< 1 Sarakuna 2 >

1 Da lokacin mutuwar Dawuda ya yi kusa, sai ya gargaɗe Solomon ɗansa, ya ce,
Kad nu Dāvidam laiks atnāca mirt, tad viņš pavēlēja savam dēlam Salamanam un sacīja:
2 “Ina gab da bin hanyar da kowa a duniya zai bi. Saboda haka ka yi ƙarfin hali, ka nuna kanka namiji,
Es eju visas pasaules ceļu. Tāpēc ņemies drošu prātu un turies kā vīrs.
3 ka kiyaye abin da Ubangiji Allahnka yake bukata. Yi tafiya a hanyoyinsa, ka kiyaye ƙa’idodi, da umarnai, da dokoki, da kuma farillansa, kamar yadda suke a rubuce a Dokar Musa, don ka yi nasara a cikin kome da za ka yi, da kuma inda za ka tafi.
Un sargi, kas jāsargā Tam Kungam, tavam Dievam, staigādams Viņa ceļos, turēdams Viņa likumus, Viņa baušļus un Viņa tiesas un Viņa liecības, tā kā Mozus bauslībā ir rakstīts, ka tu prātīgi turies iekš visa, ko tu dari, un visur, kurp tu griezies.
4 Ubangiji kuwa zai kiyaye alkawarinsa gare ni da ya ce, ‘In zuriyarka suka lura da yadda suke rayuwa, in kuma suka yi tafiya da aminci a gabana da dukan zuciyarsu, da kuma dukan ransu, ba za ka kāsa samun mutum a kujerar sarautar Isra’ila ba.’
Lai Tas Kungs Savu vārdu apstiprina, ko Tas uz mani runājis, sacīdams: ja tavi dēli savu ceļu sargās, staigādami priekš Mana vaiga uzticīgi ar visu savu sirdi un ar visu savu dvēseli, tad, Viņš sacīja, tev netrūks vīra, kas sēdēs uz Israēla goda krēsla.
5 “Yanzu fa, kai kanka ka san abin da Yowab ɗan Zeruhiya ya yi mini. Abin da ya yi wa shugabanni biyun nan na mayaƙan Isra’ila, wato, Abner ɗan Ner, da Amasa ɗan Yeter. Ya kashe su, ya kuma zub da jininsu a lokacin salama sai ka ce a fage yaƙi, da wannan jini ya yi ɗamara a gindinsa, ya kuma sa takalma a ƙafafunsa.
Tu arī gan zini, ko Joabs, Cerujas dēls, man ir darījis, un ko viņš darījis Israēla kara virsniekiem, Abneram, Nera dēlam, un Amasum, Jetera dēlam, ka viņš tos nokāvis, un kara asinis izlējis miera laikā un kara asinis licis pie savas jostas, kas ap viņa gurniem, un pie savām kurpēm, kas pie viņa kājām
6 Ka yi da shi gwargwadon hikimarka, amma kada ka bari yă gangara kabari da furfura cikin salama. (Sheol h7585)
Tāpēc dari pēc savas gudrības, ka tu viņa sirmiem matiem nelieci ar mieru nākt kapā. (Sheol h7585)
7 “Amma ka yi alheri ga’ya’yan Barzillai mutumin Gileyad, ka sa su kasance a cikin waɗanda suke ci a teburinka. Sun goyi bayana sa’ad da nake gudu daga ɗan’uwanka Absalom.
Bet Barzilajus, tā Gileādieša, dēliem, tev būs labu darīt, ka tie ir starp tiem, kas ēd pie tava galda, jo tā tie turējās pie manis, kad es bēgu priekš tava brāļa Absaloma.
8 “Ka tuna, akwai kuma Shimeyi ɗan Gera, mutumin Benyamin daga Bahurim, wanda ya yi ta yin mini muguwar la’ana a ranar da na tafi Mahanayim. Sa’ad da ya gangara ya same ni a Urdun, na rantse masa da sunan Ubangiji na ce, ‘Ba zan kashe ka da takobi ba.’
Un redzi, pie tevis ir Šimejus, Ģera dēls, tas Benjaminiets no Bakurim, kas mani lādēja ar briesmīgu lādēšanu tai dienā, kad es uz Mahānaīm gāju. Bet viņš man nonāca pretī pie Jardānes, un es viņam pie Tā Kunga esmu zvērējis, sacīdams; es tevi ar zobenu nekaušu.
9 Amma yanzu, kada ka ɗauke shi marar laifi. Kai mutum ne mai hikima; za ka san abin da za ka yi da shi. Ka kawo furfuransa zuwa kabari da jini.” (Sheol h7585)
Bet tu neturi viņu par nenoziedzīgu, jo tu esi gudrs vīrs un gan zināsi, ko tev viņam būs darīt, ka tu viņa sirmiem matiem ar asinīm lieci nākt bedrē. (Sheol h7585)
10 Sa’an nan Dawuda ya huta tare da kakanninsa. Sai aka binne shi a Birnin Dawuda.
Tā Dāvids gāja dusēt pie saviem tēviem un tapa aprakts Dāvida pilsētā.
11 Ya yi sarauta shekaru arba’in a bisa Isra’ila. Wato, shekaru bakwai a Hebron da kuma talatin da uku a Urushalima.
Un tas laiks, kamēr Dāvids ķēniņš bijis pār Israēli, ir četrdesmit gadi; septiņus gadus viņš bija valdījis Hebronē un trīsdesmit un trīs gadus Jeruzālemē.
12 Solomon kuwa ya zauna a kan kujerar sarautar mahaifinsa Dawuda, mulkinsa kuwa ya kahu sosai.
Un Salamans sēdēja uz sava tēva Dāvida goda krēsla, un viņa valstība tapa varen stiprināta.
13 To, sai Adoniya, ɗan Haggit ya tafi wurin Batsheba mahaifiyar Solomon. Ita kuwa ta tambaye shi ta ce, “Lafiya?” Ya amsa ya ce, “I, lafiya.”
Un Adonija, Aģitas dēls, nāca pie Batsebas, Salamana mātes; un tā sacīja: vai tu nāc ar mieru? Un viņš sacīja: ar mieru.
14 Sa’an nan ya ƙara da cewa, “Ina da ɗan wani abin da zan faɗa miki.” Ta ce, “Faɗa.”
Un viņš sacīja: man ar tevi kas jārunā. Un viņa sacīja: runā.
15 Sai ya ce, “Kamar yadda kika sani, mulkin nan nawa ne. Dukan Isra’ila suna ɗaukana a matsayin sarki. Amma abubuwa suka canja, sai mulkin ya koma ga ɗan’uwana; gama ya zo masa daga Ubangiji ne.
Tad viņš sacīja: tu zini, ka man tā valstība piederēja, un visas Israēla acis uz mani skatījās, ka man bija ķēniņam būt; bet nu tā valstība ir novērsta un manam brālim tikusi, jo no Tā Kunga tā viņam ir tikusi.
16 Yanzu ina da roƙo guda da zan yi gare ki. Kada ki hana mini.” Ta ce, “Sai ka faɗa.”
Bet nu es no tevis lūdzu vienu vienīgu lūgšanu, - neapkauno manu vaigu!
17 Sai ya ci gaba, “In kin yarda, ki yi magana da Sarki Solomon, gama ba zai ƙi jinki ba, ki ce yă ba ni yarinyan nan, Abishag, mutuniyar Shunam, tă zama matata.”
Un viņa uz to sacīja: runā. Tad viņš sacīja: runā jel ar ķēniņu Salamanu, jo viņš tavu vaigu neliks kaunā, ka viņš man Abizagu no Šunemes dod par sievu.
18 Batsheba ta ce, “Da kyau, zan yi magana da sarki dominka.”
Un Batseba sacīja: labi, es tevis pēc ar ķēniņu runāšu.
19 Sai Batsheba ta tafi wurin Sarki Solomon don tă yi masa magana a kan Adoniya. Sarki ya miƙe tsaye don yă sadu da ita, ya rusuna mata, ya kuma zauna a kujerar sarautarsa. Ya sa aka kawo wa mahaifiyar sarki kujerar sarauta, ta kuwa zauna a gefen damansa.
Tā Batseba nāca pie ķēniņa Salamana, Adonijas labad ar viņu runāt. Un ķēniņš cēlās viņai pretī un paklanījās priekš tās; un viņš apsēdās uz sava goda krēsla un deva ķēniņa mātei arī krēslu, un tā sēdēja pa viņa labo roku.
20 Ta ce, “Ina da ɗan roƙon da zan nema ka yi mini. Ina fata ba za ka hana ni ba.” Sai sarki ya amsa ya ce, “Mahaifiyata, sai ki faɗa in ji, ba zan hana miki ba.”
Un viņa sacīja: es lūdzos no tevis vienu mazu lūgšanu, - neapkauno manu vaigu. Un ķēniņš uz to sacīja: lūdz, mana māte, es tavu vaigu neapkaunošu.
21 Saboda haka sai ta ce, “Ka sa a ba wa ɗan’uwanka Adoniya, Abishag mutuniyar Shunam tă zama matarsa.”
Un viņa sacīja: dod Abizagu no Šunemes savam brālim Adonijam par sievu.
22 Sarki Solomon ya amsa wa mahaifiyarsa ya ce, “Me ya sa kika roƙar wa Adoniya Abishag mutuniyar Shunam kawai? Ki ma sa a ba shi mulkin mana. Ai, shi yayana ne. I, ki roƙa dominsa, da domin Abiyatar firist, da kuma domin Yowab ɗan Zeruhiya mana!”
Tad ķēniņš Salamans atbildēja un sacīja uz savu māti: kāpēc tad tu prasi Abizagu no Šunemes priekš Adonijas? Prasi priekš viņa arī to valstību, jo viņš ir mans brālis, vecāks nekā es, priekš viņa un Abjatara, tā priestera, un Joaba, Cerujas dēla!
23 Sai Sarki Solomon ya rantse da sunan Ubangiji ya ce, “Bari Allah yă yi mini hukunci mai tsanani, idan ban sa Adoniya ya biya wannan roƙo da ransa ba!
Un ķēniņš Salamans zvērēja pie Tā Kunga un sacīja: lai man Dievs šā un tā dara, tiešām, Adonija šo vārdu būs runājis pret savu dzīvību.
24 Yanzu kuwa, muddin Ubangiji yana a raye, shi wanda ya kafa ni sosai a kan kujerar sarautar mahaifina Dawuda, ya kuma kafa mini mulki kamar yadda ya yi alkawari; za a kashe Adoniya yau!”
Un nu, tik tiešām kā Tas Kungs dzīvo, kas mani apstiprinājis un mani sēdinājis uz mana tēva Dāvida goda krēslu, un kas man ir namu cēlis, itin kā viņš runājis, tiešām, Adonija šodien taps nokauts.
25 Saboda haka Sarki Solomon ya umarci Benahiya ɗan Yehohiyada yă kashe Adoniya; ya kuwa kashe shi.
Un ķēniņš Salamans nosūtīja pavēli Benajam, Jojadas dēlam; šis to nokāva, un tas nomira.
26 Ga Abiyatar firist kuwa sarki ya ce, “Tafi gonarka a Anatot. Ka cancanci ka mutu, amma ba zan kashe ka yanzu ba, domin ka ɗauki akwatin alkawarin Ubangiji Mai Iko Duka a gaban mahaifina Dawuda, ka kuma sha wahala tare mahaifina.”
Un uz priesteri Abjataru ķēniņš sacīja: ej uz Anatotu, uz savu tīrumu, jo tu esi nāvi pelnījis. Bet es tevi šodien nenokaušu, tāpēc ka tu Tā Kunga Dieva šķirstu nesis mana tēva Dāvida priekšā, un ka tu līdz panesis visu, ko mans tēvs panesis.
27 Saboda haka Solomon ya cire Abiyatar daga aikin firist na Ubangiji, ya cika maganar da Ubangiji ya yi a Shilo game da gidan Eli.
Tā Salamans izdzina Abjataru, ka tas Tam Kungam vairs nebija par priesteri, lai piepildītos Tā Kunga vārds, ko viņš par Elus namu Šīlo bija runājis.
28 Sa’ad da labarin ya kai wurin Yowab, wanda ya haɗa kai da Adoniya, ko da yake bai haɗa kai da Absalom ba, sai ya gudu zuwa tentin Ubangiji, ya kama ƙahonin bagade ya riƙe.
Kad nu šī vēsts pie Joaba nāca (jo Joabs bija turējies pie Adonijas, jebšu nebija turējies pie Absaloma), tad Joabs bēga Tā Kunga teltī un satvēra altāra ragus.
29 Aka faɗa wa Sarki Solomon cewa Yowab ya gudu zuwa tentin Ubangiji, yana kuma kusa da bagade. Sai Solomon ya umarci Benahiya ɗan Yehohiyada ya ce, “Je ka kashe shi!”
Un ķēniņam Salamanam tapa sacīts, ka Joabs bēdzis Tā Kunga teltī, un redzi, viņš ir pie altāra. Tad Salamans sūtīja Benaju, Jojadas dēlu, un sacīja: ej, kauj viņu.
30 Sai Benahiya ya shiga tentin Ubangiji ya ce wa Yowab, “Sarki ya ce, ‘Ka fita!’” Amma Yowab ya amsa ya ce, “A’a, a nan zan mutu.” Sai Benahiya ya ce wa sarki, “Ga yadda Yowab ya amsa mini.”
Un kad Benaja uz Tā Kunga telti nāca, tad viņš uz to sacīja: tā saka ķēniņš: ej ārā. Bet viņš sacīja: nē, bet še es gribu mirt. Tad Benaja nesa ķēniņam atbildi un sacīja: tā Joabs ir runājis un tā viņš man ir atbildējis.
31 Sai sarki ya umarci Benahiya ya ce, “Yi kamar yadda ya faɗa. Ka kashe shi, ka kuma binne shi, ka wanke ni da gidan mahaifina daga laifin jini marasa laifin da Yowab ya zubar.
Un ķēniņš uz viņu sacīja: dari tā, kā viņš ir runājis, kauj viņu un aproc viņu, ka tu no manis un no mana tēva nama atņem tās asinis, ko Joabs velti izlējis.
32 Ubangiji zai sāka masa saboda jinin da ya zubar, domin ba da sanin mahaifina Dawuda ne ya fāɗa wa mutum biyun nan da takobi ba. Dukansu biyu, Abner ɗan Ner, shugaban mayaƙan Isra’ila, da Amasa ɗan Yeter, shugaban mayaƙan Yahuda, mutane ne mafi kyau da kuma mafi adalci fiye da shi.
Un Tas Kungs lai liek viņa asinīm atkal nākt uz viņa galvu, tāpēc ka viņš ir sitis divus vīrus, kas labāki un taisnāki bija nekā viņš, un tos ir nokāvis ar zobenu, bez mana tēva Dāvida ziņas, proti Abneru, Nera dēlu, Israēla kara virsnieku, un Amasu, Jetera dēlu, Jūda kara virsnieku.
33 Bari alhakin jininsu yă koma a kan Yowab da kuma zuriyarsa har abada. Amma bari salamar Ubangiji tă kasance a kan Dawuda da zuriyarsa, da gidansa, da kuma mulkinsa, har abada.”
Viņu asinis lai atkal nāk uz Joaba galvu un uz viņa dzimuma galvu mūžīgi. Bet Dāvidam un viņa dzimumam un viņa namam un viņa goda krēslam lai ir miers no Tā Kunga mūžīgi.
34 Sai Benahiya ɗan Yehohiyada ya haura ya bugi Yowab, ya kashe shi, ya kuwa binne shi a gidansa a ƙauye.
Un Benaja, Jojadas dēls, nogāja un sita viņu un to nokāva. Un viņš tapa aprakts savā namā tuksnesī.
35 Sai sarki ya sa Benahiya ɗan Yehohiyada ya zama shugaba a bisa mayaƙa a matsayin Yowab, ya kuma sa Zadok firist a wurin Abiyatar.
Un ķēniņš iecēla Benaju, Jojadas dēlu, viņa vietā pār karaspēku, un priesteri Cadoku ķēniņš iecēla Abjatara vietā.
36 Sa’an nan sarki ya aika aka kawo Shimeyi, ya kuma ce masa, “Ka gina wa kanka gida a nan a Urushalima, ka zauna a ciki, kada ka kuskura ka tafi wani wuri.
Un ķēniņš nosūtīja un lika Šimeju aicināt, un uz to sacīja: uztaisi sev namu Jeruzālemē un dzīvo tur un neizej no turienes it nekur;
37 Gama ran da ka fita, ka haye Kwarin Kidron, ka tabbata za ka mutu, alhakin jininka kuwa zai koma kanka.”
Un notiks, kurā dienā tu iziesi un iesi pār Kidronas upi, tad zini tiešām, ka tu mirdams mirsi, - tavas asinis lai paliek uz tavas galvas.
38 Shimeyi ya amsa wa sarki ya ce, “Abin da ka faɗa yana da kyau. Bawanka zai yi kamar yadda ranka yă daɗe sarki, ya faɗa.” Shimeyi kuwa ya yi zama a Urushalima na dogon lokaci.
Tad Šimejus sacīja uz ķēniņu: tas ir labs vārds; kā mans kungs, tas ķēniņš, ir runājis, tā tavs kalps darīs. Tā Šimejus dzīvoja Jeruzālemē labu laiku.
39 Amma bayan shekaru uku, biyu daga cikin bayin Shimeyi suka gudu zuwa wurin Akish ɗan Ma’aka, sarkin Gat. Aka faɗa wa Shimeyi cewa, “Bayinka suna a Gat.”
Un notikās pēc trim gadiem, ka Šimejum divi kalpi aizbēga pie Aķisa, Maēkas dēla, Gatas ķēniņa. Un Šimejum teica un sacīja: redzi, tavi kalpi ir Gatā.
40 Da jin haka, sai ya tashi ya shimfiɗa wa jakinsa abin zama, ya hau, ya tafi Gat wurin Akish domin neman bayinsa. Shimeyi kuwa ya dawo da su gida daga Gat.
Tad Šimejus cēlās un apsegloja savu ēzeli un nogāja uz Gatu pie Aķisa, savus kalpus meklēt. Un tā Šimejus nogāja un atveda savus kalpus no Gatas.
41 Da aka faɗa wa Solomon cewa Shimeyi ya bar Urushalima zuwa Gat, har ya dawo.
Un Salamanam tapa sacīts, ka Šimejus no Jeruzālemes bija nogājis uz Gatu un atkal pārnācis.
42 Sai sarki ya aika a kawo Shimeyi, ya ce masa, “Ban sa ka rantse da sunan Ubangiji, na kuma ja maka kunne cewa, ‘A ranar da ka kuskura ka bar nan ka tafi wani wuri, ka tabbata za ka mutu ba’? A lokacin ka ce mini, ‘Abin da ka faɗa yana da kyau. Zan kuwa kiyaye.’
Tad ķēniņš sūtīja un sauca Šimeju un uz to sacīja: vai es tevi pie Tā Kunga neesmu apzvērinājis un tev piekodinājis sacīdams: kurā dienā tu iziesi un iesi šur vai tur, tad zini tiešām, ka tev jāmirst? Un tu sacīji uz mani: es esmu labu vārdu dzirdējis.
43 To, me ya sa ba ka kiyaye rantsuwar da ka yi ga Ubangiji, ka kuma yi biyayya da umarnin da na ba ka ba?”
Kāpēc tad tu neesi turējis Tā Kunga zvērestu un to pavēli, ko es tev esmu pavēlējis?
44 Sarki ya ce wa Shimeyi, “Ka sani a zuciyarka dukan muguntar da ka yi wa mahaifina Dawuda. Yanzu Ubangiji zai sāka maka saboda muguntarka.
Un ķēniņš sacīja uz Šimeju: tu zini visu to ļaunu, ko tava sirds apzinās, ko tu manam tēvam Dāvidam darījis, tāpēc Tas Kungs tavam ļaunumam atkal licis nākt uz tavu galvu.
45 Amma za a yi wa Sarki Solomon albarka, sarautar Dawuda kuma za tă kasance a tsare a gaban Ubangiji har abada.”
Bet ķēniņš Salamans būs svētīts, un Dāvida goda krēsls būs pastāvīgs priekš Tā Kunga mūžīgi.
46 Sai sarki ya umarci Benahiya ɗan Yehohiyada, yă fita, yă bugi Shimeyi, yă kashe shi. Ya kuwa kashe shi. Mulki kuwa ya kahu sosai a hannun Solomon.
Un ķēniņš pavēlēja Benajam, Jojadas dēlam; tas izgāja un viņu sita, un tas nomira. Tā valstība kļuva apstiprināta caur Salamana roku.

< 1 Sarakuna 2 >