< 1 Sarakuna 20 >

1 Ben-Hadad sarkin Aram kuwa ya tattara mayaƙansa gaba ɗaya. Sarakuna talatin da biyu suka tafi tare da shi haɗe da dawakansu da kekunan yaƙinsu. Ya haura ya yi wa Samariya kwanto, ya kuma yaƙe ta.
And Benadad, king of Syria, gathered together all his host, and there were two and thirty kings with him, and horses, and chariots: and going up, he fought against Samaria, and besieged it.
2 Ya aika da’yan aika zuwa cikin birnin wurin Ahab sarkin Isra’ila yana cewa, “Ga abin da Ben-Hadad ya ce,
And, sending messengers to Achab king of Israel into the city,
3 ‘Azurfarka da zinariyarka nawa ne. Mafi kyau cikin matanka da’ya’yanka nawa ne.’”
He said: Thus saith Benadad: Thy silver, and thy gold is mine: and thy wives, and thy goodliest children are mine.
4 Sarkin Isra’ila ya amsa, ya ce, “Kamar dai yadda ka faɗa, ranka yă daɗe, sarki. Ni da dukan abin da nake da shi, naka ne.”
And the king of Israel answered: According to thy word, my lord O king, I am thine, and all that I have.
5 Sai’yan aikan suka sāke dawo suka ce, “Ga abin da Ben-Hadad ya ce, ‘Na aika ka ba da azurfarka da zinariyarka, matanka da kuma’ya’yanka.
And the messengers came again, and said: Thus saith Benadad, who sent us unto thee: Thy silver, and thy gold, and thy wives, and thy children thou shalt deliver up to me.
6 Amma war haka gobe zan aika shugabannina su bincika fadanka da kuma gidajen shugabanninka. Za su kwashe dukan abubuwan da kake ganin darajarsu su tafi.’”
Tomorrow therefore at this same hour I will send my servants to thee, and they shall search thy house, and the houses of thy servants: and all that pleaseth them, they shall put in their hands, and take away.
7 Sarkin Isra’ila ya tattara dukan dattawan ƙasar, ya ce musu, “Ku duba fa, wannan mutum yana neman tsokana! Sa’ad da ya aika in ba shi matana da’ya’yana, azurfana da zinariyana, ban hana masa ba.”
And the king of Israel called all the ancients of the land, and said: Mark, and see that he layeth snares for us. For he sent to me for my wives, and for my children, and for my silver and gold: and I said not nay.
8 Dattawa da dukan mutane suka amsa, suka ce, “Kada ka saurare shi ko ka yarda da abin da yake bukata.”
And all the ancients, and all the people said to him: Hearken not to him, nor consent to him.
9 Saboda haka ya ba wa’yan aikan Ben-Hadad amsa, ya ce, “Ku faɗa wa ranka yă daɗe, sarki, ‘Bawanka zai yi dukan abin da ka bukaci da farko, amma wannan na ƙarshe ba zan iya yin ba.’” Suka tafi suka kai amsar wa Ben-Hadad.
Wherefore he answered the messengers of Benadad: Tell my lord the king: All that thou didst send for to me thy servant at first, I will do: but this thing I cannot do.
10 Sai Ben-Hadad ya aika da wani saƙo wa Ahab, ya ce, “Bari alloli su yi da ni yadda suke so, su kuma yi haka da tsanani, in isashen ƙura ta rage a Samariya da za a iya ba wa mutanena a tafin hannu.”
And the messengers returning brought him word. And he sent again and said: Such and such things may the gods do to me, and more may they add, if the dust of Samaria shall suffice for handfuls for all the people that follow me.
11 Sarki Isra’ila ya amsa, ya ce, “Ku faɗa masa, ‘Wanda ya sa kayan yaƙinsa bai kamata yă yi fariya ba sai ya tuɓe su.’”
And the king of Israel answering, said: Tell him: Let not the girded boast himself as the ungirded.
12 Ben-Hadad ya ji wannan saƙo yayinda shi da sarakunan suke sha a cikin tentunansu, sai ya umarce mutanensa, ya ce, “Ku shirya don yaƙi.” Saboda haka suka shirya don su yaƙi birnin.
And it came to pass, when Benadad heard this word, that he and the kings were drinking in pavilions, and he said to his servants: Beset the city. And they beset it.
13 Ana cikin haka sai wani annabi ya zo wurin Ahab sarkin Isra’ila ya sanar masa cewa, “Ga abin da Ubangiji ya ce, ‘Ka ga wannan ɗumbun mayaƙa? Zan ba da su cikin hannunka a yau, sa’an nan za ka san cewa ni ne Ubangiji.’”
And behold a prophet coming to Achab king of Israel, said to him: Thus saith the Lord: Hast thou seen all this exceeding great multitude, behold I will deliver them into thy hand this day: that thou mayest know that I am the Lord.
14 Ahab ya ce, “Amma wa zai yi haka?” Annabin ya amsa, “Ga abin da Ubangiji ya ce, ‘Sojoji matasa na shugabannin yankuna za su yi haka.’” Ya tambaya, “Wa kuma zai fara yaƙin?” Annabin ya amsa, “Kai za ka fara.”
And Achab said: By whom? And he said to him: Thus saith the Lord: By the servants of the princes of the provinces. And he said: Who shall begin to fight? And he said: Thou.
15 Saboda haka Ahab ya kira sojoji matasa na shugabannin yankuna, mutum 232. Sa’an nan ya tattara sauran Isra’ilawa su 7,000 gaba ɗaya.
So he mustered the servants of the princes of the provinces, and he found the number of two hundred and thirty-two: and he mustered after them the people, all the children of Israel, seven thousand:
16 Suka fita da tsakar rana yayinda Ben-Hadad tare da sarakuna 32 masu goyon bayansa suke cikin tentunansu suna sha, suna buguwa.
And they went out at noon. But Benadad was drinking himself drunk in his pavilion, and the two and thirty kings with him, who were come to help him.
17 Sojojin nan matasa na shugabannin yankuna suka fara fita. Ben-Hadad kuwa ya riga ya aiki’yan leƙen asiri, waɗanda suka ce, “Mutane suna zuwa daga Samariya.”
And the servants of the princes of the provinces went out first. And Benadad sent. And they told him, saying: There are men come out of Samaria.
18 Ya ce, “In sun fito don salama, ku kamo su da rai; in sun fito yaƙi ne, ku kamo su da rai.”
And he said: Whether they come for peace, take them alive: or whether they come to fight, take them alive.
19 Sojojin nan matasa na shugabannin yankuna suka taka suka fita daga birnin da mayaƙa a bayansu.
So the servants of the princes of the provinces went out, and the rest of the army followed:
20 Kowannensu kuwa ya buge abokin gābansa. Ganin wannan, sai Arameyawa suka gudu, Isra’ilawa suna bi. Amma Ben-Hadad na Aram ya tsere a kan dokinsa tare da waɗansu mahayan dawakansa.
And every one slew the man that came against him: and the Syrians fled, and Israel pursued after them. And Benadad king of Syria fled away on horseback with his horsemen.
21 Sarki Isra’ila ya bi, ya kuma sha ƙarfin dawakan da keken yaƙin, ya kashe Arameyawa da yawa.
But the king of Israel going out overthrew the horses and chariots, and slew the Syrians with a great slaughter.
22 Daga baya, annabin ya zo wurin sarkin Isra’ila ya ce, “Ka ƙarfafa matsayinka ka kuma ga abin da za a yi, gama a bazara mai zuwa sarkin Aram zai sāke kawo yaƙi.”
(And a prophet coming to the king of Israel, said to him: Go, and strengthen thyself, and know, and see what thou dost: for the next year the king of Syria will come up against thee.)
23 Ana cikin haka, shugabannin sarkin Aram suka ba shi shawara, “Allolinsu, allolin tuddai ne. Shi ya sa suka fi mu ƙarfi. Amma in mun yaƙe su a fili, tabbatacce za mu fi su ƙarfi.
But the servants of the king of Syria said to him: Their gods are gods of the hills, therefore they have overcome us: but it is better that we should fight against them in the plains, and we shall overcome them.
24 Ka yi wannan. Ka cire dukan sarakuna daga matsayinsu ka sa waɗansu shugabanni a maimakonsu.
Do thou therefore this thing: Remove all the kings from thy army, and put captains in their stead:
25 Dole kuma ka tā da waɗansu mayaƙa kamar waɗanda ka rasa, doki don doki, keken yaƙi kuma don keken yaƙi, saboda mu iya yaƙe Isra’ila a fili. Ta haka tabbatacce za mu fi ƙarfinsu.” Sai ya yarda da su, ya kuma yi haka.
And make up the number of soldiers that have been slain of thine, and horses according to the former horses, and chariots according to the chariots which thou hadst before: and we will fight against them in the plains, and thou shalt see that we shall overcome them. He believed their counsel and did so.
26 Bazara na biye Ben-Hadad ya tattara Arameyawa, ya haura zuwa Afek don yă yaƙi Isra’ila.
Wherefore at the return of the year, Benadad mustered the Syrians, ancient up to Aphec, to fight against Israel.
27 Sa’ad da aka tattara Isra’ilawa, aka kuma ba su guzuri, sai suka taka suka fita don su sadu da Arameyawa. Isra’ilawa suka kafa sansani ɗaura da su kamar ƙananan garkuna biyu na awaki, yayinda Arameyawa suka rufe dukan jejin.
And the children of Israel were mustered, and taking victuals went out on the other side, and camped over against them, like two little hocks of goats: but the Syrians filled the land.
28 Sai mutumin Allah ya zo ya ce wa sarkin Isra’ila, “Ga abin da Ubangiji ya ce, ‘Domin Arameyawa suna tsammani Ubangiji allahn tuddai ne, ba allahn kwari ba, zan ba da wannan ɗumbun mayaƙa a hannuwanka, za ka kuwa sani ni ne Ubangiji.’”
(And a man of God coming, said to the king of Israel: Thus saith the Lord: Because the Syrians have said: The Lord is God of the hills, but is not God of the valleys: I will deliver all this great multitude into thy hand, and you shall know that I am the Lord.)
29 Kwana bakwai suka yi sansani ɗaura da juna, a rana ta bakwai sai yaƙi ya haɗu. Isra’ilawa suka kashe sojojin kafa na Arameyawa dubu ɗari a rana ɗaya.
And both sides set their armies in array one against the other seven days, and on the seventh day the battle was fought: and the children of Israel slew of the Syrians a hundred thousand footmen in one day.
30 Sauransu suka tsere zuwa birnin Afek, inda katangar ya fāɗa a kan mutum dubu ashirin da bakwai. Sai Ben-Hadad ya gudu zuwa birni ya ɓuya a ciki cikin ɗaki.
And they that remained fled to Aphec, into the city: and the wall fell upon seven and twenty thousand men, that were left. And Benadad fleeing went into the city, into a chamber that was within a chamber.
31 Fadawansa suka je suka ce masa, “Mun ji an ce sarakunan Isra’ila masu jinƙai ne, bari mu sa tufafin makoki, mu ɗaura igiyoyi a wuyanmu, sa’an nan mu tafi wurin sarkin Isra’ila, wataƙila zai bar ka da rai.”
And his servants said to him: Behold, we have heard that the kings of the house of Israel are merciful: so let us put sackcloth on our loins, and ropes on our heads, and go out to the king of Israel: perhaps he will save our lives.
32 Saye da tufafin makoki kewaye a gindinsu, da kuma igiyoyi kewaye da kawunansu, suka tafi wurin sarkin Isra’ila, suka ce, “Bawanka Ben-Hadad ya ce, ‘Ina roƙonka bari in rayu.’” Sarki ya amsa, “Har yanzu yana da rai? Shi ɗan’uwana ne.”
So they girded sackcloth on their loins, and put ropes on their heads, and came to the king of Israel, and said to him: Thy servant Benadad saith: I beseech thee let me have my life. And he said: If he be yet alive he is my brother.
33 Da ma abin da fadawan suke so su ji ke nan, sai suka yi sauri, suka karɓi maganar a bakinsa, suka ce, “I, ɗan’uwanka, Ben-hadad!” Sarki ya ce, “Ku je ku kawo shi.” Da Ben-Hadad ya fita, sai Ahab ya sa aka kawo shi cikin keken yaƙinsa.
The men took this for a sign: and in haste caught the word out of his mouth, and said: Thy brother Benadad. And he said to them: Go, and bring him to me. Then Benadad came out to him, and he lifted him up into his chariot.
34 Ben-Hadad ya ce, “Zan mayar da biranen mahaifinka da na ƙwace daga mahaifinka. Za ka iya sa wurin kasuwarka a cikin Damaskus, kamar yadda mahaifinka ya yi a Samariya.” Ahab ya ce, “Bisa wannan yarjejjeniya zan sake ka.” Saboda haka ya yi yarjejjeniya da shi, sai ya bar shi ya tafi.
And he said to him: The cities which my father took from thy father, I will restore: and do thou make thee streets in Damascus, as my father made in Samaria, and having made a league I will depart from thee. So he made a league with him, and let him go.
35 Ta wurin maganar Ubangiji, ɗaya daga cikin’ya’ya maza na annabawa ya ce wa abokinsa, “Ka buge ni da makaminka,” amma mutumin ya ƙi.
Then a certain man of the sons of the prophets said to his companion in the word of the Lord: Strike me. But he would not strike.
36 Sai annabin ya ce, “Domin ba ka yi biyayya da Ubangiji ba, da zarar ka bar ni zaki zai kashe ka.” Daga baya mutumin ya tafi, zaki ya same shi, ya kuma kashe shi.
Then he said to him: Because thou wouldst not hearken to the word of the Lord, behold then shalt depart from me, and a lion shall slay thee. And when he was gone a little from him, a lion found him, and slew him.
37 Annabin ya sami wani mutum ya ce, “Ka buge ni, ina roƙonka.” Sai mutumin ya buge shi, ya ji masa ciwo.
Then he found another man, and said to him: Strike me. And he struck him, and wounded him.
38 Sa’an nan annabin ya tafi ya tsaya a bakin hanya yana jiran sarki. Ya ɓad da kamanni da ƙyalle a kansa. Ƙyallen ya sauka zuwa bisa idanunsa.
So the prophet went, and met the king in the way, and disguised himself by sprinkling dust on his face and his eyes.
39 Yayinda sarki yake wucewa, sai annabin ya yi kira da ƙarfi gare shi ya ce “Ni bawanka na tafi yaƙi, sai ga wani ya kawo mini wani mutum, ya ce, ‘Ka riƙe wannan mutum, kada ka bar shi yă kuɓuta ko da ƙaƙa, idan ka bari ya kuɓuta, a bakin ranka, ko kuwa ka biya talanti ɗaya na azurfa.’
And as the king passed by, he cried to the king, and said: Thy servant went out to fight hand to hand: and when a certain man was run away, one brought him to me, and said: Keep this man: and if he shall slip away, thy life shall be for his life, or thou shalt pay a talent of silver.
40 Yayinda bawanka yana fama, yana kai da kawowa, sai mutumin ya ɓace.” Sai sarkin Isra’ila ya ce, “Hukuncinka ke nan, ka furta shi da kanka.”
And whilst I in a hurry turned this way and that, on a sudden he was not to be seen. And the king of Israel said to him: This is thy judgment, which thyself hast decreed.
41 Sai annabin ya cire ƙyallen da sauri daga kansa, da ya rufe idanunsa, sarkin Isra’ila kuwa ya gane shi a matsayi ɗaya daga cikin annabawa.
But he forthwith wiped off the dust from his face, and the king of Israel knew him, that he was one of the prophets.
42 Sai ya ce wa sarki, “Ga abin da Ubangiji ya ce, ‘Ka saki mutumin da na ƙudura yă mutu. Saboda haka ranka zai zama a maimakon ransa, mutanenka a maimakon mutanensa.’”
And he said to him: Thus saith the Lord: Because thou hast let go out of thy hand a mall worthy of death, thy life shall be for his life, and thy people for his people.
43 Cike da fushi, sarkin Isra’ila ya tafi fadarsa a Samariya.
And the king of Israel returned to his house, slighting to hear, and raging came into Samaria.

< 1 Sarakuna 20 >