< 1 Sarakuna 20 >

1 Ben-Hadad sarkin Aram kuwa ya tattara mayaƙansa gaba ɗaya. Sarakuna talatin da biyu suka tafi tare da shi haɗe da dawakansu da kekunan yaƙinsu. Ya haura ya yi wa Samariya kwanto, ya kuma yaƙe ta.
And Ben-Hadad king of Aram has gathered all his force, and thirty-two kings [are] with him, and horse and chariot, and he goes up and lays siege against Samaria, and fights with it,
2 Ya aika da’yan aika zuwa cikin birnin wurin Ahab sarkin Isra’ila yana cewa, “Ga abin da Ben-Hadad ya ce,
and sends messengers to Ahab king of Israel, to the city,
3 ‘Azurfarka da zinariyarka nawa ne. Mafi kyau cikin matanka da’ya’yanka nawa ne.’”
and says to him, “Thus said Ben-Hadad: Your silver and your gold are mine, and your wives and your sons—the best—are mine.”
4 Sarkin Isra’ila ya amsa, ya ce, “Kamar dai yadda ka faɗa, ranka yă daɗe, sarki. Ni da dukan abin da nake da shi, naka ne.”
And the king of Israel answers and says, “According to your word, my lord, O king: I [am] yours, and all that I have.”
5 Sai’yan aikan suka sāke dawo suka ce, “Ga abin da Ben-Hadad ya ce, ‘Na aika ka ba da azurfarka da zinariyarka, matanka da kuma’ya’yanka.
And the messengers turn back and say, “Thus spoke Ben-Hadad, saying, Surely I sent to you, saying, Your silver, and your gold, and your wives, and your sons, you give to me;
6 Amma war haka gobe zan aika shugabannina su bincika fadanka da kuma gidajen shugabanninka. Za su kwashe dukan abubuwan da kake ganin darajarsu su tafi.’”
for if, at this time tomorrow, I send my servants to you, then they have searched your house, and the houses of your servants, and it has been [that] every desirable thing of your eyes they place in their hand, and have taken [them] away.”
7 Sarkin Isra’ila ya tattara dukan dattawan ƙasar, ya ce musu, “Ku duba fa, wannan mutum yana neman tsokana! Sa’ad da ya aika in ba shi matana da’ya’yana, azurfana da zinariyana, ban hana masa ba.”
And the king of Israel calls to all [the] elderly of the land and says, “Please know and see that this [one] is seeking evil, for he sent to me for my wives, and for my sons, and for my silver, and for my gold, and I did not withhold from him.”
8 Dattawa da dukan mutane suka amsa, suka ce, “Kada ka saurare shi ko ka yarda da abin da yake bukata.”
And all the elderly and all the people say to him, “Do not listen, nor consent.”
9 Saboda haka ya ba wa’yan aikan Ben-Hadad amsa, ya ce, “Ku faɗa wa ranka yă daɗe, sarki, ‘Bawanka zai yi dukan abin da ka bukaci da farko, amma wannan na ƙarshe ba zan iya yin ba.’” Suka tafi suka kai amsar wa Ben-Hadad.
And he says to the messengers of Ben-Hadad, “Say to my lord the king, All that you sent to your servant for at the first I do, and this thing I am not able to do”; and the messengers go and take him back word.
10 Sai Ben-Hadad ya aika da wani saƙo wa Ahab, ya ce, “Bari alloli su yi da ni yadda suke so, su kuma yi haka da tsanani, in isashen ƙura ta rage a Samariya da za a iya ba wa mutanena a tafin hannu.”
And Ben-Hadad sends to him and says, “Thus the gods do to me, and thus do they add, if the dust of Samaria suffice for handfuls for all the people who [are] at my feet.”
11 Sarki Isra’ila ya amsa, ya ce, “Ku faɗa masa, ‘Wanda ya sa kayan yaƙinsa bai kamata yă yi fariya ba sai ya tuɓe su.’”
And the king of Israel answers and says, “Speak: Do not let him who is girding on boast himself as him who is loosing [his armor].”
12 Ben-Hadad ya ji wannan saƙo yayinda shi da sarakunan suke sha a cikin tentunansu, sai ya umarce mutanensa, ya ce, “Ku shirya don yaƙi.” Saboda haka suka shirya don su yaƙi birnin.
And it comes to pass at the hearing of this word—and he is drinking, he and the kings, in the shelters—that he says to his servants, “Set yourselves”; and they set themselves against the city.
13 Ana cikin haka sai wani annabi ya zo wurin Ahab sarkin Isra’ila ya sanar masa cewa, “Ga abin da Ubangiji ya ce, ‘Ka ga wannan ɗumbun mayaƙa? Zan ba da su cikin hannunka a yau, sa’an nan za ka san cewa ni ne Ubangiji.’”
And behold, a certain prophet has come near to Ahab king of Israel and says, “Thus said YHWH: Have you seen all this great multitude? Behold, I am giving it into your hand today, and you have known that I [am] YHWH.”
14 Ahab ya ce, “Amma wa zai yi haka?” Annabin ya amsa, “Ga abin da Ubangiji ya ce, ‘Sojoji matasa na shugabannin yankuna za su yi haka.’” Ya tambaya, “Wa kuma zai fara yaƙin?” Annabin ya amsa, “Kai za ka fara.”
And Ahab says, “By whom?” And he says, “Thus said YHWH: By the young men of the heads of the provinces”; and he says, “Who directs the battle?” And he says, “You.”
15 Saboda haka Ahab ya kira sojoji matasa na shugabannin yankuna, mutum 232. Sa’an nan ya tattara sauran Isra’ilawa su 7,000 gaba ɗaya.
And he inspects the young men of the heads of the provinces, and they are two hundred and thirty-two, and after them he has mustered all the people, all the sons of Israel—seven thousand,
16 Suka fita da tsakar rana yayinda Ben-Hadad tare da sarakuna 32 masu goyon bayansa suke cikin tentunansu suna sha, suna buguwa.
and they go out at noon, and Ben-Hadad is drinking—drunk in the shelters, he and the kings, the thirty-two kings helping him.
17 Sojojin nan matasa na shugabannin yankuna suka fara fita. Ben-Hadad kuwa ya riga ya aiki’yan leƙen asiri, waɗanda suka ce, “Mutane suna zuwa daga Samariya.”
And the young men of the heads of the provinces go out at the first, and Ben-Hadad sends, and they declare to him, saying, “Men have come out of Samaria.”
18 Ya ce, “In sun fito don salama, ku kamo su da rai; in sun fito yaƙi ne, ku kamo su da rai.”
And he says, “If they have come out for peace, catch them alive; and if they have come out for battle, catch them alive.”
19 Sojojin nan matasa na shugabannin yankuna suka taka suka fita daga birnin da mayaƙa a bayansu.
And these have gone out of the city—the young men of the heads of the provinces—and the force that [is] after them,
20 Kowannensu kuwa ya buge abokin gābansa. Ganin wannan, sai Arameyawa suka gudu, Isra’ilawa suna bi. Amma Ben-Hadad na Aram ya tsere a kan dokinsa tare da waɗansu mahayan dawakansa.
and each strikes his man, and Aram flees, and Israel pursues them, and Ben-Hadad king of Aram escapes on a horse—and the horsemen;
21 Sarki Isra’ila ya bi, ya kuma sha ƙarfin dawakan da keken yaƙin, ya kashe Arameyawa da yawa.
and the king of Israel goes out, and strikes the horses, and the charioteers, and has struck among the Arameans a great striking.
22 Daga baya, annabin ya zo wurin sarkin Isra’ila ya ce, “Ka ƙarfafa matsayinka ka kuma ga abin da za a yi, gama a bazara mai zuwa sarkin Aram zai sāke kawo yaƙi.”
And the prophet comes near to the king of Israel and says to him, “Go, strengthen yourself, and know and see that which you do, for at the turn of the year the king of Aram is coming up against you.”
23 Ana cikin haka, shugabannin sarkin Aram suka ba shi shawara, “Allolinsu, allolin tuddai ne. Shi ya sa suka fi mu ƙarfi. Amma in mun yaƙe su a fili, tabbatacce za mu fi su ƙarfi.
And the servants of the king of Aram said to him, “Their gods [are] gods of hills, therefore they were stronger than us; and yet, we fight with them in the plain—are we not stronger than they?
24 Ka yi wannan. Ka cire dukan sarakuna daga matsayinsu ka sa waɗansu shugabanni a maimakonsu.
And this thing you do: turn aside each of the kings out of his place, and set captains in their stead;
25 Dole kuma ka tā da waɗansu mayaƙa kamar waɗanda ka rasa, doki don doki, keken yaƙi kuma don keken yaƙi, saboda mu iya yaƙe Isra’ila a fili. Ta haka tabbatacce za mu fi ƙarfinsu.” Sai ya yarda da su, ya kuma yi haka.
and you, number for yourself a force as the force that is fallen from you, and horse for horse, and chariot for chariot, and we fight with them in the plain; are we not stronger than they?” And he listens to their voice, and does so.
26 Bazara na biye Ben-Hadad ya tattara Arameyawa, ya haura zuwa Afek don yă yaƙi Isra’ila.
And it comes to pass at the turn of the year, that Ben-Hadad inspects the Arameans, and goes up to Aphek, to battle with Israel,
27 Sa’ad da aka tattara Isra’ilawa, aka kuma ba su guzuri, sai suka taka suka fita don su sadu da Arameyawa. Isra’ilawa suka kafa sansani ɗaura da su kamar ƙananan garkuna biyu na awaki, yayinda Arameyawa suka rufe dukan jejin.
and the sons of Israel have been inspected, and supported, and go to meet them, and the sons of Israel encamp before them, like two flocks of goats, and the Arameans have filled the land.
28 Sai mutumin Allah ya zo ya ce wa sarkin Isra’ila, “Ga abin da Ubangiji ya ce, ‘Domin Arameyawa suna tsammani Ubangiji allahn tuddai ne, ba allahn kwari ba, zan ba da wannan ɗumbun mayaƙa a hannuwanka, za ka kuwa sani ni ne Ubangiji.’”
And a man of God comes near, and speaks to the king of Israel and says, “Thus said YHWH: Because that the Arameans have said, YHWH [is] God of [the] hills, but He [is] not God of [the] valleys—I have given the whole of this great multitude into your hand, and you have known that I [am] YHWH.”
29 Kwana bakwai suka yi sansani ɗaura da juna, a rana ta bakwai sai yaƙi ya haɗu. Isra’ilawa suka kashe sojojin kafa na Arameyawa dubu ɗari a rana ɗaya.
And they encamp opposite one another [for] seven days, and it comes to pass on the seventh day, that the battle draws near, and the sons of Israel strike one hundred thousand footmen of Aram in one day.
30 Sauransu suka tsere zuwa birnin Afek, inda katangar ya fāɗa a kan mutum dubu ashirin da bakwai. Sai Ben-Hadad ya gudu zuwa birni ya ɓuya a ciki cikin ɗaki.
And those left flee to Aphek, into the city, and the wall falls on twenty-seven chief men who are left, and Ben-Hadad has fled, and comes into the city, into the innermost part.
31 Fadawansa suka je suka ce masa, “Mun ji an ce sarakunan Isra’ila masu jinƙai ne, bari mu sa tufafin makoki, mu ɗaura igiyoyi a wuyanmu, sa’an nan mu tafi wurin sarkin Isra’ila, wataƙila zai bar ka da rai.”
And his servants say to him, “Now behold, we have heard that the kings of the house of Israel—that they are kind kings; please let us put sackcloth on our loins and ropes on our heads, and we go out to the king of Israel; it may be he keeps you alive.”
32 Saye da tufafin makoki kewaye a gindinsu, da kuma igiyoyi kewaye da kawunansu, suka tafi wurin sarkin Isra’ila, suka ce, “Bawanka Ben-Hadad ya ce, ‘Ina roƙonka bari in rayu.’” Sarki ya amsa, “Har yanzu yana da rai? Shi ɗan’uwana ne.”
And they gird sackcloth on their loins, and ropes [are] on their heads, and they come to the king of Israel, and say, “Your servant Ben-Hadad has said, Please let me live”; and he says, “Is he still alive? He [is] my brother.”
33 Da ma abin da fadawan suke so su ji ke nan, sai suka yi sauri, suka karɓi maganar a bakinsa, suka ce, “I, ɗan’uwanka, Ben-hadad!” Sarki ya ce, “Ku je ku kawo shi.” Da Ben-Hadad ya fita, sai Ahab ya sa aka kawo shi cikin keken yaƙinsa.
And the men observe diligently, and hurry, and catch [the word] from him, and say, “Your brother Ben-Hadad”; and he says, “Go in, bring him”; and Ben-Hadad comes out to him, and he causes him to come up on the chariot.
34 Ben-Hadad ya ce, “Zan mayar da biranen mahaifinka da na ƙwace daga mahaifinka. Za ka iya sa wurin kasuwarka a cikin Damaskus, kamar yadda mahaifinka ya yi a Samariya.” Ahab ya ce, “Bisa wannan yarjejjeniya zan sake ka.” Saboda haka ya yi yarjejjeniya da shi, sai ya bar shi ya tafi.
And he says to him, “The cities that my father took from your father, I give back, and you make streets for yourself in Damascus, as my father did in Samaria; and I, with a covenant, send you away”; and he makes a covenant with him, and sends him away.
35 Ta wurin maganar Ubangiji, ɗaya daga cikin’ya’ya maza na annabawa ya ce wa abokinsa, “Ka buge ni da makaminka,” amma mutumin ya ƙi.
And a certain man of the sons of the prophets said to his neighbor by the word of YHWH, “Please strike me”; and the man refuses to strike him,
36 Sai annabin ya ce, “Domin ba ka yi biyayya da Ubangiji ba, da zarar ka bar ni zaki zai kashe ka.” Daga baya mutumin ya tafi, zaki ya same shi, ya kuma kashe shi.
and he says to him, “Because that you have not listened to the voice of YHWH, behold, you are going from me, and the lion has struck you”; and he goes from him, and the lion finds him, and strikes him.
37 Annabin ya sami wani mutum ya ce, “Ka buge ni, ina roƙonka.” Sai mutumin ya buge shi, ya ji masa ciwo.
And he finds another man and says, “Please strike me”; and the man strikes him, striking and wounding,
38 Sa’an nan annabin ya tafi ya tsaya a bakin hanya yana jiran sarki. Ya ɓad da kamanni da ƙyalle a kansa. Ƙyallen ya sauka zuwa bisa idanunsa.
and the prophet goes and stands for the king on the way, and disguises himself with ashes on his eyes.
39 Yayinda sarki yake wucewa, sai annabin ya yi kira da ƙarfi gare shi ya ce “Ni bawanka na tafi yaƙi, sai ga wani ya kawo mini wani mutum, ya ce, ‘Ka riƙe wannan mutum, kada ka bar shi yă kuɓuta ko da ƙaƙa, idan ka bari ya kuɓuta, a bakin ranka, ko kuwa ka biya talanti ɗaya na azurfa.’
And it comes to pass—the king is passing by—that he has cried to the king and says, “Your servant went out into the midst of the battle, and behold, a man has turned aside and brings a man to me, and says, Keep this man; if he is at all missing, then your life has been for his life, or you weigh out a talent of silver;
40 Yayinda bawanka yana fama, yana kai da kawowa, sai mutumin ya ɓace.” Sai sarkin Isra’ila ya ce, “Hukuncinka ke nan, ka furta shi da kanka.”
and it comes to pass, your servant is working here and there, and he is not!” And the king of Israel says to him, “Your judgment [is] right; you have determined [it].”
41 Sai annabin ya cire ƙyallen da sauri daga kansa, da ya rufe idanunsa, sarkin Isra’ila kuwa ya gane shi a matsayi ɗaya daga cikin annabawa.
And he hurries and turns aside the ashes from off his eyes, and the king of Israel discerns him, that he [is] of the prophets,
42 Sai ya ce wa sarki, “Ga abin da Ubangiji ya ce, ‘Ka saki mutumin da na ƙudura yă mutu. Saboda haka ranka zai zama a maimakon ransa, mutanenka a maimakon mutanensa.’”
and he says to him, “Thus said YHWH: Because you have sent away the man I devoted, out of [your] hand, even your life has been for his life, and your people for his people”;
43 Cike da fushi, sarkin Isra’ila ya tafi fadarsa a Samariya.
and the king of Israel goes to his house, sulky and angry, and comes to Samaria.

< 1 Sarakuna 20 >