< 1 Sarakuna 2 >
1 Da lokacin mutuwar Dawuda ya yi kusa, sai ya gargaɗe Solomon ɗansa, ya ce,
Bayat nga umas-asideg ti aldaw nga ipapatay ni David, binilinna ni Solomon nga anakna a kunana,
2 “Ina gab da bin hanyar da kowa a duniya zai bi. Saboda haka ka yi ƙarfin hali, ka nuna kanka namiji,
“Dandanin ti ipapanawko iti rabaw ti daga. Agbalinka koma a natibker, ngarud, ipakitam a naturedka.
3 ka kiyaye abin da Ubangiji Allahnka yake bukata. Yi tafiya a hanyoyinsa, ka kiyaye ƙa’idodi, da umarnai, da dokoki, da kuma farillansa, kamar yadda suke a rubuce a Dokar Musa, don ka yi nasara a cikin kome da za ka yi, da kuma inda za ka tafi.
Tungpalem dagiti bilin ni Yahweh a Diosmo nga agbiagka iti wagasna, a tungpalem dagiti alagadenna, dagiti bilbilinna, dagiti pangngeddengna, ken ti pammaneknekna iti tulagna, a tungpalem amin a naisurat iti linteg ni Moises, tapno rumang-ayka iti amin nga aramidem ken iti sadinoman a papanam,
4 Ubangiji kuwa zai kiyaye alkawarinsa gare ni da ya ce, ‘In zuriyarka suka lura da yadda suke rayuwa, in kuma suka yi tafiya da aminci a gabana da dukan zuciyarsu, da kuma dukan ransu, ba za ka kāsa samun mutum a kujerar sarautar Isra’ila ba.’
tapno tungpalen ni Yahweh ti saona nga imbagana maipanggep kaniak a kunana, 'No annadan dagiti annakmo ti tignayda, a magnada a sipupudno iti imatangko iti amin a puso ken kararuada, saankanto a maawanan iti tao nga agtugaw iti trono ti Israel.'
5 “Yanzu fa, kai kanka ka san abin da Yowab ɗan Zeruhiya ya yi mini. Abin da ya yi wa shugabanni biyun nan na mayaƙan Isra’ila, wato, Abner ɗan Ner, da Amasa ɗan Yeter. Ya kashe su, ya kuma zub da jininsu a lokacin salama sai ka ce a fage yaƙi, da wannan jini ya yi ɗamara a gindinsa, ya kuma sa takalma a ƙafafunsa.
Ammom met ti inaramid kaniak ni Joab nga anak ni Zeruiah, ken ti inaramidna a panangpatay kadagiti dua a pangulo ti armada ti Israel, ni Abner nga anak ni Ner, ken ni Amasa nga anak ni Jeter. Pinagsayasayna ti dara iti tiempo ti kappia ken imbarikes ken insapatosna ti dara iti gubat.
6 Ka yi da shi gwargwadon hikimarka, amma kada ka bari yă gangara kabari da furfura cikin salama. (Sheol )
Aramidem ti ammom a maiparbeng kenni Joab babaen iti kinasirib a nasursurom, ngem saanmo koma nga itulok a sitatalna a maitanem ti ubanan nga ulona. (Sheol )
7 “Amma ka yi alheri ga’ya’yan Barzillai mutumin Gileyad, ka sa su kasance a cikin waɗanda suke ci a teburinka. Sun goyi bayana sa’ad da nake gudu daga ɗan’uwanka Absalom.
Nupay kasta, ipakitam ti kinaimbag kadagiti annak ni Barsilai a taga-Gallaad, ket palubosam a maysada kadagiti makisango kenka a mangan iti lamisaanmo, ta immayda kaniak idi intarayak ni Absalom a kabsatmo.
8 “Ka tuna, akwai kuma Shimeyi ɗan Gera, mutumin Benyamin daga Bahurim, wanda ya yi ta yin mini muguwar la’ana a ranar da na tafi Mahanayim. Sa’ad da ya gangara ya same ni a Urdun, na rantse masa da sunan Ubangiji na ce, ‘Ba zan kashe ka da takobi ba.’
Adtoy, kaduayo met ni Shimei nga anak ni Gera, a taga-Bahurim iti Benjamin, a nangilunod kaniak iti kasta unay idi napanak idiay Mahanaim. Simmalog ni Shimei a mangsabat kaniak idiay Jordan, ket inkarik kenkuana iti nagan ni Yahweh, a kunak, 'Saanka a patayen babaen iti kampilan.'
9 Amma yanzu, kada ka ɗauke shi marar laifi. Kai mutum ne mai hikima; za ka san abin da za ka yi da shi. Ka kawo furfuransa zuwa kabari da jini.” (Sheol )
Ngarud, saanmo nga itulok a makalasat isuna manipud iti pannakadusa. Nasiribka a tao, ket ammom ti rumbeng nga aramidem kenkuana. Itanemmonto a dara-dara ti ubanan nga ulona. (Sheol )
10 Sa’an nan Dawuda ya huta tare da kakanninsa. Sai aka binne shi a Birnin Dawuda.
Kalpasanna, pimmusay ni David ket naitanem iti siudad ni David.
11 Ya yi sarauta shekaru arba’in a bisa Isra’ila. Wato, shekaru bakwai a Hebron da kuma talatin da uku a Urushalima.
Uppat a pulo a tawen ti panagturay ni David iti Israel. Pito a tawen a nagturay isuna idiay Hebron ken tallopulo a tawen idiay Jerusalem.
12 Solomon kuwa ya zauna a kan kujerar sarautar mahaifinsa Dawuda, mulkinsa kuwa ya kahu sosai.
Ket nagtugaw ni Solomon iti trono ti amana a ni David ket napatalgedan ti panagturayna.
13 To, sai Adoniya, ɗan Haggit ya tafi wurin Batsheba mahaifiyar Solomon. Ita kuwa ta tambaye shi ta ce, “Lafiya?” Ya amsa ya ce, “I, lafiya.”
Kalpasanna, immay kenni Batseba nga ina ni Solomon ni Adoniha nga anak ni Haggit. Kinuna ni Batseba kenkuana, “Kappia kadi ti immayam?” Simmungbat isuna, “Wen, immayak a sikakappia.”
14 Sa’an nan ya ƙara da cewa, “Ina da ɗan wani abin da zan faɗa miki.” Ta ce, “Faɗa.”
Ket kinuna ni Adoniha, “Adda ibagak kenka.” Isu a simmungbat ni Batseba, “Agsaoka.”
15 Sai ya ce, “Kamar yadda kika sani, mulkin nan nawa ne. Dukan Isra’ila suna ɗaukana a matsayin sarki. Amma abubuwa suka canja, sai mulkin ya koma ga ɗan’uwana; gama ya zo masa daga Ubangiji ne.
Kinuna ni Adoniha, “Ammom a para kaniak koma ti pagarian ken dagiti amin a tattao ti Israel, ninamnamada a siak ti agbalin nga ari. Nupay kasta, naiyawat iti kabsatko ti pagarian, ta para kenkuana daytoy a nagtaud kenni Yahweh.
16 Yanzu ina da roƙo guda da zan yi gare ki. Kada ki hana mini.” Ta ce, “Sai ka faɗa.”
Ita, adda maysa a kiddawek kenka. Saannak koma a paayen.” Kinuna ni Batseba kenkuana, “Agsaoka.”
17 Sai ya ci gaba, “In kin yarda, ki yi magana da Sarki Solomon, gama ba zai ƙi jinki ba, ki ce yă ba ni yarinyan nan, Abishag, mutuniyar Shunam, tă zama matata.”
Kinunana ni Adoniha, “Kasaritam koma ni Solomon nga ari, ta saannaka a paayen, tapno itedna koma kaniak ni Abisag a taga-Sunem nga agbalin nga asawak.”
18 Batsheba ta ce, “Da kyau, zan yi magana da sarki dominka.”
Kinuna ni Batseba, “Ala wen, kasaritak ti ari.”
19 Sai Batsheba ta tafi wurin Sarki Solomon don tă yi masa magana a kan Adoniya. Sarki ya miƙe tsaye don yă sadu da ita, ya rusuna mata, ya kuma zauna a kujerar sarautarsa. Ya sa aka kawo wa mahaifiyar sarki kujerar sarauta, ta kuwa zauna a gefen damansa.
Napan ngarud nakisarita ni Batseba kenni Ari Solomon para kenni Adoniha. Timmakder ti ari tapno sabtenna isuna ken nagkurno iti sangoananna. Ket nagtugaw ti ari iti tronona ket nagpaiyeg isuna iti tugaw para iti inana. Nagtugaw ni Batseba iti makannawan ni Solomon.
20 Ta ce, “Ina da ɗan roƙon da zan nema ka yi mini. Ina fata ba za ka hana ni ba.” Sai sarki ya amsa ya ce, “Mahaifiyata, sai ki faɗa in ji, ba zan hana miki ba.”
Ket kinuna ni Batseba, “Adda bassit a kiddawek kenka; saannak koma a paayen.” Simmungbat ti ari kenkuana, “Agkiddawkayo ina, saankayo a paayen.”
21 Saboda haka sai ta ce, “Ka sa a ba wa ɗan’uwanka Adoniya, Abishag mutuniyar Shunam tă zama matarsa.”
Kinuna ni Batseba, “Itedmo koma kenni Adoniha a kabsatmo ni Abisag a taga-Sunem tapno agbalin nga asawana.”
22 Sarki Solomon ya amsa wa mahaifiyarsa ya ce, “Me ya sa kika roƙar wa Adoniya Abishag mutuniyar Shunam kawai? Ki ma sa a ba shi mulkin mana. Ai, shi yayana ne. I, ki roƙa dominsa, da domin Abiyatar firist, da kuma domin Yowab ɗan Zeruhiya mana!”
Simmungbat ni Ari Solomon ket kinunana iti inana, “Apay a kiddawenyo ni Abisag a taga-Sunem para kenni Adoniha? Apay a saanmo pay a kiddawen ti pagarian para kenkuana, ta isuna ti inauna a kabsatko—para kenkuana, para kenni ni Abiatar a padi, ken para kenni Joab nga anak ni Zeruiah?”
23 Sai Sarki Solomon ya rantse da sunan Ubangiji ya ce, “Bari Allah yă yi mini hukunci mai tsanani, idan ban sa Adoniya ya biya wannan roƙo da ransa ba!
Kalpasanna, insapata ni Ari Solomon iti nagan ni Yahweh a kunana, “Sapay koma aramiden ti Dios daytoy kaniak ken ad-adda pay koma, no saan nga imbaga ni Adonia daytoy a sao maibusor iti biagna.
24 Yanzu kuwa, muddin Ubangiji yana a raye, shi wanda ya kafa ni sosai a kan kujerar sarautar mahaifina Dawuda, ya kuma kafa mini mulki kamar yadda ya yi alkawari; za a kashe Adoniya yau!”
Ita ngarud, iti nagan ni Yahweh nga adda iti agnanayon a nangisaad ken nangikabil kaniak iti trono ni David nga amak, ken nangaramid iti balay para kaniak kas inkarina, awan duadua a mapapatay ita nga aldaw ni Adoniha.”
25 Saboda haka Sarki Solomon ya umarci Benahiya ɗan Yehohiyada yă kashe Adoniya; ya kuwa kashe shi.
Isu nga imbaon ni Ari Solomon ni Benaias nga anak ni Jehoyada ket nasarakan ni Benaias ni Adoniha ket pinatayna daytoy.
26 Ga Abiyatar firist kuwa sarki ya ce, “Tafi gonarka a Anatot. Ka cancanci ka mutu, amma ba zan kashe ka yanzu ba, domin ka ɗauki akwatin alkawarin Ubangiji Mai Iko Duka a gaban mahaifina Dawuda, ka kuma sha wahala tare mahaifina.”
Kalpasanna, kinuna ti ari kenni Abiatar a padi, “Mapanka idiay Anatot, iti ayan ti dagam. Rumbeng laeng a matayka, ngem saanka nga ipapatay ita, gapu ta sika ti nakaitalkan ti lakasa ti tulag ni Yahweh a Dios iti sangoanan ni David nga amak ken nakipagsagabaka iti amin a sinagaba ti amak.”
27 Saboda haka Solomon ya cire Abiyatar daga aikin firist na Ubangiji, ya cika maganar da Ubangiji ya yi a Shilo game da gidan Eli.
Inikkat ngarud ni Solomon ni Abiatar a kas padi ni Yahweh, babaen kenkuana natungpal ti sao ni Yahweh nga imbagana idiay Shiloh maipapan iti balay ni Eli.
28 Sa’ad da labarin ya kai wurin Yowab, wanda ya haɗa kai da Adoniya, ko da yake bai haɗa kai da Absalom ba, sai ya gudu zuwa tentin Ubangiji, ya kama ƙahonin bagade ya riƙe.
Nadamag ni Joab daytoy, ta tinulongan ni Joab ni Adoniha, uray no saanna a tinulongan ni Absalom. Isu a timmaray ni Joab a napan iti tolda ni Yahweh ket immiggem kadagiti sara nga adda iti altar.
29 Aka faɗa wa Sarki Solomon cewa Yowab ya gudu zuwa tentin Ubangiji, yana kuma kusa da bagade. Sai Solomon ya umarci Benahiya ɗan Yehohiyada ya ce, “Je ka kashe shi!”
Naibaga kenni Ari Solomon a timmaray ni Joab iti tolda ni Yahweh ket addan iti abay ti altar. Imbaon ngarud ni Solomon ni Benaias nga anak ni Jehoyada a kunana, “Inka patayen isuna.”
30 Sai Benahiya ya shiga tentin Ubangiji ya ce wa Yowab, “Sarki ya ce, ‘Ka fita!’” Amma Yowab ya amsa ya ce, “A’a, a nan zan mutu.” Sai Benahiya ya ce wa sarki, “Ga yadda Yowab ya amsa mini.”
Isu a napan ni Benaias iti tolda ni Yahweh ket kinunana kenkuana, “Ibagbaga ti ari, 'Rummuarka.'” Simmungbat ni Joab, “Saan, ditoyak a matay.” Nagsubli ngarud ni Benaias iti ayan ti ari a kunana, “Kinuna ni Joab a kaykayatnan ti matay iti ayan ti altar.”
31 Sai sarki ya umarci Benahiya ya ce, “Yi kamar yadda ya faɗa. Ka kashe shi, ka kuma binne shi, ka wanke ni da gidan mahaifina daga laifin jini marasa laifin da Yowab ya zubar.
Kinuna ti ari kenkuana, “Aramidem no ania ti kayatna. Patayem ket itabonmo isuna, tapno maikkatmo kaniak ken iti balay ti amak ti dara a pinagsayasay ni Joab nga awan gapgapuna.
32 Ubangiji zai sāka masa saboda jinin da ya zubar, domin ba da sanin mahaifina Dawuda ne ya fāɗa wa mutum biyun nan da takobi ba. Dukansu biyu, Abner ɗan Ner, shugaban mayaƙan Isra’ila, da Amasa ɗan Yeter, shugaban mayaƙan Yahuda, mutane ne mafi kyau da kuma mafi adalci fiye da shi.
Isubli koma ni Yahweh ti dara ni Joab iti bukodna nga ulo, gapu ta dinarupna ti dua a lallaki a nalinlinteg ken nasaysayaat ngem isuna ket pinatayna ida babaen iti kampilan a saan nga ammo ni David nga amak, ni Abner a pangulo ti armada ti Israel nga anak ni Ner, ken ni Amasa a pangulo ti armada ti Juda nga anak ni Jeter.
33 Bari alhakin jininsu yă koma a kan Yowab da kuma zuriyarsa har abada. Amma bari salamar Ubangiji tă kasance a kan Dawuda da zuriyarsa, da gidansa, da kuma mulkinsa, har abada.”
Agsubli koma ti darada iti ulo ni Joab ken iti ulo dagiti kaputotanna iti agnanayon. Ngem kenni David ken kadagiti kaputotanna, ken iti balayna, ken iti tronona, adda koma ti kappia iti agnanayon nga agtaud kenni Yahweh.”
34 Sai Benahiya ɗan Yehohiyada ya haura ya bugi Yowab, ya kashe shi, ya kuwa binne shi a gidansa a ƙauye.
Simmang-at ngarud ni Benaias nga anak ni Jehoyada, ket dinarup ken pinatayna ni Joab. Naitabon isuna iti mismo a balayna idiay let-ang.
35 Sai sarki ya sa Benahiya ɗan Yehohiyada ya zama shugaba a bisa mayaƙa a matsayin Yowab, ya kuma sa Zadok firist a wurin Abiyatar.
Insaad ti ari ni Benaias nga anak ni Jehoyada a kas pangulo ti armada a kas kasukat ni Joab, ket insaadna met Zadok a padi a kas kasukat ni Abiatar.
36 Sa’an nan sarki ya aika aka kawo Shimeyi, ya kuma ce masa, “Ka gina wa kanka gida a nan a Urushalima, ka zauna a ciki, kada ka kuskura ka tafi wani wuri.
Kalpasanna, nangibaon ti ari iti mangayab kenni Shimei ket kinunana kenkuana, “Mangaramidka iti balaymo idiay Jerusalem ket agnaedka sadiay, ken saanka a mapmapan iti sabali a lugar.
37 Gama ran da ka fita, ka haye Kwarin Kidron, ka tabbata za ka mutu, alhakin jininka kuwa zai koma kanka.”
Ta iti kanito a ballasiwem ti Tanap ti Kidron, ammomon nga awan duadua a matayka. Sikanto ti makinbasol iti ipapataymo.”
38 Shimeyi ya amsa wa sarki ya ce, “Abin da ka faɗa yana da kyau. Bawanka zai yi kamar yadda ranka yă daɗe sarki, ya faɗa.” Shimeyi kuwa ya yi zama a Urushalima na dogon lokaci.
Isu a kinuna ni Shimei iti ari, “Nasayaat ti imbagam. Kas iti imbaga ti apok nga ari, aramiden ngarud daytoy ti adipenmo.” Nagnaed ngarud ni Shimei iti Jerusalem iti adu nga al-aldaw.
39 Amma bayan shekaru uku, biyu daga cikin bayin Shimeyi suka gudu zuwa wurin Akish ɗan Ma’aka, sarkin Gat. Aka faɗa wa Shimeyi cewa, “Bayinka suna a Gat.”
Ngem idi aglippasen ti tallo a tawen, dua kadagiti adipenna ti nagtalaw a napan kenni Akis nga ari ti Gat nga anak ni Maacah. Imbagada kenni Shemei daytoy a kunada, “Kitaem, adda idiay Gat dagiti adipenmo.”
40 Da jin haka, sai ya tashi ya shimfiɗa wa jakinsa abin zama, ya hau, ya tafi Gat wurin Akish domin neman bayinsa. Shimeyi kuwa ya dawo da su gida daga Gat.
Nagrubwat ngarud ni Shimei, inkabilna ti silyeta iti asnona ket napan kenni Akis idiay Gat tapno birokenna dagiti adipenna. Inyawidna dagiti adipenna manipud idiay Gat.
41 Da aka faɗa wa Solomon cewa Shimeyi ya bar Urushalima zuwa Gat, har ya dawo.
Idi naibaga kenni Solomon a pimmanaw ni Shimei idiay Jerusalem ket napan biit idiay Gat,
42 Sai sarki ya aika a kawo Shimeyi, ya ce masa, “Ban sa ka rantse da sunan Ubangiji, na kuma ja maka kunne cewa, ‘A ranar da ka kuskura ka bar nan ka tafi wani wuri, ka tabbata za ka mutu ba’? A lokacin ka ce mini, ‘Abin da ka faɗa yana da kyau. Zan kuwa kiyaye.’
nangibaon ni Solomon iti mangayab kenni Shimei, ket kinunana kenkuana, “Saan kadi a pinagsapataka iti nagan ni Yahweh, ken pinatalgedak a kunak, 'Iti kanito a rummuarka ket mapanka iti sabali a lugar, ammomon nga awan duadua a matayka'? Ket kinunam kaniak, 'Nasayaat ti imbagam.'
43 To, me ya sa ba ka kiyaye rantsuwar da ka yi ga Ubangiji, ka kuma yi biyayya da umarnin da na ba ka ba?”
Apay ngarud a saanmo a tinungpal ti sapatam kenni Yahweh, ken ti imbilinko kenka?”
44 Sarki ya ce wa Shimeyi, “Ka sani a zuciyarka dukan muguntar da ka yi wa mahaifina Dawuda. Yanzu Ubangiji zai sāka maka saboda muguntarka.
Kinuna pay ti ari kenni Shimei, “Ammom iti pusom dagiti kinadangkes nga inaramidmo kenni David nga amak. No kasta ngarud, isubli met laeng ni Yahweh kenka ti kinadangkesmo.
45 Amma za a yi wa Sarki Solomon albarka, sarautar Dawuda kuma za tă kasance a tsare a gaban Ubangiji har abada.”
Ngem mabendisionanto ni Ari Solomon, ket maisaadto iti agnanayon ti trono ni David iti sangoanan ni Yahweh.”
46 Sai sarki ya umarci Benahiya ɗan Yehohiyada, yă fita, yă bugi Shimeyi, yă kashe shi. Ya kuwa kashe shi. Mulki kuwa ya kahu sosai a hannun Solomon.
Isu nga imbaon ti ari ni Benaias nga anak ni Jehoyada, rimmuar isuna ket pinatayna ni Shimei. Isu a napatalgedan ti turay iti ima ni Solomon.