< 1 Sarakuna 21 >
1 Ana nan bayan haka sai waɗannan abubuwa suka faru. Nabot mutumin Yezireyel yana da gonar inabi a Yezireyel, a yankin Samariya, kusa da gidan Sarki Ahab.
And it came to pass after these events, that Naboth the Yizre'elite had a vineyard, which was in Yizre'el, near the palace of Achab the king of Samaria.
2 Sai Ahab ya ce wa Nabot, “Ka ba ni gonar inabinka in yi amfani da ita don kayan lambu, da yake tana kusa da fadana. Zan ba ka wata gonar inabin da ta fi wannan, ko kuma in ka gwammace, sai in biya ka duk abin da ya dace da ita.”
And Achab spoke unto Naboth, saying, Give me thy vineyard, that it may serve me for a herb-garden, because it is near unto my house; and I will give thee in its stead a vineyard better than it; [or, ] if it seem good in thy eyes, I will give thee the money, the value of the same.
3 Amma Nabot ya amsa wa Ahab ya ce, “Ubangiji yă sawwaƙe in ba ka gādon kakannina.”
And Naboth said to Achab, Far be it from me before the Lord, that I should give the inheritance of my fathers unto thee.
4 Ahab ya cika da fushi saboda Nabot, mutumin Yezireyel ya ce, “Ba zan ba ka gādon kakannina ba.” Ya kwanta a gadonsa yana zub da hawaye, ya kuma ƙi cin abinci.
And Achab came into his house low-spirited and displeased because of the word which Naboth the Yizre'elite had spoken to him, when he said, I will not give unto thee the inheritance of my fathers. And he laid himself down upon his bed, and turned away his face, and would eat no food.
5 Matarsa Yezebel ta shiga ciki ta tambaye shi, ta ce, “Me ya sa ka kumbura? Me ya sa ba za ka ci abinci ba?”
But Izebel his wife came to him, and spoke unto him, Why is thy spirit so sad! and why eatest thou no food?
6 Sai ya amsa mata, ya ce, “Domin na ce wa Nabot mutumin Yezireyel, ‘Ka sayar mini gonar inabinka; ko kuwa in ka gwammace, zan ba ka wata gonar inabi a maimakonta.’ Amma ya ce, ‘Ba zan ba ka gonar inabina ba.’”
And he said unto her, Because I spoke unto Naboth the Yizre'elite, and said unto him, Give me thy vineyard for money; or else, if it please thee, I will give thee a vineyard in its stead; but he hath said, I will not give unto thee my vineyard.
7 Yezebel matarsa ta ce, “Yaya kake yi kamar ba kai ne sarki Isra’ila ba? Tashi ka ci abinci! Ka yi farin ciki. Zan ba ka gonar inabin Nabot mutumin Yezireyel.”
Then said unto him Izebel his wife, Dost thou now govern the kingdom of Israel? arise, eat bread, and let thy heart be merry: I will myself give thee the vineyard of Naboth the Yizre'elite.
8 Sai ta rubuta wasiƙu a sunan Ahab, ta buga hatiminsa a kansu, sa’an nan ta aika su ga dattawa da manyan gari waɗanda suke zama a birnin da Nabot yake.
So she wrote letters in Achab's name, and sealed them with his seal; and she sent the letters unto the elders and unto the nobles who were in his city, and who dwelt near Naboth.
9 Cikin waɗannan wasiƙu ta rubuta, “Ku yi shelar ranar azumi, ku zaunar da Nabot a wuri mai martaba a cikin mutane.
And she wrote in the letters, saying, Proclaim a fast, and cause Naboth to sit at the head of the people;
10 Amma ku zaunar da waɗansu’yan iska biyu ɗaura da shi, ku sa su ba da shaida cewa ya zagi Allah da sarki. Sa’an nan ku ɗauke shi ku jajjefe shi da dutse sai ya mutu.”
And seat two men, worthless fellows, opposite to him, and let them bear witness against him, saying, Thou hast blasphemed God and the king; and then lead him forth, and stone him, that he may die.
11 Sai dattawa da manyan gari, waɗanda suke zama a birnin da Nabot yake, suka yi kamar yadda Yezebel ta umarta a cikin wasiƙun da ta rubuta.
And the men of his city, the elders and the nobles, those who dwelt in his city, did as Izebel had sent unto them, as was written in the letters which she had sent unto them.
12 Suka yi shelar azumi, suka kuma zaunar da Nabot a wuri mai martaba a cikin mutane.
They proclaimed a fast, and caused Naboth to sit at the head of the people.
13 Sa’an nan’yan iska biyu suka zo, suka zauna ɗaura da shi, suka kawo zarge a kan Nabot a gaban mutane, suna cewa, “Nabot ya zagi Allah da sarki.” Saboda haka aka ɗauke shi waje da birnin, aka jajjefe shi da dutse har ya mutu.
And there came in two men, worthless fellows, and seated themselves opposite to him; and these worthless men testified against him, against Naboth, in the presence of the people, saying, Naboth hath blasphemed God and the king. Then they led him forth out of the city, and stoned him with stones, that he died.
14 Sa’an nan suka aika wa Yezebel. “An jajjefe Nabot, ya kuma mutu.”
And they sent to Izebel, saying, Naboth hath been stoned, and is dead.
15 Nan da nan sa’ad da Yezebel ta ji cewa an jajjefe Nabot da dutse ya kuma mutu, sai ta ce wa Ahab, “Tashi ka mallaki gonar inabin Nabot mutumin Yezireyel wanda ya ƙi ya sayar maka. Ba shi da rai, ya mutu.”
And it came to pass, when Izebel heard that Naboth had been stoned, and was dead, that Izebel said to Achab, Arise, take possession of the vineyard of Naboth the Yizre'elite, which he refused to give thee for money; for Naboth is not alive, but dead.
16 Da Ahab ya ji cewa Nabot ya mutu, sai ya tashi ya gangara don yă mallaki gonar inabin Nabot.
And it came to pass, when Achab heard that Naboth was dead, that Achab rose up to go down to the vineyard of Naboth the Yizre'elite, to take possession of it.
17 Sai maganar Ubangiji ta zo wa Iliya mutumin Tishbe.
And the word of the Lord came to Elijah the Tishbite, saying,
18 Ta ce, “Gangara don ka sadu da Ahab sarkin Isra’ila, wanda yake mulki a Samariya. Yanzu yana a gonar inabin Nabot, inda ya tafi yă mallake ta.
Arise, go down to meet Achab the king of Israel, who is in Samaria; behold he is in the vineyard of Naboth, whither he is gone down to take possession of it.
19 Ka ce masa, Ga abin da Ubangiji ya ce, ‘Ba ka kashe mutum ka kuma ƙwace kayansa ba?’ Sa’an nan ka ce masa ga abin da Ubangiji ya ce, ‘A inda karnuka suka lashe jinin Nabot, karnuka za su lashe jininka, I, naka!’”
And thou shalt speak unto him, saying, Thus hath said the Lord, Hast thou murdered, and also taken possession? And thou shalt speak unto him, saying, Thus hath said the Lord, In the place where the dogs licked the blood of Naboth shall the dogs lick thy blood, yes, thine also.
20 Ahab ya ce wa Iliya, “Wato, ka same ni kuma, abokin gābana!” Sai ya amsa ya ce, “Na same ka, domin ka sayar da kanka ga yin mugunta a gaban Ubangiji.
And Achab said to Elijah, Hast thou found me, O my enemy? And he answered, I have found thee: because thou hast sold thyself to do what is evil in the eyes of the Lord.
21 ‘Zan kawo masifa a kanka. Zan kawar da zuriyarka, in kuma yanke daga Ahab kowane ɗa namiji na ƙarshe cikin Isra’ila, bawa ko’yantacce.
Behold, I will bring evil upon thee, and I will sweep out after thee, and will cut off from Achab every male, and the guarded and fortified in Israel,
22 Zan mai da gidanka kamar gida Yerobowam ɗan Nebat, da na Ba’asha ɗan Ahiya, domin ka tsokane ni har na yi fushi, ka kuma sa Isra’ila ya yi zunubi.’
And I will make thy house like the house of Jerobo'am the son of Nebat, and like the house of Ba'sha the son of Achiyah, for the provocation wherewith thou hast provoked [me] to anger, and induced Israel to sin.
23 “Game da Yezebel kuwa Ubangiji ya ce, ‘Karnuka za su cinye Yezebel a katangar Yezireyel.’
And also concerning Izebel hath the Lord spoken, saying, The dogs shall eat Izebel in the valley of Yizre'el.
24 “Karnuka za su cinye waɗanda suke na Ahab waɗanda suka mutu a cikin birni, tsuntsayen sararin sama kuma za su cinye waɗanda suka mutu a jeji.”
Him that dieth of Achab in the city shall the dogs eat; and him that dieth in the field shall the fowls of the heavens eat.
25 (Babu wani mutum kamar Ahab, wanda ya ba da kansa ga aikata mugunta a gaban Ubangiji. Yezebel matarsa ce ta zuga shi.
But indeed there was none like unto Achab, who sold himself to do what is evil in the eyes of the Lord, to which Izebel his wife incited him.
26 Ya yi abar ƙyama ƙwarai ta wurin bin gumaka, kamar Amoriyawan da Ubangiji ya kora a gaban Isra’ila.)
And he acted very abominably in following the idols, in all things just as had done the Emorites, whom the Lord had driven out from before the children of Israel.
27 Sa’ad da Ahab ya ji waɗannan kalmomi, sai ya yage rigarsa, ya sa rigunan makoki, ya kuma yi azumi. Ya kwanta a kayan makoki, ya kuma yi tafiya cikin sauƙinkai.
And it came to pass, when Achab heard these words, that he rent his clothes, and put sackcloth upon his flesh, and fasted, and slept in the sackcloth, and walked about barefooted.
28 Sai maganar Ubangiji ta zo wa Iliya mutumin Tishbe, ta ce,
And the word of the Lord came to Elijah the Tishbite, saying,
29 “Ka lura da yadda Ahab ya ƙasƙantar da kansa a gabana kuwa? Domin ya ƙasƙantar da kansa, ba zan kawo wannan masifa a kwanakinsa ba, amma zan kawo ta a kan gidansa a kwanakin ɗansa.”
Hast thou seen how Achab hath humbled himself before me? therefore, because he hath humbled himself before me, will I not bring the evil in his days: in the days of his son will I bring the evil upon his house.