6 Sai ya amsa mata, ya ce, “Domin na ce wa Nabot mutumin Yezireyel, ‘Ka sayar mini gonar inabinka; ko kuwa in ka gwammace, zan ba ka wata gonar inabi a maimakonta.’ Amma ya ce, ‘Ba zan ba ka gonar inabina ba.’”
Which answeride to hir, Y spak to Naboth of Jezrael, and Y seide to hym, Yyue thi vyner to me for money takun, ethir if it plesith thee, Y schal yyue to thee a betere vyner for it. And he seide, Y schal not yyue to thee my vyner.
7 Yezebel matarsa ta ce, “Yaya kake yi kamar ba kai ne sarki Isra’ila ba? Tashi ka ci abinci! Ka yi farin ciki. Zan ba ka gonar inabin Nabot mutumin Yezireyel.”
Therfor Jezabel, his wijf, seide to hym, Thou art of greet auctorite, and thou gouernest wel Israel; rise thou, and ete breed, and be thou `pacient, ethir coumfortid; Y schal yyue to thee the vyner of Naboth of Jezrael.
8 Sai ta rubuta wasiƙu a sunan Ahab, ta buga hatiminsa a kansu, sa’an nan ta aika su ga dattawa da manyan gari waɗanda suke zama a birnin da Nabot yake.
Therfor sche wroot lettris in the name of Achab, and seelide tho with the ryng of hym; and sche sente to the grettere men in birthe, and to the beste men, that weren in the citee of hym, and dwelliden with Naboth.
9 Cikin waɗannan wasiƙu ta rubuta, “Ku yi shelar ranar azumi, ku zaunar da Nabot a wuri mai martaba a cikin mutane.
Sotheli this was the sentence of the lettre; Preche ye fastyng, and make ye Naboth to sitte among the firste men of the puple;
10 Amma ku zaunar da waɗansu’yan iska biyu ɗaura da shi, ku sa su ba da shaida cewa ya zagi Allah da sarki. Sa’an nan ku ɗauke shi ku jajjefe shi da dutse sai ya mutu.”
and sende ye priueli twei men, the sones of Belial, ayens hym, and sey thei fals witnessyng, Naboth blesside God and the kyng; and lede ye out hym, and stoon ye him, and die he so.
11 Sai dattawa da manyan gari, waɗanda suke zama a birnin da Nabot yake, suka yi kamar yadda Yezebel ta umarta a cikin wasiƙun da ta rubuta.
Therfor hise citeseyns, the grettere men in birthe, and the beste men that dwelliden with hym in the citee, diden as Jezabel hadde comaundid, and as it was writun in the lettris, whiche sche hadde sent to hem.
12 Suka yi shelar azumi, suka kuma zaunar da Nabot a wuri mai martaba a cikin mutane.
Thei prechiden fastyng, and maden Naboth to sitte among the firste men of the puple;
13 Sa’an nan’yan iska biyu suka zo, suka zauna ɗaura da shi, suka kawo zarge a kan Nabot a gaban mutane, suna cewa, “Nabot ya zagi Allah da sarki.” Saboda haka aka ɗauke shi waje da birnin, aka jajjefe shi da dutse har ya mutu.
and whanne twey men, sones of the deuel, weren brouyt, thei maden hem to sitte ayens hym, and thei, that is, as men of the deuel, seiden witnessyng ayens him bifor al the multitude, Naboth blesside God and the kyng; for which thing thei ledden hym with out the citee, and killiden him with stoonys.
14 Sa’an nan suka aika wa Yezebel. “An jajjefe Nabot, ya kuma mutu.”
And thei senten to Jezabel, and seiden, Naboth is stoonyd, and is deed.
15 Nan da nan sa’ad da Yezebel ta ji cewa an jajjefe Nabot da dutse ya kuma mutu, sai ta ce wa Ahab, “Tashi ka mallaki gonar inabin Nabot mutumin Yezireyel wanda ya ƙi ya sayar maka. Ba shi da rai, ya mutu.”
Forsothe it was doon, whanne Jezabel hadde herd Naboth stonyd and deed, sche spak to Achab, Rise thou, take thou in possessioun the vyner of Naboth of Jezrael, which nolde assente to thee, and yyue it for money takun; for Naboth lyueth not, but is deed.
16 Da Ahab ya ji cewa Nabot ya mutu, sai ya tashi ya gangara don yă mallaki gonar inabin Nabot.
And whanne Achab hadde herd this, that is, Naboth deed, he roos, and yede doun in to the vyner of Naboth of Jezrael, to haue it in possessioun.
17 Sai maganar Ubangiji ta zo wa Iliya mutumin Tishbe.
Therfor the word of the Lord was maad to Elie of Thesbi,
18 Ta ce, “Gangara don ka sadu da Ahab sarkin Isra’ila, wanda yake mulki a Samariya. Yanzu yana a gonar inabin Nabot, inda ya tafi yă mallake ta.
and seide, Rise thou, go doun in to the comyng of Achab, kyng of Israel, which is in Samarie; lo! he goith doun to the vyner of Naboth, that he haue it in possessioun.
19 Ka ce masa, Ga abin da Ubangiji ya ce, ‘Ba ka kashe mutum ka kuma ƙwace kayansa ba?’ Sa’an nan ka ce masa ga abin da Ubangiji ya ce, ‘A inda karnuka suka lashe jinin Nabot, karnuka za su lashe jininka, I, naka!’”
And thou schalt speke to hym, and `thou schalt seie, The Lord God seith these thingis, Thou hast slayn, ferthermore and thou hast take in possessioun; and aftir these thingis thou schalt adde, In this place, wherynne doggis lickiden the blood of Naboth, thei schulen licke also thi blood.
20 Ahab ya ce wa Iliya, “Wato, ka same ni kuma, abokin gābana!” Sai ya amsa ya ce, “Na same ka, domin ka sayar da kanka ga yin mugunta a gaban Ubangiji.
And Achab seyde to Elie, Whether thou hast founde me thin enemy? Which Elie seide, Y haue founde, for thou art seeld that thou schuldist do yuel in the siyt of the Lord.
21 ‘Zan kawo masifa a kanka. Zan kawar da zuriyarka, in kuma yanke daga Ahab kowane ɗa namiji na ƙarshe cikin Isra’ila, bawa ko’yantacce.
Therfor the Lord seith these thingis, Lo! Y schal brynge yn on thee yuel, and Y schal kitte awey thin hyndrere thingis, and Y schal sle of Achab a pissere to the wal, and prisoned, and the laste in Israel;
22 Zan mai da gidanka kamar gida Yerobowam ɗan Nebat, da na Ba’asha ɗan Ahiya, domin ka tsokane ni har na yi fushi, ka kuma sa Isra’ila ya yi zunubi.’
and Y schal yyue thin hows as the hows of Jeroboam, sone of Naboth, and as the hows of Baasa, sone of Ahia; for thou didist to excite me to wrathfulnesse, and madist Israel to do synne.
23 “Game da Yezebel kuwa Ubangiji ya ce, ‘Karnuka za su cinye Yezebel a katangar Yezireyel.’
But also the Lord spak of Jezabel, and seide, Doggis schulen ete Jezabel in the feeld of Jesrael;
24 “Karnuka za su cinye waɗanda suke na Ahab waɗanda suka mutu a cikin birni, tsuntsayen sararin sama kuma za su cinye waɗanda suka mutu a jeji.”
if Achab schal die in the citee, doggis schulen ete hym; sotheli if he schal die in the feeld, briddis of the eyr schulen ete hym.
25 (Babu wani mutum kamar Ahab, wanda ya ba da kansa ga aikata mugunta a gaban Ubangiji. Yezebel matarsa ce ta zuga shi.
Therfor noon other was sich as Achab, that was seeld to do yuel in the siyt of the Lord; for Jezabel his wijf excitide hym;
26 Ya yi abar ƙyama ƙwarai ta wurin bin gumaka, kamar Amoriyawan da Ubangiji ya kora a gaban Isra’ila.)
and he was maad abhomynable, in so myche that he suede the ydols that Ammorreis maden, which Ammorreis the Lord wastide fro the face of the sones of Israel.
27 Sa’ad da Ahab ya ji waɗannan kalmomi, sai ya yage rigarsa, ya sa rigunan makoki, ya kuma yi azumi. Ya kwanta a kayan makoki, ya kuma yi tafiya cikin sauƙinkai.
Therfor whanne Achab hadde herd these wordis, he to-rente his cloth, and hilide his fleisch with an hayre, and he fastide, and slepte in a sak, and yede with the heed cast doun.
28 Sai maganar Ubangiji ta zo wa Iliya mutumin Tishbe, ta ce,
The word of the Lord was maad to Elie of Thesbi, and seide,
29 “Ka lura da yadda Ahab ya ƙasƙantar da kansa a gabana kuwa? Domin ya ƙasƙantar da kansa, ba zan kawo wannan masifa a kwanakinsa ba, amma zan kawo ta a kan gidansa a kwanakin ɗansa.”
Whethir thou hast not seyn Achab maad low bifor me? Therfor for he is maad low for the cause of me, Y schal not brynge yn yuel in hise daies, but in the daies of his sone Y schal bryng yn yuel to his hows.

< 1 Sarakuna 21 >