< 1 Sarakuna 20 >

1 Ben-Hadad sarkin Aram kuwa ya tattara mayaƙansa gaba ɗaya. Sarakuna talatin da biyu suka tafi tare da shi haɗe da dawakansu da kekunan yaƙinsu. Ya haura ya yi wa Samariya kwanto, ya kuma yaƙe ta.
Och Benhadad, Konungen i Syrien, församlade alla sina magt, och voro två och tretio Konungar med honom, och hästar och vagnar; och drog upp, och belade Samarien, och stridde deremot;
2 Ya aika da’yan aika zuwa cikin birnin wurin Ahab sarkin Isra’ila yana cewa, “Ga abin da Ben-Hadad ya ce,
Och sände båd till Achab, Israels Konung, in uti staden;
3 ‘Azurfarka da zinariyarka nawa ne. Mafi kyau cikin matanka da’ya’yanka nawa ne.’”
Och lät säga honom: Så säger Benhadad: Ditt silfver och ditt guld är mitt; och dina hustrur, och din bästa barn äro också min.
4 Sarkin Isra’ila ya amsa, ya ce, “Kamar dai yadda ka faɗa, ranka yă daɗe, sarki. Ni da dukan abin da nake da shi, naka ne.”
Israels Konung svarade, och sade: Min herre Konung, såsom du sagt hafver, jag är din, och allt det jag hafver.
5 Sai’yan aikan suka sāke dawo suka ce, “Ga abin da Ben-Hadad ya ce, ‘Na aika ka ba da azurfarka da zinariyarka, matanka da kuma’ya’yanka.
Och båden kommo igen, och sade: Så säger Benhadad: Efter jag hafver sändt till dig, och låtit säga: Ditt silfver och ditt guld, dina hustrur och din barn skall du få mig;
6 Amma war haka gobe zan aika shugabannina su bincika fadanka da kuma gidajen shugabanninka. Za su kwashe dukan abubuwan da kake ganin darajarsu su tafi.’”
Så vill jag i morgon på denna tiden sända mina tjenare till dig, att de ransaka ditt hus, och dina underdånares hus; och hvad dig kärt är, skola de taga i deras händer, och bära bort.
7 Sarkin Isra’ila ya tattara dukan dattawan ƙasar, ya ce musu, “Ku duba fa, wannan mutum yana neman tsokana! Sa’ad da ya aika in ba shi matana da’ya’yana, azurfana da zinariyana, ban hana masa ba.”
Då kallade Israels Konung alla landsens äldsta, och sade: Märker och ser, hvilket ondt han företager; han sände till mig om mina hustrur och barn, silfver och guld, och jag hafver det intet nekat honom.
8 Dattawa da dukan mutane suka amsa, suka ce, “Kada ka saurare shi ko ka yarda da abin da yake bukata.”
Då sade till honom alle de gamle, och allt folket: Du skall intet höra honom, eller samtyckat.
9 Saboda haka ya ba wa’yan aikan Ben-Hadad amsa, ya ce, “Ku faɗa wa ranka yă daɗe, sarki, ‘Bawanka zai yi dukan abin da ka bukaci da farko, amma wannan na ƙarshe ba zan iya yin ba.’” Suka tafi suka kai amsar wa Ben-Hadad.
Och han sade till Benhadads båd: Säger minom herra Konungenom: Allt det du böd dinom tjenare i förstone, vill jag göra; men detta kan jag icke göra. Och båden gingo sina färde, och sade sådant igen.
10 Sai Ben-Hadad ya aika da wani saƙo wa Ahab, ya ce, “Bari alloli su yi da ni yadda suke so, su kuma yi haka da tsanani, in isashen ƙura ta rage a Samariya da za a iya ba wa mutanena a tafin hannu.”
Då sände Benhadad till honom, och lät säga honom: Gudarna göre mig det och det, om stoftet i Samarien skall räcka till att allt folket under mig må taga der en hand full af.
11 Sarki Isra’ila ya amsa, ya ce, “Ku faɗa masa, ‘Wanda ya sa kayan yaƙinsa bai kamata yă yi fariya ba sai ya tuɓe su.’”
Men Konungen i Israel svarade och sade: Säger: Den som lägger harnesket uppå, skall icke så berömma sig, såsom den det aflagt hafver.
12 Ben-Hadad ya ji wannan saƙo yayinda shi da sarakunan suke sha a cikin tentunansu, sai ya umarce mutanensa, ya ce, “Ku shirya don yaƙi.” Saboda haka suka shirya don su yaƙi birnin.
Då Benhadad det hörde, och drack med Konungarna i tjällen, sade han till sina tjenare: Gör er redo; och de gjorde redo emot staden.
13 Ana cikin haka sai wani annabi ya zo wurin Ahab sarkin Isra’ila ya sanar masa cewa, “Ga abin da Ubangiji ya ce, ‘Ka ga wannan ɗumbun mayaƙa? Zan ba da su cikin hannunka a yau, sa’an nan za ka san cewa ni ne Ubangiji.’”
Och si, en Prophet gick fram till Achab, Israels Konung, och sade: Så säger Herren: Du hafver ju sett allan den stora hopen; si, jag vill i dag gifva honom i dina hand, att du veta skall att jag är Herren.
14 Ahab ya ce, “Amma wa zai yi haka?” Annabin ya amsa, “Ga abin da Ubangiji ya ce, ‘Sojoji matasa na shugabannin yankuna za su yi haka.’” Ya tambaya, “Wa kuma zai fara yaƙin?” Annabin ya amsa, “Kai za ka fara.”
Achab sade: Genom hvem? Han sade: Så säger Herren: Genom landsfogdarnas tjenare. Han sade: Ho skall begynna striden? Han sade: Du.
15 Saboda haka Ahab ya kira sojoji matasa na shugabannin yankuna, mutum 232. Sa’an nan ya tattara sauran Isra’ilawa su 7,000 gaba ɗaya.
Då räknade han landsfogdarnas tjenare, och de voro tuhundrad och två och tretio; och räknade efter dem hela folket af all Israels barn, sjutusend män;
16 Suka fita da tsakar rana yayinda Ben-Hadad tare da sarakuna 32 masu goyon bayansa suke cikin tentunansu suna sha, suna buguwa.
Och drogo ut om middag. Men Benhadad drack, och var drucken i tjällen, med de två och tretio Konungar, som honom till hjelp komne voro.
17 Sojojin nan matasa na shugabannin yankuna suka fara fita. Ben-Hadad kuwa ya riga ya aiki’yan leƙen asiri, waɗanda suka ce, “Mutane suna zuwa daga Samariya.”
Och landsfogdarnas tjenare drogo först ut. Då sände Benhadad ut; och de bådade honom, och sade: Det draga män utu Samarien.
18 Ya ce, “In sun fito don salama, ku kamo su da rai; in sun fito yaƙi ne, ku kamo su da rai.”
Han sade: Griper dem lefvande, ehvad de äro utdragne till frid eller strid.
19 Sojojin nan matasa na shugabannin yankuna suka taka suka fita daga birnin da mayaƙa a bayansu.
Då landsfogdarnas tjenare voro utdragne, och hären efter dem,
20 Kowannensu kuwa ya buge abokin gābansa. Ganin wannan, sai Arameyawa suka gudu, Isra’ilawa suna bi. Amma Ben-Hadad na Aram ya tsere a kan dokinsa tare da waɗansu mahayan dawakansa.
Slog hvar och en den han öfverkom. Och de Syrer flydde, och Israel jagade efter dem; och Benhadad, Konungen i Syrien, undslapp med hästar och resenärar.
21 Sarki Isra’ila ya bi, ya kuma sha ƙarfin dawakan da keken yaƙin, ya kashe Arameyawa da yawa.
Och Israels Konung drog ut, och slog hästar och vagnar, så att han gjorde en stor slagtning på de Syrer.
22 Daga baya, annabin ya zo wurin sarkin Isra’ila ya ce, “Ka ƙarfafa matsayinka ka kuma ga abin da za a yi, gama a bazara mai zuwa sarkin Aram zai sāke kawo yaƙi.”
Då gick en Prophet till Israels Konung, och sade till honom: Gack bort, och förstärk dig, och märk och se hvad du göra skall; ty Konungen i Syrien varder igenkommandes emot dig, när året är ute.
23 Ana cikin haka, shugabannin sarkin Aram suka ba shi shawara, “Allolinsu, allolin tuddai ne. Shi ya sa suka fi mu ƙarfi. Amma in mun yaƙe su a fili, tabbatacce za mu fi su ƙarfi.
Förty Konungens tjenare i Syrien sade till honom: Deras gudar äro bergsgudar, derföre hafva de vunnit oss. O! att vi måtte strida med dem på slättene; hvad gäller, vi skulle vinna dem?
24 Ka yi wannan. Ka cire dukan sarakuna daga matsayinsu ka sa waɗansu shugabanni a maimakonsu.
Gör alltså: Tag bort Konungarna, hvar af sitt rum, och sätt öfverstar i deras stad;
25 Dole kuma ka tā da waɗansu mayaƙa kamar waɗanda ka rasa, doki don doki, keken yaƙi kuma don keken yaƙi, saboda mu iya yaƙe Isra’ila a fili. Ta haka tabbatacce za mu fi ƙarfinsu.” Sai ya yarda da su, ya kuma yi haka.
Och skicka dig en här, sådana som hären var, som du mist hafver, och hästar och vagnar, såsom hine voro, och låt oss strida emot dem på slättene; hvad gäller, vi öfvervinne dem? Han hörde deras röst, och gjorde så.
26 Bazara na biye Ben-Hadad ya tattara Arameyawa, ya haura zuwa Afek don yă yaƙi Isra’ila.
Som nu året omgånget var, skickade Benhadad de Syrer, och drog upp till Aphek, till att strida emot Israel.
27 Sa’ad da aka tattara Isra’ilawa, aka kuma ba su guzuri, sai suka taka suka fita don su sadu da Arameyawa. Isra’ilawa suka kafa sansani ɗaura da su kamar ƙananan garkuna biyu na awaki, yayinda Arameyawa suka rufe dukan jejin.
Och Israels barn skickade sig ock, och bespisade sig, och drogo dit emot dem, och lägrade sig emot dem, såsom två små getahjordar; men landet var fullt med Syrer.
28 Sai mutumin Allah ya zo ya ce wa sarkin Isra’ila, “Ga abin da Ubangiji ya ce, ‘Domin Arameyawa suna tsammani Ubangiji allahn tuddai ne, ba allahn kwari ba, zan ba da wannan ɗumbun mayaƙa a hannuwanka, za ka kuwa sani ni ne Ubangiji.’”
Och en Guds man gick fram, och sade till Israels Konung: Så säger Herren: Derföre, att de Syrer hafva sagt: Herren är en Gud på bergom, och icke en Gud i dalar; så hafver jag gifvit allan denna stora hopen uti dina hand, att I skolen veta att jag är Herren.
29 Kwana bakwai suka yi sansani ɗaura da juna, a rana ta bakwai sai yaƙi ya haɗu. Isra’ilawa suka kashe sojojin kafa na Arameyawa dubu ɗari a rana ɗaya.
Och de lägrade sig tvärtemot hina i sju dagar; på sjunde dagen drogo de tillhopa i strid. Och Israels barn slogo de Syrer hundradetusend fotfolk af, på en dag.
30 Sauransu suka tsere zuwa birnin Afek, inda katangar ya fāɗa a kan mutum dubu ashirin da bakwai. Sai Ben-Hadad ya gudu zuwa birni ya ɓuya a ciki cikin ɗaki.
Och de som öfverblefvo, flydde till Aphek in i staden. Och murarna föllo uppå de sju och tjugu tusend män, som qvare blefvo. Och Benhadad flydde också in i staden, uti en liten kammar.
31 Fadawansa suka je suka ce masa, “Mun ji an ce sarakunan Isra’ila masu jinƙai ne, bari mu sa tufafin makoki, mu ɗaura igiyoyi a wuyanmu, sa’an nan mu tafi wurin sarkin Isra’ila, wataƙila zai bar ka da rai.”
Då sade hans tjenare till honom: Si, nu hafve vi hört, att Israels hus Konungar äro barmhertige Konungar; så låt oss taga säcker kringom våra länder, och rep kringom vår hufvud, och gå ut till Israels Konung; tilläfventyrs han låter dina själ lefva.
32 Saye da tufafin makoki kewaye a gindinsu, da kuma igiyoyi kewaye da kawunansu, suka tafi wurin sarkin Isra’ila, suka ce, “Bawanka Ben-Hadad ya ce, ‘Ina roƙonka bari in rayu.’” Sarki ya amsa, “Har yanzu yana da rai? Shi ɗan’uwana ne.”
Och de bundo säcker öfver sina länder, och rep om sin hufvud, och kommo till Israels Konung, och sade: Benhadad din tjenare låter dig säga: Käre, låt mina själ lefva. Han sade: Lefver han ännu, så är han min broder.
33 Da ma abin da fadawan suke so su ji ke nan, sai suka yi sauri, suka karɓi maganar a bakinsa, suka ce, “I, ɗan’uwanka, Ben-hadad!” Sarki ya ce, “Ku je ku kawo shi.” Da Ben-Hadad ya fita, sai Ahab ya sa aka kawo shi cikin keken yaƙinsa.
Och männerna togo med hast ordet af honom, och tydde det ut för sig, och sade: Ja, din broder Benhadad. Han sade: Kommer, och hafver honom hit. Då gick Benhadad ut till honom, och han lät honom sitta på sinom vagn.
34 Ben-Hadad ya ce, “Zan mayar da biranen mahaifinka da na ƙwace daga mahaifinka. Za ka iya sa wurin kasuwarka a cikin Damaskus, kamar yadda mahaifinka ya yi a Samariya.” Ahab ya ce, “Bisa wannan yarjejjeniya zan sake ka.” Saboda haka ya yi yarjejjeniya da shi, sai ya bar shi ya tafi.
Och han sade till honom: De städer, som min fader dinom fader aftagit hafver, vill jag få dig igen; och gör dig gator i Damascon, såsom min fader gjort hafver i Samarien; så vill jag fara ifrå dig med ett förbund. Och han gjorde ett förbund med honom, och lät honom fara.
35 Ta wurin maganar Ubangiji, ɗaya daga cikin’ya’ya maza na annabawa ya ce wa abokinsa, “Ka buge ni da makaminka,” amma mutumin ya ƙi.
Då sade en man utaf de Propheters söner till sin nästa, igenom Herrans ord: Käre, slå mig; men han nekade sig vilja slå honom.
36 Sai annabin ya ce, “Domin ba ka yi biyayya da Ubangiji ba, da zarar ka bar ni zaki zai kashe ka.” Daga baya mutumin ya tafi, zaki ya same shi, ya kuma kashe shi.
Då sade han till honom: Derföre, att du icke hafver hört Herrans röst, si, så skall ett lejon slå dig, när du går ifrå mig. Och då han gick ifrå honom, fann honom ett lejon, och slog honom.
37 Annabin ya sami wani mutum ya ce, “Ka buge ni, ina roƙonka.” Sai mutumin ya buge shi, ya ji masa ciwo.
Och han fann en annan man, och sade: Käre, slå mig. Och mannen slog honom, och gjorde honom sår.
38 Sa’an nan annabin ya tafi ya tsaya a bakin hanya yana jiran sarki. Ya ɓad da kamanni da ƙyalle a kansa. Ƙyallen ya sauka zuwa bisa idanunsa.
Då gick den Propheten bort, och trädde fram för Konungen på vägenom, och förvandlade sitt ansigte med asko.
39 Yayinda sarki yake wucewa, sai annabin ya yi kira da ƙarfi gare shi ya ce “Ni bawanka na tafi yaƙi, sai ga wani ya kawo mini wani mutum, ya ce, ‘Ka riƙe wannan mutum, kada ka bar shi yă kuɓuta ko da ƙaƙa, idan ka bari ya kuɓuta, a bakin ranka, ko kuwa ka biya talanti ɗaya na azurfa.’
Och när Konungen for der framom, ropade han till Konungen, och sade: Din tjenare var utdragen midt i striden; och si, en man var afviken, och hade en man till mig, och sade: Förvara denna mannen; om han kommer bort, så skall din själ vara i hans själs stad, eller du skall gifva en centener silfver.
40 Yayinda bawanka yana fama, yana kai da kawowa, sai mutumin ya ɓace.” Sai sarkin Isra’ila ya ce, “Hukuncinka ke nan, ka furta shi da kanka.”
Och då din tjenare der och der beställa hade, kom han sin väg. Konungen sade till honom: Det är din dom, som du sjelfver afsagt hafver.
41 Sai annabin ya cire ƙyallen da sauri daga kansa, da ya rufe idanunsa, sarkin Isra’ila kuwa ya gane shi a matsayi ɗaya daga cikin annabawa.
Så strök han med hast askona af ansigtet; och Israels Konung kände honom, att han var en af Propheterna.
42 Sai ya ce wa sarki, “Ga abin da Ubangiji ya ce, ‘Ka saki mutumin da na ƙudura yă mutu. Saboda haka ranka zai zama a maimakon ransa, mutanenka a maimakon mutanensa.’”
Och han sade till honom: Så säger Herren: Derföre, att du hafver släppt den man utu dina händer, som tillspillogifven var, skall din själ vara för hans själ, och ditt folk för hans folk.
43 Cike da fushi, sarkin Isra’ila ya tafi fadarsa a Samariya.
Men Israels Konung for sina färde, illa tillfrids och vred, i sitt hus, och kom till Samarien.

< 1 Sarakuna 20 >