< 1 Sarakuna 21 >

1 Ana nan bayan haka sai waɗannan abubuwa suka faru. Nabot mutumin Yezireyel yana da gonar inabi a Yezireyel, a yankin Samariya, kusa da gidan Sarki Ahab.
And it came to pass after these things, that Naboth the Jezreelite had a vineyard, which was in Jezreel, hard by the palace of Ahab, king of Samaria.
2 Sai Ahab ya ce wa Nabot, “Ka ba ni gonar inabinka in yi amfani da ita don kayan lambu, da yake tana kusa da fadana. Zan ba ka wata gonar inabin da ta fi wannan, ko kuma in ka gwammace, sai in biya ka duk abin da ya dace da ita.”
And Ahab spoke unto Naboth, saying: 'Give me thy vineyard, that I may have it for a garden of herbs, because it is near unto my house; and I will give thee for it a better vineyard than it; or, if it seem good to thee, I will give thee the worth of it in money.'
3 Amma Nabot ya amsa wa Ahab ya ce, “Ubangiji yă sawwaƙe in ba ka gādon kakannina.”
And Naboth said to Ahab: 'The LORD forbid it me, that I should give the inheritance of my fathers unto thee.'
4 Ahab ya cika da fushi saboda Nabot, mutumin Yezireyel ya ce, “Ba zan ba ka gādon kakannina ba.” Ya kwanta a gadonsa yana zub da hawaye, ya kuma ƙi cin abinci.
And Ahab came into his house sullen and displeased because of the word which Naboth the Jezreelite had spoken to him; for he had said: 'I will not give thee the inheritance of my fathers.' And he laid him down upon his bed, and turned away his face, and would eat no bread.
5 Matarsa Yezebel ta shiga ciki ta tambaye shi, ta ce, “Me ya sa ka kumbura? Me ya sa ba za ka ci abinci ba?”
But Jezebel his wife came to him, and said unto him: 'Why is thy spirit so sullen, that thou eatest no bread?'
6 Sai ya amsa mata, ya ce, “Domin na ce wa Nabot mutumin Yezireyel, ‘Ka sayar mini gonar inabinka; ko kuwa in ka gwammace, zan ba ka wata gonar inabi a maimakonta.’ Amma ya ce, ‘Ba zan ba ka gonar inabina ba.’”
And he said unto her: 'Because I spoke unto Naboth the Jezreelite, and said unto him: Give me thy vineyard for money; or else, if it please thee, I will give thee another vineyard for it; and he answered: I will not give thee my vineyard.'
7 Yezebel matarsa ta ce, “Yaya kake yi kamar ba kai ne sarki Isra’ila ba? Tashi ka ci abinci! Ka yi farin ciki. Zan ba ka gonar inabin Nabot mutumin Yezireyel.”
And Jezebel his wife said unto him: 'Dost thou now govern the kingdom of Israel? arise, and eat bread, and let thy heart be merry; I will give thee the vineyard of Naboth the Jezreelite.'
8 Sai ta rubuta wasiƙu a sunan Ahab, ta buga hatiminsa a kansu, sa’an nan ta aika su ga dattawa da manyan gari waɗanda suke zama a birnin da Nabot yake.
So she wrote letters in Ahab's name, and sealed them with his seal, and sent the letters unto the elders and to the nobles that were in his city, and that dwelt with Naboth.
9 Cikin waɗannan wasiƙu ta rubuta, “Ku yi shelar ranar azumi, ku zaunar da Nabot a wuri mai martaba a cikin mutane.
And she wrote in the letters, saying: 'Proclaim a fast, and set Naboth at the head of the people;
10 Amma ku zaunar da waɗansu’yan iska biyu ɗaura da shi, ku sa su ba da shaida cewa ya zagi Allah da sarki. Sa’an nan ku ɗauke shi ku jajjefe shi da dutse sai ya mutu.”
and set two men, base fellows, before him, and let them bear witness against him, saying: Thou didst curse God and the king. And then carry him out, and stone him, that he die.'
11 Sai dattawa da manyan gari, waɗanda suke zama a birnin da Nabot yake, suka yi kamar yadda Yezebel ta umarta a cikin wasiƙun da ta rubuta.
And the men of his city, even the elders and the nobles who dwelt in his city, did as Jezebel had sent unto them, according as it was written in the letters which she had sent unto them.
12 Suka yi shelar azumi, suka kuma zaunar da Nabot a wuri mai martaba a cikin mutane.
They proclaimed a fast, and set Naboth at the head of the people.
13 Sa’an nan’yan iska biyu suka zo, suka zauna ɗaura da shi, suka kawo zarge a kan Nabot a gaban mutane, suna cewa, “Nabot ya zagi Allah da sarki.” Saboda haka aka ɗauke shi waje da birnin, aka jajjefe shi da dutse har ya mutu.
And the two men, the base fellows, came in and sat before him; and the base fellows bore witness against him, even against Naboth, in the presence of the people, saying: 'Naboth did curse God and the king.' Then they carried him forth out of the city, and stoned him with stones, that he died.
14 Sa’an nan suka aika wa Yezebel. “An jajjefe Nabot, ya kuma mutu.”
Then they sent to Jezebel, saying: 'Naboth is stoned, and is dead.'
15 Nan da nan sa’ad da Yezebel ta ji cewa an jajjefe Nabot da dutse ya kuma mutu, sai ta ce wa Ahab, “Tashi ka mallaki gonar inabin Nabot mutumin Yezireyel wanda ya ƙi ya sayar maka. Ba shi da rai, ya mutu.”
And it came to pass, when Jezebel heard that Naboth was stoned, and was dead, that Jezebel said to Ahab: 'Arise, take possession of the vineyard of Naboth the Jezreelite, which he refused to give thee for money; for Naboth is not alive, but dead.'
16 Da Ahab ya ji cewa Nabot ya mutu, sai ya tashi ya gangara don yă mallaki gonar inabin Nabot.
And it came to pass, when Ahab heard that Naboth was dead, that Ahab rose up to go down to the vineyard of Naboth the Jezreelite, to take possession of it.
17 Sai maganar Ubangiji ta zo wa Iliya mutumin Tishbe.
And the word of the LORD came to Elijah the Tishbite, saying:
18 Ta ce, “Gangara don ka sadu da Ahab sarkin Isra’ila, wanda yake mulki a Samariya. Yanzu yana a gonar inabin Nabot, inda ya tafi yă mallake ta.
'Arise, go down to meet Ahab king of Israel, who dwelleth in Samaria; behold, he is in the vineyard of Naboth, whither he is gone down to take possession of it.
19 Ka ce masa, Ga abin da Ubangiji ya ce, ‘Ba ka kashe mutum ka kuma ƙwace kayansa ba?’ Sa’an nan ka ce masa ga abin da Ubangiji ya ce, ‘A inda karnuka suka lashe jinin Nabot, karnuka za su lashe jininka, I, naka!’”
And thou shalt speak unto him, saying: Thus saith the LORD: Hast thou killed, and also taken possessions? and thou shalt speak unto him, saying: Thus saith the LORD: In the place where dogs licked the blood of Naboth shall dogs lick thy blood, even thine.'
20 Ahab ya ce wa Iliya, “Wato, ka same ni kuma, abokin gābana!” Sai ya amsa ya ce, “Na same ka, domin ka sayar da kanka ga yin mugunta a gaban Ubangiji.
And Ahab said to Elijah: 'Hast thou found me, O mine enemy?' And he answered: 'I have found thee; because thou hast given thyself over to do that which is evil in the sight of the LORD.
21 ‘Zan kawo masifa a kanka. Zan kawar da zuriyarka, in kuma yanke daga Ahab kowane ɗa namiji na ƙarshe cikin Isra’ila, bawa ko’yantacce.
Behold, I will bring evil upon thee, and will utterly sweep thee away, and will cut off from Ahab every man-child, and him that is shut up and him that is left at large in Israel.
22 Zan mai da gidanka kamar gida Yerobowam ɗan Nebat, da na Ba’asha ɗan Ahiya, domin ka tsokane ni har na yi fushi, ka kuma sa Isra’ila ya yi zunubi.’
And I will make thy house like the house of Jeroboam the son of Nebat, and like the house of Baasa the son of Ahijah, for the provocation wherewith thou hast provoked Me, and hast made Israel to sin.
23 “Game da Yezebel kuwa Ubangiji ya ce, ‘Karnuka za su cinye Yezebel a katangar Yezireyel.’
And of Jezebel also spoke the LORD, saying: The dogs shall eat Jezebel in the moat of Jezreel.
24 “Karnuka za su cinye waɗanda suke na Ahab waɗanda suka mutu a cikin birni, tsuntsayen sararin sama kuma za su cinye waɗanda suka mutu a jeji.”
Him that dieth of Ahab in the city the dogs shall eat; and him that dieth in the field shall the fowls of the air eat.'
25 (Babu wani mutum kamar Ahab, wanda ya ba da kansa ga aikata mugunta a gaban Ubangiji. Yezebel matarsa ce ta zuga shi.
But there was none like unto Ahab, who did give himself over to do that which was evil in the sight of the LORD, whom Jezebel his wife stirred up.
26 Ya yi abar ƙyama ƙwarai ta wurin bin gumaka, kamar Amoriyawan da Ubangiji ya kora a gaban Isra’ila.)
And he did very abominably in following idols, according to all that the Amorites did, whom the LORD cast out before the children of Israel.
27 Sa’ad da Ahab ya ji waɗannan kalmomi, sai ya yage rigarsa, ya sa rigunan makoki, ya kuma yi azumi. Ya kwanta a kayan makoki, ya kuma yi tafiya cikin sauƙinkai.
And it came to pass, when Ahab heard those words, that he rent his clothes, and put sackcloth upon his flesh, and fasted, and lay in sackcloth, and went softy.
28 Sai maganar Ubangiji ta zo wa Iliya mutumin Tishbe, ta ce,
And the word of the LORD came to Elijah the Tishbite, saying:
29 “Ka lura da yadda Ahab ya ƙasƙantar da kansa a gabana kuwa? Domin ya ƙasƙantar da kansa, ba zan kawo wannan masifa a kwanakinsa ba, amma zan kawo ta a kan gidansa a kwanakin ɗansa.”
'Seest thou how Ahab humbleth himself before Me? because he humbleth himself before Me, I will not bring the evil in his days; but in his son's days will I bring the evil upon his house.'

< 1 Sarakuna 21 >