< 1 Sarakuna 20 >

1 Ben-Hadad sarkin Aram kuwa ya tattara mayaƙansa gaba ɗaya. Sarakuna talatin da biyu suka tafi tare da shi haɗe da dawakansu da kekunan yaƙinsu. Ya haura ya yi wa Samariya kwanto, ya kuma yaƙe ta.
Then Benhadad, the king of Syria, gathered together his entire army. And there were thirty-two kings with him, with horses and chariots. And ascending, he fought against Samaria, and he besieged it.
2 Ya aika da’yan aika zuwa cikin birnin wurin Ahab sarkin Isra’ila yana cewa, “Ga abin da Ben-Hadad ya ce,
And sending messengers into the city, to Ahab, the king of Israel,
3 ‘Azurfarka da zinariyarka nawa ne. Mafi kyau cikin matanka da’ya’yanka nawa ne.’”
he said: “Thus says Benhadad: Your silver and your gold is mine. And your wives and your best sons are mine.”
4 Sarkin Isra’ila ya amsa, ya ce, “Kamar dai yadda ka faɗa, ranka yă daɗe, sarki. Ni da dukan abin da nake da shi, naka ne.”
And the king of Israel responded, “In agreement with your word, my lord the king, I am yours, with all that is mine.”
5 Sai’yan aikan suka sāke dawo suka ce, “Ga abin da Ben-Hadad ya ce, ‘Na aika ka ba da azurfarka da zinariyarka, matanka da kuma’ya’yanka.
And the messengers, returning, said: “Thus says Benhadad, who sent us to you: Your silver and your gold, and your wives and your sons, you shall give to me.
6 Amma war haka gobe zan aika shugabannina su bincika fadanka da kuma gidajen shugabanninka. Za su kwashe dukan abubuwan da kake ganin darajarsu su tafi.’”
Therefore, tomorrow, at this same hour, I will send my servants to you, and they will search your house and the houses of your servants. And all that pleases them, they will put in their hands and take away.”
7 Sarkin Isra’ila ya tattara dukan dattawan ƙasar, ya ce musu, “Ku duba fa, wannan mutum yana neman tsokana! Sa’ad da ya aika in ba shi matana da’ya’yana, azurfana da zinariyana, ban hana masa ba.”
Then the king of Israel called all the elders of the land, and he said: “Let your souls take heed, and see that he commits treachery against us. For he sent to me for my wives and sons, and for silver and gold. And I did not refuse.”
8 Dattawa da dukan mutane suka amsa, suka ce, “Kada ka saurare shi ko ka yarda da abin da yake bukata.”
And all those greater by birth, with all the people, said to him, “You should neither listen, nor acquiesce to him.”
9 Saboda haka ya ba wa’yan aikan Ben-Hadad amsa, ya ce, “Ku faɗa wa ranka yă daɗe, sarki, ‘Bawanka zai yi dukan abin da ka bukaci da farko, amma wannan na ƙarshe ba zan iya yin ba.’” Suka tafi suka kai amsar wa Ben-Hadad.
And so, he responded to the messengers of Benhadad: “Tell my lord the king: Everything about which you sent to me in the beginning, I your servant will do. But this thing, I am not able to do.”
10 Sai Ben-Hadad ya aika da wani saƙo wa Ahab, ya ce, “Bari alloli su yi da ni yadda suke so, su kuma yi haka da tsanani, in isashen ƙura ta rage a Samariya da za a iya ba wa mutanena a tafin hannu.”
And returning, the messengers took this to him, and he sent again and said, “May the gods do these things to me, and may they add these other things, if the dust of Samaria is enough to fill the hands of all the people who follow me.”
11 Sarki Isra’ila ya amsa, ya ce, “Ku faɗa masa, ‘Wanda ya sa kayan yaƙinsa bai kamata yă yi fariya ba sai ya tuɓe su.’”
And responding, the king of Israel said, “Tell him that one who is girded should not boast the same as one who is ungirded.”
12 Ben-Hadad ya ji wannan saƙo yayinda shi da sarakunan suke sha a cikin tentunansu, sai ya umarce mutanensa, ya ce, “Ku shirya don yaƙi.” Saboda haka suka shirya don su yaƙi birnin.
Then it happened that, when Benhadad had heard this word, he and the kings were drinking in a pavilion. And he said to his servants, “Encircle the city.” And they encircled it.
13 Ana cikin haka sai wani annabi ya zo wurin Ahab sarkin Isra’ila ya sanar masa cewa, “Ga abin da Ubangiji ya ce, ‘Ka ga wannan ɗumbun mayaƙa? Zan ba da su cikin hannunka a yau, sa’an nan za ka san cewa ni ne Ubangiji.’”
And behold, one prophet, drawing near to Ahab, the king of Israel, said to him: “Thus says the Lord: Certainly, you have seen this entire exceedingly great multitude? Behold, I will deliver them into your hand today, so that you may know that I am the Lord.”
14 Ahab ya ce, “Amma wa zai yi haka?” Annabin ya amsa, “Ga abin da Ubangiji ya ce, ‘Sojoji matasa na shugabannin yankuna za su yi haka.’” Ya tambaya, “Wa kuma zai fara yaƙin?” Annabin ya amsa, “Kai za ka fara.”
And Ahab said, “By whom?” And he said to him: “Thus says the Lord: By the footmen of the leaders of the provinces.” And he said, “Who should begin to do battle?” And he said, “You should.”
15 Saboda haka Ahab ya kira sojoji matasa na shugabannin yankuna, mutum 232. Sa’an nan ya tattara sauran Isra’ilawa su 7,000 gaba ɗaya.
Therefore, he took a count of the servants of the leaders of the provinces. And he found the number to be two hundred thirty-two. And he set them in order after the people, all the sons of Israel, who were seven thousand.
16 Suka fita da tsakar rana yayinda Ben-Hadad tare da sarakuna 32 masu goyon bayansa suke cikin tentunansu suna sha, suna buguwa.
And they went out at midday. But Benhadad was drinking; he was inebriated in his pavilion, and the thirty-two kings with him, who had arrived in order to assist him.
17 Sojojin nan matasa na shugabannin yankuna suka fara fita. Ben-Hadad kuwa ya riga ya aiki’yan leƙen asiri, waɗanda suka ce, “Mutane suna zuwa daga Samariya.”
Then the servants of the leaders of the provinces went out to the first place, at the front. And so, Benhadad sent, and they reported to him, saying: “Men have gone out from Samaria.”
18 Ya ce, “In sun fito don salama, ku kamo su da rai; in sun fito yaƙi ne, ku kamo su da rai.”
And he said: “If they have arrived for peace, apprehend them alive; if to do battle, capture them alive.”
19 Sojojin nan matasa na shugabannin yankuna suka taka suka fita daga birnin da mayaƙa a bayansu.
Therefore, the servants of the leaders of the provinces went out, and the remainder of the army was following.
20 Kowannensu kuwa ya buge abokin gābansa. Ganin wannan, sai Arameyawa suka gudu, Isra’ilawa suna bi. Amma Ben-Hadad na Aram ya tsere a kan dokinsa tare da waɗansu mahayan dawakansa.
And each one struck down the man who came against him. And the Syrians fled, and Israel pursued them. Also, Benhadad, the king of Syria, fled on a horse, with his horsemen.
21 Sarki Isra’ila ya bi, ya kuma sha ƙarfin dawakan da keken yaƙin, ya kashe Arameyawa da yawa.
But the king of Israel, going out, struck the horses and the chariots, and he struck the Syrians with a great slaughter.
22 Daga baya, annabin ya zo wurin sarkin Isra’ila ya ce, “Ka ƙarfafa matsayinka ka kuma ga abin da za a yi, gama a bazara mai zuwa sarkin Aram zai sāke kawo yaƙi.”
Then a prophet, drawing near to the king of Israel, said to him: “Go and be strengthened. And know and see what you are doing. For in the following year, the king of Syria will rise up against you.”
23 Ana cikin haka, shugabannin sarkin Aram suka ba shi shawara, “Allolinsu, allolin tuddai ne. Shi ya sa suka fi mu ƙarfi. Amma in mun yaƙe su a fili, tabbatacce za mu fi su ƙarfi.
Then truly, the servants of the king of Syria said to him: “Their gods are the gods of the mountains; because of this, they have overwhelmed us. But it is better that we fight against them in the plains, and then we will prevail over them.
24 Ka yi wannan. Ka cire dukan sarakuna daga matsayinsu ka sa waɗansu shugabanni a maimakonsu.
Therefore, you should do this word: Remove each of the kings from your army, and set commanders in their place.
25 Dole kuma ka tā da waɗansu mayaƙa kamar waɗanda ka rasa, doki don doki, keken yaƙi kuma don keken yaƙi, saboda mu iya yaƙe Isra’ila a fili. Ta haka tabbatacce za mu fi ƙarfinsu.” Sai ya yarda da su, ya kuma yi haka.
And replace the number of soldiers who have been cut down of yours, and the horses, in accord with the earlier number of horses, and the chariots, in accord with the number of chariots that you had before. And we will fight against them in the plains, and you will see that we will prevail over them.” And he trusted in their counsel, and he did so.
26 Bazara na biye Ben-Hadad ya tattara Arameyawa, ya haura zuwa Afek don yă yaƙi Isra’ila.
Therefore, after the passing of the year, Benhadad took a count of the Syrians, and he ascended to Aphek, so that he might fight against Israel.
27 Sa’ad da aka tattara Isra’ilawa, aka kuma ba su guzuri, sai suka taka suka fita don su sadu da Arameyawa. Isra’ilawa suka kafa sansani ɗaura da su kamar ƙananan garkuna biyu na awaki, yayinda Arameyawa suka rufe dukan jejin.
Then the sons of Israel were numbered, and taking provisions, they set out to the opposite side. And they stretched out the camp facing them, like two little flocks of goats. But the Syrians filled the land.
28 Sai mutumin Allah ya zo ya ce wa sarkin Isra’ila, “Ga abin da Ubangiji ya ce, ‘Domin Arameyawa suna tsammani Ubangiji allahn tuddai ne, ba allahn kwari ba, zan ba da wannan ɗumbun mayaƙa a hannuwanka, za ka kuwa sani ni ne Ubangiji.’”
And one man of God, drawing near, said to the king of Israel: “Thus says the Lord: Because the Syrians have said, ‘The Lord is the God of the mountains, but he is not the God of the valleys,’ I will deliver this entire great multitude into your hand, and you shall know that I am the Lord.”
29 Kwana bakwai suka yi sansani ɗaura da juna, a rana ta bakwai sai yaƙi ya haɗu. Isra’ilawa suka kashe sojojin kafa na Arameyawa dubu ɗari a rana ɗaya.
And for seven days, both sides arranged each of their battle lines. Then, on the seventh day, the war was undertaken. And the sons of Israel struck down, from the Syrians, one hundred thousand foot soldiers in one day.
30 Sauransu suka tsere zuwa birnin Afek, inda katangar ya fāɗa a kan mutum dubu ashirin da bakwai. Sai Ben-Hadad ya gudu zuwa birni ya ɓuya a ciki cikin ɗaki.
Then those who had remained fled to Aphek, into the city. And the wall fell upon twenty-seven thousand men of those who had remained. Then Benhadad, fleeing, entered the city, into a room that was inside another room.
31 Fadawansa suka je suka ce masa, “Mun ji an ce sarakunan Isra’ila masu jinƙai ne, bari mu sa tufafin makoki, mu ɗaura igiyoyi a wuyanmu, sa’an nan mu tafi wurin sarkin Isra’ila, wataƙila zai bar ka da rai.”
And his servants said to him: “Behold, we have heard that the kings of the house of Israel show clemency. And so, let us put sackcloth around our waists, and ropes on our heads, and let us go out to the king of Israel. Perhaps he will save our lives.”
32 Saye da tufafin makoki kewaye a gindinsu, da kuma igiyoyi kewaye da kawunansu, suka tafi wurin sarkin Isra’ila, suka ce, “Bawanka Ben-Hadad ya ce, ‘Ina roƙonka bari in rayu.’” Sarki ya amsa, “Har yanzu yana da rai? Shi ɗan’uwana ne.”
So they wrapped sackcloth around their waists, and they placed ropes on their heads. And they went to the king of Israel, and they said to him: “Your servant, Benhadad, says: ‘I beg you to let my soul live.’” And he replied, “If he is still alive, he is my brother.”
33 Da ma abin da fadawan suke so su ji ke nan, sai suka yi sauri, suka karɓi maganar a bakinsa, suka ce, “I, ɗan’uwanka, Ben-hadad!” Sarki ya ce, “Ku je ku kawo shi.” Da Ben-Hadad ya fita, sai Ahab ya sa aka kawo shi cikin keken yaƙinsa.
The men accepted this as a good sign. And hastily, they took up the word from his mouth, and they said, “Benhadad is your brother.” And he said to them, “Go, and bring him to me.” Therefore, Benhadad went out to him, and he lifted him onto his chariot.
34 Ben-Hadad ya ce, “Zan mayar da biranen mahaifinka da na ƙwace daga mahaifinka. Za ka iya sa wurin kasuwarka a cikin Damaskus, kamar yadda mahaifinka ya yi a Samariya.” Ahab ya ce, “Bisa wannan yarjejjeniya zan sake ka.” Saboda haka ya yi yarjejjeniya da shi, sai ya bar shi ya tafi.
And he said to him: “The cities that my father took from your father, I will return. And you may make streets for yourself in Damascus, just as my father made in Samaria. And after we have made a pact, I will withdraw from you.” Therefore, he formed a pact with him, and he released him.
35 Ta wurin maganar Ubangiji, ɗaya daga cikin’ya’ya maza na annabawa ya ce wa abokinsa, “Ka buge ni da makaminka,” amma mutumin ya ƙi.
Then a certain man from the sons of the prophets said to his associate, by the word of the Lord, “Strike me.” But he was not willing to strike.
36 Sai annabin ya ce, “Domin ba ka yi biyayya da Ubangiji ba, da zarar ka bar ni zaki zai kashe ka.” Daga baya mutumin ya tafi, zaki ya same shi, ya kuma kashe shi.
And he said to him: “Because you were not willing to heed the voice of the Lord, behold, you will depart from me, and a lion will slay you. And when he had departed a short distance from him, a lion found him, and slew him.
37 Annabin ya sami wani mutum ya ce, “Ka buge ni, ina roƙonka.” Sai mutumin ya buge shi, ya ji masa ciwo.
But upon finding another man, he said to him, “Strike me.” And he struck him, and wounded him.
38 Sa’an nan annabin ya tafi ya tsaya a bakin hanya yana jiran sarki. Ya ɓad da kamanni da ƙyalle a kansa. Ƙyallen ya sauka zuwa bisa idanunsa.
Then the prophet departed. And he met the king along the way, and he changed his appearance by sprinkling dust around his mouth and eyes.
39 Yayinda sarki yake wucewa, sai annabin ya yi kira da ƙarfi gare shi ya ce “Ni bawanka na tafi yaƙi, sai ga wani ya kawo mini wani mutum, ya ce, ‘Ka riƙe wannan mutum, kada ka bar shi yă kuɓuta ko da ƙaƙa, idan ka bari ya kuɓuta, a bakin ranka, ko kuwa ka biya talanti ɗaya na azurfa.’
And when the king had passed by, he cried out to the king, and he said: “Your servant went out to do battle in close quarters. And when one man had fled, a certain person brought him to me, and he said: ‘Guard this man. For if he slips away, your life will take the place of his life, or you will weigh out one talent of silver.’
40 Yayinda bawanka yana fama, yana kai da kawowa, sai mutumin ya ɓace.” Sai sarkin Isra’ila ya ce, “Hukuncinka ke nan, ka furta shi da kanka.”
And while I was distracted, turning one way and another, suddenly, he was not to be seen.” And the king of Israel said to him, “This is your judgment, that which you yourself have decreed.”
41 Sai annabin ya cire ƙyallen da sauri daga kansa, da ya rufe idanunsa, sarkin Isra’ila kuwa ya gane shi a matsayi ɗaya daga cikin annabawa.
Then immediately, he wiped away the dust from his face, and the king of Israel recognized him, that he was one of the prophets.
42 Sai ya ce wa sarki, “Ga abin da Ubangiji ya ce, ‘Ka saki mutumin da na ƙudura yă mutu. Saboda haka ranka zai zama a maimakon ransa, mutanenka a maimakon mutanensa.’”
And he said to him: “Thus says the Lord: Because you have released from your hand a man worthy of death, your life will take the place of his life, and your people will take the place of his people.”
43 Cike da fushi, sarkin Isra’ila ya tafi fadarsa a Samariya.
And so the king of Israel returned to his house, unwilling to listen, and a fury entered into Samaria.

< 1 Sarakuna 20 >