< 1 Sarakuna 20 >

1 Ben-Hadad sarkin Aram kuwa ya tattara mayaƙansa gaba ɗaya. Sarakuna talatin da biyu suka tafi tare da shi haɗe da dawakansu da kekunan yaƙinsu. Ya haura ya yi wa Samariya kwanto, ya kuma yaƙe ta.
Now Ben-hadad, king of Aram, got all his army together, and thirty-two kings with him, and horses and carriages of war; he went up and made war on Samaria, shutting it in.
2 Ya aika da’yan aika zuwa cikin birnin wurin Ahab sarkin Isra’ila yana cewa, “Ga abin da Ben-Hadad ya ce,
And he sent representatives into the town to Ahab, king of Israel;
3 ‘Azurfarka da zinariyarka nawa ne. Mafi kyau cikin matanka da’ya’yanka nawa ne.’”
And they said to him, Ben-hadad says, Your silver and your gold are mine; and your wives and children are mine.
4 Sarkin Isra’ila ya amsa, ya ce, “Kamar dai yadda ka faɗa, ranka yă daɗe, sarki. Ni da dukan abin da nake da shi, naka ne.”
And the king of Israel sent him an answer saying, As you say, my lord king, I am yours with all I have.
5 Sai’yan aikan suka sāke dawo suka ce, “Ga abin da Ben-Hadad ya ce, ‘Na aika ka ba da azurfarka da zinariyarka, matanka da kuma’ya’yanka.
Then the representatives came back again, and said, These are the words of Ben-hadad: I sent to you saying, Give up to me your silver and your gold, your wives and your children;
6 Amma war haka gobe zan aika shugabannina su bincika fadanka da kuma gidajen shugabanninka. Za su kwashe dukan abubuwan da kake ganin darajarsu su tafi.’”
But I will send my servants to you tomorrow about this time, to make a search through your house and the houses of your people, and everything which is pleasing in your eyes they will take away in their hands.
7 Sarkin Isra’ila ya tattara dukan dattawan ƙasar, ya ce musu, “Ku duba fa, wannan mutum yana neman tsokana! Sa’ad da ya aika in ba shi matana da’ya’yana, azurfana da zinariyana, ban hana masa ba.”
Then the king of Israel sent for all the responsible men of the land, and said, Now will you take note and see the evil purpose of this man: he sent for my wives and my children, my silver and my gold, and I did not keep them back.
8 Dattawa da dukan mutane suka amsa, suka ce, “Kada ka saurare shi ko ka yarda da abin da yake bukata.”
And all the responsible men and the people said to him, Do not give attention to him or do what he says.
9 Saboda haka ya ba wa’yan aikan Ben-Hadad amsa, ya ce, “Ku faɗa wa ranka yă daɗe, sarki, ‘Bawanka zai yi dukan abin da ka bukaci da farko, amma wannan na ƙarshe ba zan iya yin ba.’” Suka tafi suka kai amsar wa Ben-Hadad.
So he said to the representatives of Ben-hadad, Say to my lord the king, All the orders you sent the first time I will do; but this thing I may not do. And the representatives went back with this answer.
10 Sai Ben-Hadad ya aika da wani saƙo wa Ahab, ya ce, “Bari alloli su yi da ni yadda suke so, su kuma yi haka da tsanani, in isashen ƙura ta rage a Samariya da za a iya ba wa mutanena a tafin hannu.”
Then Ben-hadad sent to him, saying, May the gods' punishment be on me if there is enough of the dust of Samaria for all the people at my feet to take some in their hands.
11 Sarki Isra’ila ya amsa, ya ce, “Ku faɗa masa, ‘Wanda ya sa kayan yaƙinsa bai kamata yă yi fariya ba sai ya tuɓe su.’”
And the king of Israel said in answer, Say to him, The time for loud talk is not when a man is putting on his arms, but when he is taking them off.
12 Ben-Hadad ya ji wannan saƙo yayinda shi da sarakunan suke sha a cikin tentunansu, sai ya umarce mutanensa, ya ce, “Ku shirya don yaƙi.” Saboda haka suka shirya don su yaƙi birnin.
Now when this answer was given to Ben-hadad, he was drinking with the kings in the tents, and he said to his men, Take up your positions. So they put themselves in position for attacking the town.
13 Ana cikin haka sai wani annabi ya zo wurin Ahab sarkin Isra’ila ya sanar masa cewa, “Ga abin da Ubangiji ya ce, ‘Ka ga wannan ɗumbun mayaƙa? Zan ba da su cikin hannunka a yau, sa’an nan za ka san cewa ni ne Ubangiji.’”
Then a prophet came up to Ahab, king of Israel, and said, The Lord says, Have you seen all this great army? See, I will give it into your hands today, and you will see that I am the Lord.
14 Ahab ya ce, “Amma wa zai yi haka?” Annabin ya amsa, “Ga abin da Ubangiji ya ce, ‘Sojoji matasa na shugabannin yankuna za su yi haka.’” Ya tambaya, “Wa kuma zai fara yaƙin?” Annabin ya amsa, “Kai za ka fara.”
And Ahab said, By whom? And he said, The Lord says, By the servants of the chiefs who are over the divisions of the land. Then he said, By whom is the fighting to be started? And he made answer, By you.
15 Saboda haka Ahab ya kira sojoji matasa na shugabannin yankuna, mutum 232. Sa’an nan ya tattara sauran Isra’ilawa su 7,000 gaba ɗaya.
Then he got together the servants of all the chiefs who were over the divisions of the land, two hundred and thirty-two of them; and after them, he got together all the people, all the children of Israel, seven thousand.
16 Suka fita da tsakar rana yayinda Ben-Hadad tare da sarakuna 32 masu goyon bayansa suke cikin tentunansu suna sha, suna buguwa.
And in the middle of the day they went out. But Ben-hadad was drinking in the tents with the thirty-two kings who were helping him.
17 Sojojin nan matasa na shugabannin yankuna suka fara fita. Ben-Hadad kuwa ya riga ya aiki’yan leƙen asiri, waɗanda suka ce, “Mutane suna zuwa daga Samariya.”
And the servants of the chiefs who were over the divisions of the land went forward first; and when Ben-hadad sent out, they gave him the news, saying, Men have come out from Samaria.
18 Ya ce, “In sun fito don salama, ku kamo su da rai; in sun fito yaƙi ne, ku kamo su da rai.”
And he said, If they have come out for peace, take them living, and if they have come out for war, take them living.
19 Sojojin nan matasa na shugabannin yankuna suka taka suka fita daga birnin da mayaƙa a bayansu.
So the servants of the chiefs of the divisions of the land went out of the town, with the army coming after them.
20 Kowannensu kuwa ya buge abokin gābansa. Ganin wannan, sai Arameyawa suka gudu, Isra’ilawa suna bi. Amma Ben-Hadad na Aram ya tsere a kan dokinsa tare da waɗansu mahayan dawakansa.
And every one of them put his man to death, and the Aramaeans went in flight with Israel after them; and Ben-hadad, king of Aram, got away safely on a horse with his horsemen.
21 Sarki Isra’ila ya bi, ya kuma sha ƙarfin dawakan da keken yaƙin, ya kashe Arameyawa da yawa.
And the king of Israel went out and took the horses and the war-carriages, and made great destruction among the Aramaeans.
22 Daga baya, annabin ya zo wurin sarkin Isra’ila ya ce, “Ka ƙarfafa matsayinka ka kuma ga abin da za a yi, gama a bazara mai zuwa sarkin Aram zai sāke kawo yaƙi.”
Then the prophet came up to the king of Israel, and said to him, Now make yourself strong, and take care what you do, or a year from now the king of Aram will come up against you again.
23 Ana cikin haka, shugabannin sarkin Aram suka ba shi shawara, “Allolinsu, allolin tuddai ne. Shi ya sa suka fi mu ƙarfi. Amma in mun yaƙe su a fili, tabbatacce za mu fi su ƙarfi.
Then the king of Aram's servants said to him, Their god is a god of the hills; that is why they were stronger than we: but if we make an attack on them in the lowlands, we will certainly be stronger than they.
24 Ka yi wannan. Ka cire dukan sarakuna daga matsayinsu ka sa waɗansu shugabanni a maimakonsu.
This is what you have to do: take away the kings from their positions, and put captains in their places;
25 Dole kuma ka tā da waɗansu mayaƙa kamar waɗanda ka rasa, doki don doki, keken yaƙi kuma don keken yaƙi, saboda mu iya yaƙe Isra’ila a fili. Ta haka tabbatacce za mu fi ƙarfinsu.” Sai ya yarda da su, ya kuma yi haka.
And get together another army like the one which came to destruction, horse for horse, and carriage for carriage; and let us make war on them in the lowlands, and certainly we will be stronger than they. And he gave ear to what they said, and did so.
26 Bazara na biye Ben-Hadad ya tattara Arameyawa, ya haura zuwa Afek don yă yaƙi Isra’ila.
So, a year later, Ben-hadad got the Aramaeans together and went up to Aphek to make war on Israel.
27 Sa’ad da aka tattara Isra’ilawa, aka kuma ba su guzuri, sai suka taka suka fita don su sadu da Arameyawa. Isra’ilawa suka kafa sansani ɗaura da su kamar ƙananan garkuna biyu na awaki, yayinda Arameyawa suka rufe dukan jejin.
And the children of Israel got themselves together, and food was made ready and they went against them; the tents of the children of Israel were like two little flocks of goats before them, but all the country was full of the Aramaeans.
28 Sai mutumin Allah ya zo ya ce wa sarkin Isra’ila, “Ga abin da Ubangiji ya ce, ‘Domin Arameyawa suna tsammani Ubangiji allahn tuddai ne, ba allahn kwari ba, zan ba da wannan ɗumbun mayaƙa a hannuwanka, za ka kuwa sani ni ne Ubangiji.’”
And a man of God came up and said to the king of Israel, The Lord says, Because the Aramaeans have said, The Lord is a god of the hills and not of the valleys; I will give all this great army into your hands, and you will see that I am the Lord.
29 Kwana bakwai suka yi sansani ɗaura da juna, a rana ta bakwai sai yaƙi ya haɗu. Isra’ilawa suka kashe sojojin kafa na Arameyawa dubu ɗari a rana ɗaya.
Now the two armies kept their positions facing one another for seven days. And on the seventh day the fight was started; and the children of Israel put to the sword a hundred thousand Aramaean footmen in one day.
30 Sauransu suka tsere zuwa birnin Afek, inda katangar ya fāɗa a kan mutum dubu ashirin da bakwai. Sai Ben-Hadad ya gudu zuwa birni ya ɓuya a ciki cikin ɗaki.
But the rest went in flight to Aphek, into the town, where a wall came down on the twenty-seven thousand who were still living. And Ben-hadad went in flight into the town, into an inner room.
31 Fadawansa suka je suka ce masa, “Mun ji an ce sarakunan Isra’ila masu jinƙai ne, bari mu sa tufafin makoki, mu ɗaura igiyoyi a wuyanmu, sa’an nan mu tafi wurin sarkin Isra’ila, wataƙila zai bar ka da rai.”
Then his servants said to him, It is said that the kings of Israel are full of mercy: let us then put on haircloth, and cords on our heads, and go to the king of Israel; it may be that he will give you your life.
32 Saye da tufafin makoki kewaye a gindinsu, da kuma igiyoyi kewaye da kawunansu, suka tafi wurin sarkin Isra’ila, suka ce, “Bawanka Ben-Hadad ya ce, ‘Ina roƙonka bari in rayu.’” Sarki ya amsa, “Har yanzu yana da rai? Shi ɗan’uwana ne.”
So they put on haircloth, and cords on their heads, and came to the king of Israel and said, Your servant Ben-hadad says, Let me now keep my life. And he said, Is he still living? he is my brother.
33 Da ma abin da fadawan suke so su ji ke nan, sai suka yi sauri, suka karɓi maganar a bakinsa, suka ce, “I, ɗan’uwanka, Ben-hadad!” Sarki ya ce, “Ku je ku kawo shi.” Da Ben-Hadad ya fita, sai Ahab ya sa aka kawo shi cikin keken yaƙinsa.
Now the men took it as a sign, and quickly took up his words; and they said, Ben-hadad is your brother. Then he said, Go and get him. So Ben-hadad came out to him and he made him get up into his carriage.
34 Ben-Hadad ya ce, “Zan mayar da biranen mahaifinka da na ƙwace daga mahaifinka. Za ka iya sa wurin kasuwarka a cikin Damaskus, kamar yadda mahaifinka ya yi a Samariya.” Ahab ya ce, “Bisa wannan yarjejjeniya zan sake ka.” Saboda haka ya yi yarjejjeniya da shi, sai ya bar shi ya tafi.
And Ben-hadad said to him, The towns my father took from your father I will give back; and you may make streets for yourself in Damascus as my father did in Samaria. And as for me, at the price of this agreement you will let me go. So he made an agreement with him and let him go.
35 Ta wurin maganar Ubangiji, ɗaya daga cikin’ya’ya maza na annabawa ya ce wa abokinsa, “Ka buge ni da makaminka,” amma mutumin ya ƙi.
And a certain man of the sons of the prophets said to his neighbour by the word of the Lord, Give me a wound. But the man would not.
36 Sai annabin ya ce, “Domin ba ka yi biyayya da Ubangiji ba, da zarar ka bar ni zaki zai kashe ka.” Daga baya mutumin ya tafi, zaki ya same shi, ya kuma kashe shi.
Then he said to him, Because you have not given ear to the voice of the Lord, straight away when you have gone from me a lion will put you to death. And when he had gone, straight away a lion came rushing at him and put him to death.
37 Annabin ya sami wani mutum ya ce, “Ka buge ni, ina roƙonka.” Sai mutumin ya buge shi, ya ji masa ciwo.
Then he came across another man, and said, Give me a wound. And the man gave him a blow wounding him.
38 Sa’an nan annabin ya tafi ya tsaya a bakin hanya yana jiran sarki. Ya ɓad da kamanni da ƙyalle a kansa. Ƙyallen ya sauka zuwa bisa idanunsa.
So the prophet went away, and pulling his head-band over his eyes to keep his face covered, took his place by the road waiting for the king.
39 Yayinda sarki yake wucewa, sai annabin ya yi kira da ƙarfi gare shi ya ce “Ni bawanka na tafi yaƙi, sai ga wani ya kawo mini wani mutum, ya ce, ‘Ka riƙe wannan mutum, kada ka bar shi yă kuɓuta ko da ƙaƙa, idan ka bari ya kuɓuta, a bakin ranka, ko kuwa ka biya talanti ɗaya na azurfa.’
And when the king went by, crying out to him he said, Your servant went out into the fight; and a man came out to me with another man and said, Keep this man: if by any chance he gets away, your life will be the price of his life, or you will have to give a talent of silver in payment.
40 Yayinda bawanka yana fama, yana kai da kawowa, sai mutumin ya ɓace.” Sai sarkin Isra’ila ya ce, “Hukuncinka ke nan, ka furta shi da kanka.”
But while your servant was turning this way and that, he was gone. Then the king of Israel said to him, You are responsible; you have given the decision against yourself.
41 Sai annabin ya cire ƙyallen da sauri daga kansa, da ya rufe idanunsa, sarkin Isra’ila kuwa ya gane shi a matsayi ɗaya daga cikin annabawa.
Then he quickly took the head-band from his eyes; and the king of Israel saw that he was one of the prophets.
42 Sai ya ce wa sarki, “Ga abin da Ubangiji ya ce, ‘Ka saki mutumin da na ƙudura yă mutu. Saboda haka ranka zai zama a maimakon ransa, mutanenka a maimakon mutanensa.’”
And he said to him, These are the words of the Lord: Because you have let go from your hands the man whom I had put to the curse, your life will be taken for his life, and your people for his people.
43 Cike da fushi, sarkin Isra’ila ya tafi fadarsa a Samariya.
Then the king of Israel went back to his house, bitter and angry, and came to Samaria.

< 1 Sarakuna 20 >