< 1 Sarakuna 2 >
1 Da lokacin mutuwar Dawuda ya yi kusa, sai ya gargaɗe Solomon ɗansa, ya ce,
Davut'un ölümü yaklaşınca, oğlu Süleyman'a şunları söyledi:
2 “Ina gab da bin hanyar da kowa a duniya zai bi. Saboda haka ka yi ƙarfin hali, ka nuna kanka namiji,
“Herkes gibi ben de yakında bu dünyadan ayrılacağım. Güçlü ve kararlı ol.
3 ka kiyaye abin da Ubangiji Allahnka yake bukata. Yi tafiya a hanyoyinsa, ka kiyaye ƙa’idodi, da umarnai, da dokoki, da kuma farillansa, kamar yadda suke a rubuce a Dokar Musa, don ka yi nasara a cikin kome da za ka yi, da kuma inda za ka tafi.
Tanrın RAB'bin verdiği görevleri yerine getir. Onun yollarında yürü ve Musa'nın yasasında yazıldığı gibi Tanrı'nın kurallarına, buyruklarına, ilkelerine ve öğütlerine uy ki, yaptığın her şeyde ve gittiğin her yerde başarılı olasın.
4 Ubangiji kuwa zai kiyaye alkawarinsa gare ni da ya ce, ‘In zuriyarka suka lura da yadda suke rayuwa, in kuma suka yi tafiya da aminci a gabana da dukan zuciyarsu, da kuma dukan ransu, ba za ka kāsa samun mutum a kujerar sarautar Isra’ila ba.’
O zaman RAB bana verdiği şu sözü yerine getirecektir: ‘Eğer soyun nasıl yaşadığına dikkat eder, candan ve yürekten bana bağlı kalarak yollarımda yürürse, İsrail tahtından senin soyunun ardı arkası kesilmeyecektir.’
5 “Yanzu fa, kai kanka ka san abin da Yowab ɗan Zeruhiya ya yi mini. Abin da ya yi wa shugabanni biyun nan na mayaƙan Isra’ila, wato, Abner ɗan Ner, da Amasa ɗan Yeter. Ya kashe su, ya kuma zub da jininsu a lokacin salama sai ka ce a fage yaƙi, da wannan jini ya yi ɗamara a gindinsa, ya kuma sa takalma a ƙafafunsa.
“Seruya oğlu Yoav'ın bana ve İsrail ordusunun iki komutanı Ner oğlu Avner'le Yeter oğlu Amasa'ya neler yaptığını biliyorsun. Sanki savaş varmış gibi onları öldürerek barış döneminde kan döktü. Belindeki kemerle ayağındaki çarıklara kan bulaştırdı.
6 Ka yi da shi gwargwadon hikimarka, amma kada ka bari yă gangara kabari da furfura cikin salama. (Sheol )
Sen aklına uyanı yap, ama onun ak saçlı başının esenlik içinde ölüler diyarına gitmesine izin verme. (Sheol )
7 “Amma ka yi alheri ga’ya’yan Barzillai mutumin Gileyad, ka sa su kasance a cikin waɗanda suke ci a teburinka. Sun goyi bayana sa’ad da nake gudu daga ɗan’uwanka Absalom.
“Gilatlı Barzillay'ın oğullarına iyi davran, sofranda yemek yiyenlerin arasında onlara da yer ver. Çünkü ben ağabeyin Avşalom'un önünden kaçtığım zaman onlar bana yardım etmişlerdi.
8 “Ka tuna, akwai kuma Shimeyi ɗan Gera, mutumin Benyamin daga Bahurim, wanda ya yi ta yin mini muguwar la’ana a ranar da na tafi Mahanayim. Sa’ad da ya gangara ya same ni a Urdun, na rantse masa da sunan Ubangiji na ce, ‘Ba zan kashe ka da takobi ba.’
“Mahanayim'e gittiğim gün beni çok ağır biçimde lanetleyen Benyamin oymağından Bahurimli Gera'nın oğlu Şimi de yanında. Beni Şeria Irmağı kıyısında karşılamaya geldiğinde, ‘Seni kılıçla öldürmeyeceğim’ diye RAB'bin adıyla ona ant içmiştim.
9 Amma yanzu, kada ka ɗauke shi marar laifi. Kai mutum ne mai hikima; za ka san abin da za ka yi da shi. Ka kawo furfuransa zuwa kabari da jini.” (Sheol )
Ama sen sakın onu cezasız bırakma. Ona ne yapacağını bilecek kadar akıllısın. Onun ak saçlı başını ölüler diyarına kanlar içinde gönder.” (Sheol )
10 Sa’an nan Dawuda ya huta tare da kakanninsa. Sai aka binne shi a Birnin Dawuda.
Davut ölüp atalarına kavuşunca, kendi adıyla bilinen kentte gömüldü.
11 Ya yi sarauta shekaru arba’in a bisa Isra’ila. Wato, shekaru bakwai a Hebron da kuma talatin da uku a Urushalima.
Yedi yıl Hevron'da, otuz üç yıl Yeruşalim'de olmak üzere toplam kırk yıl İsrail'de krallık yaptı.
12 Solomon kuwa ya zauna a kan kujerar sarautar mahaifinsa Dawuda, mulkinsa kuwa ya kahu sosai.
Babası Davut'un tahtına geçen Süleyman'ın krallığı çok sağlam temellere oturmuştu.
13 To, sai Adoniya, ɗan Haggit ya tafi wurin Batsheba mahaifiyar Solomon. Ita kuwa ta tambaye shi ta ce, “Lafiya?” Ya amsa ya ce, “I, lafiya.”
Hagit oğlu Adoniya, Süleyman'ın annesi Bat-Şeva'nın yanına gitti. Bat-Şeva ona, “Dostça mı geldin?” diye sordu. Adoniya, “Dostça” diye karşılık verdi.
14 Sa’an nan ya ƙara da cewa, “Ina da ɗan wani abin da zan faɗa miki.” Ta ce, “Faɗa.”
Ve ekledi: “Sana söyleyeceklerim var.” Bat-Şeva, “Söyle!” dedi.
15 Sai ya ce, “Kamar yadda kika sani, mulkin nan nawa ne. Dukan Isra’ila suna ɗaukana a matsayin sarki. Amma abubuwa suka canja, sai mulkin ya koma ga ɗan’uwana; gama ya zo masa daga Ubangiji ne.
Adoniya, “Bildiğin gibi, daha önce krallık benim elimdeydi” dedi, “Bütün İsrail benim kral olmamı bekliyordu. Ancak her şey değişti ve krallık kardeşimin eline geçti. Çünkü RAB'bin isteği buydu.
16 Yanzu ina da roƙo guda da zan yi gare ki. Kada ki hana mini.” Ta ce, “Sai ka faɗa.”
Ama benim senden bir dileğim var. Lütfen geri çevirme.” Bat-Şeva, “Söyle!” dedi.
17 Sai ya ci gaba, “In kin yarda, ki yi magana da Sarki Solomon, gama ba zai ƙi jinki ba, ki ce yă ba ni yarinyan nan, Abishag, mutuniyar Shunam, tă zama matata.”
Adoniya, “Kral Süleyman seni kırmaz” dedi, “Lütfen ona söyle, Şunemli Avişak'ı bana eş olarak versin.”
18 Batsheba ta ce, “Da kyau, zan yi magana da sarki dominka.”
Bat-Şeva, “Peki, senin için kralla konuşacağım” diye karşılık verdi.
19 Sai Batsheba ta tafi wurin Sarki Solomon don tă yi masa magana a kan Adoniya. Sarki ya miƙe tsaye don yă sadu da ita, ya rusuna mata, ya kuma zauna a kujerar sarautarsa. Ya sa aka kawo wa mahaifiyar sarki kujerar sarauta, ta kuwa zauna a gefen damansa.
Bat-Şeva, Adoniya'nın dileğini iletmek üzere Kral Süleyman'ın yanına gitti. Süleyman annesini karşılamak için ayağa kalkıp önünde eğildikten sonra tahtına oturdu. Annesi için de sağ tarafına bir taht koydurdu.
20 Ta ce, “Ina da ɗan roƙon da zan nema ka yi mini. Ina fata ba za ka hana ni ba.” Sai sarki ya amsa ya ce, “Mahaifiyata, sai ki faɗa in ji, ba zan hana miki ba.”
Tahtına oturan annesi, “Senden küçük bir dileğim var, lütfen beni boş çevirme” dedi. Kral, “Söyle anne, seni kırmam” diye karşılık verdi.
21 Saboda haka sai ta ce, “Ka sa a ba wa ɗan’uwanka Adoniya, Abishag mutuniyar Shunam tă zama matarsa.”
Bat-Şeva, “Şunemli Avişak ağabeyin Adoniya'ya eş olarak verilsin” dedi.
22 Sarki Solomon ya amsa wa mahaifiyarsa ya ce, “Me ya sa kika roƙar wa Adoniya Abishag mutuniyar Shunam kawai? Ki ma sa a ba shi mulkin mana. Ai, shi yayana ne. I, ki roƙa dominsa, da domin Abiyatar firist, da kuma domin Yowab ɗan Zeruhiya mana!”
Kral Süleyman, “Neden Şunemli Avişak'ın Adoniya'ya verilmesini istiyorsun?” dedi, “Krallığı da ona vermemi iste bari! Ne de olsa o benim büyüğüm. Üstelik Kâhin Aviyatar'la Seruya oğlu Yoav da ondan yana.”
23 Sai Sarki Solomon ya rantse da sunan Ubangiji ya ce, “Bari Allah yă yi mini hukunci mai tsanani, idan ban sa Adoniya ya biya wannan roƙo da ransa ba!
Bu olay üzerine Kral Süleyman RAB'bin adıyla ant içti: “Eğer Adoniya bu dileğini hayatıyla ödemezse, Tanrı bana aynısını, hatta daha kötüsünü yapsın!
24 Yanzu kuwa, muddin Ubangiji yana a raye, shi wanda ya kafa ni sosai a kan kujerar sarautar mahaifina Dawuda, ya kuma kafa mini mulki kamar yadda ya yi alkawari; za a kashe Adoniya yau!”
Beni güçlendirip babam Davut'un tahtına oturtan, verdiği sözü tutup bana bir hanedan kuran, yaşayan RAB'bin adıyla ant içerim ki, Adoniya bugün öldürülecek!”
25 Saboda haka Sarki Solomon ya umarci Benahiya ɗan Yehohiyada yă kashe Adoniya; ya kuwa kashe shi.
Böylece Kral Süleyman Yehoyada oğlu Benaya'yı Adoniya'yı öldürmekle görevlendirdi. Benaya da gidip Adoniya'yı öldürdü.
26 Ga Abiyatar firist kuwa sarki ya ce, “Tafi gonarka a Anatot. Ka cancanci ka mutu, amma ba zan kashe ka yanzu ba, domin ka ɗauki akwatin alkawarin Ubangiji Mai Iko Duka a gaban mahaifina Dawuda, ka kuma sha wahala tare mahaifina.”
Kral, Kâhin Aviyatar'a, “Anatot'taki tarlana dön” dedi, “Aslında ölümü hak ettin. Ama seni şimdi öldürmeyeceğim. Çünkü sen babam Davut'un önünde Egemen RAB'bin Antlaşma Sandığı'nı taşıdın ve babamın çektiği bütün sıkıntıları onunla paylaştın.”
27 Saboda haka Solomon ya cire Abiyatar daga aikin firist na Ubangiji, ya cika maganar da Ubangiji ya yi a Shilo game da gidan Eli.
Eli'nin ailesi hakkında RAB'bin Şilo'da söylediği sözün gerçekleşmesi için, Süleyman Aviyatar'ı RAB'bin kâhinliğinden uzaklaştırdı.
28 Sa’ad da labarin ya kai wurin Yowab, wanda ya haɗa kai da Adoniya, ko da yake bai haɗa kai da Absalom ba, sai ya gudu zuwa tentin Ubangiji, ya kama ƙahonin bagade ya riƙe.
Haber Yoav'a ulaştı. Yoav daha önce ayaklanan Avşalom'u desteklemediği halde Adoniya'yı destekledi. Bu nedenle RAB'bin Çadırı'na kaçtı ve sunağın boynuzlarına sarıldı.
29 Aka faɗa wa Sarki Solomon cewa Yowab ya gudu zuwa tentin Ubangiji, yana kuma kusa da bagade. Sai Solomon ya umarci Benahiya ɗan Yehohiyada ya ce, “Je ka kashe shi!”
Yoav'ın RAB'bin Çadırı'na kaçıp sunağın yanında olduğu Kral Süleyman'a bildirildi. Süleyman, Yehoyada oğlu Benaya'ya, “Git, onu vur!” diye buyruk verdi.
30 Sai Benahiya ya shiga tentin Ubangiji ya ce wa Yowab, “Sarki ya ce, ‘Ka fita!’” Amma Yowab ya amsa ya ce, “A’a, a nan zan mutu.” Sai Benahiya ya ce wa sarki, “Ga yadda Yowab ya amsa mini.”
Benaya RAB'bin Çadırı'na gitti ve Yoav'a, “Kral dışarı çıkmanı buyuruyor!” dedi. Yoav, “Hayır, burada ölmek istiyorum” karşılığını verdi. Benaya gidip Yoav'ın kendisini nasıl yanıtladığını krala bildirdi.
31 Sai sarki ya umarci Benahiya ya ce, “Yi kamar yadda ya faɗa. Ka kashe shi, ka kuma binne shi, ka wanke ni da gidan mahaifina daga laifin jini marasa laifin da Yowab ya zubar.
Kral, “Onun istediği gibi yap” dedi, “Onu orada öldür ve göm. Yoav'ın boş yere döktüğü kanın sorumluluğunu benim ve babamın soyu üstünden kaldırmış olursun.
32 Ubangiji zai sāka masa saboda jinin da ya zubar, domin ba da sanin mahaifina Dawuda ne ya fāɗa wa mutum biyun nan da takobi ba. Dukansu biyu, Abner ɗan Ner, shugaban mayaƙan Isra’ila, da Amasa ɗan Yeter, shugaban mayaƙan Yahuda, mutane ne mafi kyau da kuma mafi adalci fiye da shi.
RAB döktüğü kandan ötürü onu cezalandıracaktır. Çünkü Yoav babam Davut'un bilgisi dışında, kendisinden daha iyi ve doğru olan iki kişiyi –İsrail ordusunun komutanı Ner oğlu Avner'le Yahuda ordusunun komutanı Yeter oğlu Amasa'yı– kılıçla öldürdü.
33 Bari alhakin jininsu yă koma a kan Yowab da kuma zuriyarsa har abada. Amma bari salamar Ubangiji tă kasance a kan Dawuda da zuriyarsa, da gidansa, da kuma mulkinsa, har abada.”
Böylece dökülen kanlarının sorumluluğu sonsuza dek Yoav'ın ve soyunun üstünde kalacaktır. Ama RAB, Davut'a, soyuna, ailesine ve tahtına sonsuza dek esenlik verecektir.”
34 Sai Benahiya ɗan Yehohiyada ya haura ya bugi Yowab, ya kashe shi, ya kuwa binne shi a gidansa a ƙauye.
Yehoyada oğlu Benaya gidip Yoav'ı öldürdü. Onu ıssız bir bölgede bulunan kendi evine gömdüler.
35 Sai sarki ya sa Benahiya ɗan Yehohiyada ya zama shugaba a bisa mayaƙa a matsayin Yowab, ya kuma sa Zadok firist a wurin Abiyatar.
Kral, Yoav'ın yerine Yehoyada oğlu Benaya'yı ordu komutanı yaptı. Aviyatar'ın yerine de Kâhin Sadok'u atadı.
36 Sa’an nan sarki ya aika aka kawo Shimeyi, ya kuma ce masa, “Ka gina wa kanka gida a nan a Urushalima, ka zauna a ciki, kada ka kuskura ka tafi wani wuri.
Sonra kral haber gönderip Şimi'yi çağırttı. Ona, “Yeruşalim'de kendine bir ev yap ve orada otur” dedi, “Hiçbir yere gitme.
37 Gama ran da ka fita, ka haye Kwarin Kidron, ka tabbata za ka mutu, alhakin jininka kuwa zai koma kanka.”
Oradan ayrılıp Kidron Vadisi'nden öteye geçtiğin gün bil ki öleceksin. Sorumluluk sana ait.”
38 Shimeyi ya amsa wa sarki ya ce, “Abin da ka faɗa yana da kyau. Bawanka zai yi kamar yadda ranka yă daɗe sarki, ya faɗa.” Shimeyi kuwa ya yi zama a Urushalima na dogon lokaci.
Şimi krala, “Efendim kral, peki” diye karşılık verdi, “Kulun olarak söylediklerini aynen yapacağım.” Şimi Yeruşalim'de uzun süre yaşadı.
39 Amma bayan shekaru uku, biyu daga cikin bayin Shimeyi suka gudu zuwa wurin Akish ɗan Ma’aka, sarkin Gat. Aka faɗa wa Shimeyi cewa, “Bayinka suna a Gat.”
Aradan üç yıl geçmişti, Şimi'nin iki kölesi Gat Kralı Maaka oğlu Akiş'in yanına kaçtı. Kölelerin Gat'a kaçtığını Şimi'ye haber verdiler.
40 Da jin haka, sai ya tashi ya shimfiɗa wa jakinsa abin zama, ya hau, ya tafi Gat wurin Akish domin neman bayinsa. Shimeyi kuwa ya dawo da su gida daga Gat.
Bunun üzerine Şimi kalkıp eşeğine palan vurdu ve kölelerini aramak üzere Gat'a Akiş'in yanına gitti. Kölelerini bulup Gat'tan geri getirdi.
41 Da aka faɗa wa Solomon cewa Shimeyi ya bar Urushalima zuwa Gat, har ya dawo.
Şimi'nin Yeruşalim'den Gat'a gidip döndüğü Süleyman'a anlatılınca,
42 Sai sarki ya aika a kawo Shimeyi, ya ce masa, “Ban sa ka rantse da sunan Ubangiji, na kuma ja maka kunne cewa, ‘A ranar da ka kuskura ka bar nan ka tafi wani wuri, ka tabbata za ka mutu ba’? A lokacin ka ce mini, ‘Abin da ka faɗa yana da kyau. Zan kuwa kiyaye.’
Süleyman Şimi'yi çağırttı. “Sana RAB'bin adıyla ant içirmedim mi?” dedi, “‘Kalkıp herhangi bir yere gittiğin gün öleceğini bil!’ diye seni uyarmadım mı? Sen de bana: ‘Peki, sözünü dinleyeceğim’ demedin mi?
43 To, me ya sa ba ka kiyaye rantsuwar da ka yi ga Ubangiji, ka kuma yi biyayya da umarnin da na ba ka ba?”
Öyleyse neden RAB'bin adına içtiğin anda ve buyruğuma uymadın?”
44 Sarki ya ce wa Shimeyi, “Ka sani a zuciyarka dukan muguntar da ka yi wa mahaifina Dawuda. Yanzu Ubangiji zai sāka maka saboda muguntarka.
Kral, Şimi'ye karşı sözlerini şöyle sürdürdü: “Babam Davut'a yaptığın bütün kötülükleri çok iyi biliyorsun. Bu yaptıklarından dolayı RAB seni cezalandıracak.
45 Amma za a yi wa Sarki Solomon albarka, sarautar Dawuda kuma za tă kasance a tsare a gaban Ubangiji har abada.”
Ama Kral Süleyman kutsanacak ve Davut'un tahtı RAB'bin önünde sonsuza dek kurulu kalacaktır.”
46 Sai sarki ya umarci Benahiya ɗan Yehohiyada, yă fita, yă bugi Shimeyi, yă kashe shi. Ya kuwa kashe shi. Mulki kuwa ya kahu sosai a hannun Solomon.
Kral, Yehoyada oğlu Benaya'ya buyruk verdi. O da gidip Şimi'yi öldürdü. Böylece Süleyman'ın krallığı iyice pekişti.