< 1 Sarakuna 2 >

1 Da lokacin mutuwar Dawuda ya yi kusa, sai ya gargaɗe Solomon ɗansa, ya ce,
Or, approchèrent les jours où David devait mourir, et ils ordonna à Salomon, son fils, disant:
2 “Ina gab da bin hanyar da kowa a duniya zai bi. Saboda haka ka yi ƙarfin hali, ka nuna kanka namiji,
Moi j’entre dans la voie de toute la terre: fortifie-toi, et sois homme.
3 ka kiyaye abin da Ubangiji Allahnka yake bukata. Yi tafiya a hanyoyinsa, ka kiyaye ƙa’idodi, da umarnai, da dokoki, da kuma farillansa, kamar yadda suke a rubuce a Dokar Musa, don ka yi nasara a cikin kome da za ka yi, da kuma inda za ka tafi.
Observe les commandements du Seigneur ton Dieu, afin que tu marches dans ses voies, que tu gardes ses cérémonies, ses préceptes, ses ordonnances et ses lois, comme il est écrit dans la loi de Moïse, afin que tu comprennes tout ce que tu feras et toutes tes démarches,
4 Ubangiji kuwa zai kiyaye alkawarinsa gare ni da ya ce, ‘In zuriyarka suka lura da yadda suke rayuwa, in kuma suka yi tafiya da aminci a gabana da dukan zuciyarsu, da kuma dukan ransu, ba za ka kāsa samun mutum a kujerar sarautar Isra’ila ba.’
Afin que le Seigneur confirme les paroles qu’il a prononcées à mon sujet, disant: Si tes enfants gardent leurs voies, et qu’ils marchent devant moi dans la vérité, en tout leur cœur et en toute leur âme, un homme ne te sera pas enlevé du trône d’Israël.
5 “Yanzu fa, kai kanka ka san abin da Yowab ɗan Zeruhiya ya yi mini. Abin da ya yi wa shugabanni biyun nan na mayaƙan Isra’ila, wato, Abner ɗan Ner, da Amasa ɗan Yeter. Ya kashe su, ya kuma zub da jininsu a lokacin salama sai ka ce a fage yaƙi, da wannan jini ya yi ɗamara a gindinsa, ya kuma sa takalma a ƙafafunsa.
Toi aussi, tu sais ce que m’a fait Joab, fils de Sarvia, et ce qu’il a fait à deux chefs de l’armée d’Israël, à Abner, fils de Ner, et à Amasa, fils de Jéther, qu’il a tués; et il a versé en paix du sang de guerre; et il a mis du sang de combat sur le baudrier qui était à ses reins et sur la chaussure qui était à ses pieds.
6 Ka yi da shi gwargwadon hikimarka, amma kada ka bari yă gangara kabari da furfura cikin salama. (Sheol h7585)
Tu feras donc selon ta sagesse, et tu ne laisseras pas descendre en paix ses cheveux blancs dans les enfers. (Sheol h7585)
7 “Amma ka yi alheri ga’ya’yan Barzillai mutumin Gileyad, ka sa su kasance a cikin waɗanda suke ci a teburinka. Sun goyi bayana sa’ad da nake gudu daga ɗan’uwanka Absalom.
Mais tu rendras grâce aux fils de Berzellaï, le Galaadite, et ils mangeront à la table: car ils ont couru au-devant de moi, quand je fuyais devant Absalom, ton frère.
8 “Ka tuna, akwai kuma Shimeyi ɗan Gera, mutumin Benyamin daga Bahurim, wanda ya yi ta yin mini muguwar la’ana a ranar da na tafi Mahanayim. Sa’ad da ya gangara ya same ni a Urdun, na rantse masa da sunan Ubangiji na ce, ‘Ba zan kashe ka da takobi ba.’
Tu as aussi auprès de toi Séméi, fils de Géra, fils de Jémini, de Bahurim, qui m’a maudit de la malédiction la plus cruelle, quand je m’en allais au camp: mais, parce qu’il descendit au-devant de moi, lorsque je traversai le Jourdain, je lui jurai par le Seigneur, disant: Je ne te tuerai point par le glaive.
9 Amma yanzu, kada ka ɗauke shi marar laifi. Kai mutum ne mai hikima; za ka san abin da za ka yi da shi. Ka kawo furfuransa zuwa kabari da jini.” (Sheol h7585)
Pour toi, ne souffre pas qu’il n’éprouve aucun dommage. Mais tu es un homme sage, en sorte que tu sais ce que tu lui feras, et tu feras descendre ses cheveux blancs avec du sang dans les enfers. (Sheol h7585)
10 Sa’an nan Dawuda ya huta tare da kakanninsa. Sai aka binne shi a Birnin Dawuda.
David dormit donc avec ses pères, et il fut enseveli dans la cité de David.
11 Ya yi sarauta shekaru arba’in a bisa Isra’ila. Wato, shekaru bakwai a Hebron da kuma talatin da uku a Urushalima.
Or, les jours durant lesquels David régna sur Israël furent de quarante années: à Hébron, il régna sept ans, et à Jérusalem, trente-trois ans.
12 Solomon kuwa ya zauna a kan kujerar sarautar mahaifinsa Dawuda, mulkinsa kuwa ya kahu sosai.
Et Salomon s’assit sur le trône de David, son père, et son règne s’affermit puissamment.
13 To, sai Adoniya, ɗan Haggit ya tafi wurin Batsheba mahaifiyar Solomon. Ita kuwa ta tambaye shi ta ce, “Lafiya?” Ya amsa ya ce, “I, lafiya.”
Et Adonias, fils d’Haggith, entra chez Bethsabée, mère de Salomon. Elle lui demanda: Ton entrée ici est-elle pacifique? Il lui répondit: Pacifique.
14 Sa’an nan ya ƙara da cewa, “Ina da ɗan wani abin da zan faɗa miki.” Ta ce, “Faɗa.”
Et il ajouta: J’ai un mot pour vous. Elle lui dit: Parle. Et lui:
15 Sai ya ce, “Kamar yadda kika sani, mulkin nan nawa ne. Dukan Isra’ila suna ɗaukana a matsayin sarki. Amma abubuwa suka canja, sai mulkin ya koma ga ɗan’uwana; gama ya zo masa daga Ubangiji ne.
Vous savez, dit-il, que le royaume était à moi, et que tout Israël m’avait mis à sa tête comme roi; mais le royaume a été transféré, et il a passé à mon frère; car c’est par le Seigneur qu’il lui a été attribué.
16 Yanzu ina da roƙo guda da zan yi gare ki. Kada ki hana mini.” Ta ce, “Sai ka faɗa.”
Maintenant donc, je ne vous fais qu’une seule prière; ne couvrez pas ma face de confusion. Bethsabée lui dit: Parle.
17 Sai ya ci gaba, “In kin yarda, ki yi magana da Sarki Solomon, gama ba zai ƙi jinki ba, ki ce yă ba ni yarinyan nan, Abishag, mutuniyar Shunam, tă zama matata.”
Et Adonias lui dit: Je vous prie de dire à Salomon, le roi (car il ne peut rien vous refuser), qu’il me donne Abisag, la Sunamite, pour femme.
18 Batsheba ta ce, “Da kyau, zan yi magana da sarki dominka.”
Et Bethsabée dit: Bien; je parlerai moi-même pour toi au roi.
19 Sai Batsheba ta tafi wurin Sarki Solomon don tă yi masa magana a kan Adoniya. Sarki ya miƙe tsaye don yă sadu da ita, ya rusuna mata, ya kuma zauna a kujerar sarautarsa. Ya sa aka kawo wa mahaifiyar sarki kujerar sarauta, ta kuwa zauna a gefen damansa.
Bethsabée vint donc auprès du roi Salomon, afin de lui parler pour Adonias; et le roi se leva au-devant d’elle, puis il s’assit sur son trône: et un trône fut placé pour la mère du roi, laquelle s’assit à sa droite.
20 Ta ce, “Ina da ɗan roƙon da zan nema ka yi mini. Ina fata ba za ka hana ni ba.” Sai sarki ya amsa ya ce, “Mahaifiyata, sai ki faɗa in ji, ba zan hana miki ba.”
Et elle lui dit: Je n’ai qu’une petite prière à te faire; ne couvre pas ma face de confusion. Et le roi lui dit: Demandez, ma mère; car il n’est pas juste que j’écarte votre face.
21 Saboda haka sai ta ce, “Ka sa a ba wa ɗan’uwanka Adoniya, Abishag mutuniyar Shunam tă zama matarsa.”
Bethsabée lui dit: Qu’Abisag, la Sunamite, soit donnée à Adonias, ton frère, pour femme.
22 Sarki Solomon ya amsa wa mahaifiyarsa ya ce, “Me ya sa kika roƙar wa Adoniya Abishag mutuniyar Shunam kawai? Ki ma sa a ba shi mulkin mana. Ai, shi yayana ne. I, ki roƙa dominsa, da domin Abiyatar firist, da kuma domin Yowab ɗan Zeruhiya mana!”
Et le roi Salomon répondit et dit à sa mère: Pourquoi demandez-vous Abisag, la Sunamite, pour Adonias? Demandez aussi pour lui le royaume; car il est mon frère aîné, et il a déjà pour lui Abiathar, le prêtre, et Joab, fils de Sarvia.
23 Sai Sarki Solomon ya rantse da sunan Ubangiji ya ce, “Bari Allah yă yi mini hukunci mai tsanani, idan ban sa Adoniya ya biya wannan roƙo da ransa ba!
C’est pourquoi le roi Salomon jura par le Seigneur, disant: Que Dieu me fasse ceci, et qu’il ajoute cela, si ce n’est pas contre son âme qu’Adonias a dit cette parole.
24 Yanzu kuwa, muddin Ubangiji yana a raye, shi wanda ya kafa ni sosai a kan kujerar sarautar mahaifina Dawuda, ya kuma kafa mini mulki kamar yadda ya yi alkawari; za a kashe Adoniya yau!”
Et maintenant le Seigneur vit, lui, qui m’a affermi, qui m’a placé sur le trône de David, mon père, et qui m’a fait une maison, comme il l’avait dit! aujourd’hui Adonias sera mis à mort.
25 Saboda haka Sarki Solomon ya umarci Benahiya ɗan Yehohiyada yă kashe Adoniya; ya kuwa kashe shi.
Et le roi Salomon envoya Banaïas, fils de Joïada, qui le tua, et il mourut.
26 Ga Abiyatar firist kuwa sarki ya ce, “Tafi gonarka a Anatot. Ka cancanci ka mutu, amma ba zan kashe ka yanzu ba, domin ka ɗauki akwatin alkawarin Ubangiji Mai Iko Duka a gaban mahaifina Dawuda, ka kuma sha wahala tare mahaifina.”
Le roi dit aussi à Abiathar, le prêtre: Va à Anathoth, dans ton champ; à la vérité, tu es un homme de mort; mais aujourd’hui je ne te tuerai point, parce que tu as porté l’arche du Seigneur Dieu devant David, mon père, et que tu as supporté le labeur dans toutes les choses dans lesquelles mon père l’a enduré.
27 Saboda haka Solomon ya cire Abiyatar daga aikin firist na Ubangiji, ya cika maganar da Ubangiji ya yi a Shilo game da gidan Eli.
Salomon relégua donc Abiathar, pour qu’il ne fût plus le prêtre du Seigneur, afin que la parole que le Seigneur avait dite fût accomplie sur la maison d’Héli à Silo.
28 Sa’ad da labarin ya kai wurin Yowab, wanda ya haɗa kai da Adoniya, ko da yake bai haɗa kai da Absalom ba, sai ya gudu zuwa tentin Ubangiji, ya kama ƙahonin bagade ya riƙe.
Or cette nouvelle vint à Joab, parce qu’il avait passé à Adonias, et qu’il n’avait pas passé à Salomon: Joab donc s’enfuit dans le tabernacle du Seigneur, et saisit la corne de l’autel.
29 Aka faɗa wa Sarki Solomon cewa Yowab ya gudu zuwa tentin Ubangiji, yana kuma kusa da bagade. Sai Solomon ya umarci Benahiya ɗan Yehohiyada ya ce, “Je ka kashe shi!”
Et l’on annonça au roi Salomon que Joab s’était enfui dans le tabernacle du Seigneur, et qu’il était près de l’autel; et Salomon envoya Banaïas, fils de Joïada, disant: Va, et tue-le.
30 Sai Benahiya ya shiga tentin Ubangiji ya ce wa Yowab, “Sarki ya ce, ‘Ka fita!’” Amma Yowab ya amsa ya ce, “A’a, a nan zan mutu.” Sai Benahiya ya ce wa sarki, “Ga yadda Yowab ya amsa mini.”
Et Banaïas vint au tabernacle du Seigneur, et dit à Joab: Voici ce que dit le roi: Sors. Joab répondit: Je ne sortirai point, mais je mourrai ici. Banaïas rapporta cette parole au roi, disant: Voilà ce qu’a dit Joab, et voilà ce qu’il m’a répondu.
31 Sai sarki ya umarci Benahiya ya ce, “Yi kamar yadda ya faɗa. Ka kashe shi, ka kuma binne shi, ka wanke ni da gidan mahaifina daga laifin jini marasa laifin da Yowab ya zubar.
Et le roi lui dit: Fais comme il a dit: tue-le et l’ensevelis; et tu écarteras de moi et de la maison de mon père un sang innocent qui a été versé par Joab.
32 Ubangiji zai sāka masa saboda jinin da ya zubar, domin ba da sanin mahaifina Dawuda ne ya fāɗa wa mutum biyun nan da takobi ba. Dukansu biyu, Abner ɗan Ner, shugaban mayaƙan Isra’ila, da Amasa ɗan Yeter, shugaban mayaƙan Yahuda, mutane ne mafi kyau da kuma mafi adalci fiye da shi.
Et le Seigneur fera retomber son sang sur sa tête, parce qu’il a tué deux hommes justes, meilleurs que lui, et qu’il les a tués par le glaive, mon père David l’ignorant: Abner, fils de Ner, prince de la milice d’Israël, et Amasa, fils de Jéther, prince de l’armée de Juda;
33 Bari alhakin jininsu yă koma a kan Yowab da kuma zuriyarsa har abada. Amma bari salamar Ubangiji tă kasance a kan Dawuda da zuriyarsa, da gidansa, da kuma mulkinsa, har abada.”
Et leur sang retombera sur la tête de Joab et sur la tête de sa postérité pour jamais. Mais qu’à David et à sa postérité, à sa maison et à son trône, soit une paix éternelle par le Seigneur.
34 Sai Benahiya ɗan Yehohiyada ya haura ya bugi Yowab, ya kashe shi, ya kuwa binne shi a gidansa a ƙauye.
C’est pourquoi Banaïas, fils de Joïada, monta; et ayant attaqué Joab, il le tua; et il fut enseveli en sa maison, dans le désert.
35 Sai sarki ya sa Benahiya ɗan Yehohiyada ya zama shugaba a bisa mayaƙa a matsayin Yowab, ya kuma sa Zadok firist a wurin Abiyatar.
Et le roi établi Banaïas, fils de Joïada, sur l’armée au lieu de Joab, et il mit Sadoc, le prêtre, à la place d’Abiathar.
36 Sa’an nan sarki ya aika aka kawo Shimeyi, ya kuma ce masa, “Ka gina wa kanka gida a nan a Urushalima, ka zauna a ciki, kada ka kuskura ka tafi wani wuri.
Le roi envoya aussi, et appela Séméi, et lui dit: Bâtis-toi une maison dans Jérusalem, et demeures-y, et n’en sors point pour aller ici et là.
37 Gama ran da ka fita, ka haye Kwarin Kidron, ka tabbata za ka mutu, alhakin jininka kuwa zai koma kanka.”
Or, au jour où tu sortiras, et tu passeras le torrent de Cédron, sache que tu seras tué et que ton sang sera sur ta tête.
38 Shimeyi ya amsa wa sarki ya ce, “Abin da ka faɗa yana da kyau. Bawanka zai yi kamar yadda ranka yă daɗe sarki, ya faɗa.” Shimeyi kuwa ya yi zama a Urushalima na dogon lokaci.
Séméi dit au roi: Cette parole est juste. Comme mon seigneur le roi a dit, ainsi fera votre serviteur. C’est pourquoi Séméi demeura longtemps à Jérusalem.
39 Amma bayan shekaru uku, biyu daga cikin bayin Shimeyi suka gudu zuwa wurin Akish ɗan Ma’aka, sarkin Gat. Aka faɗa wa Shimeyi cewa, “Bayinka suna a Gat.”
Mais il arriva, après trois ans, que les esclaves de Séméi s’enfuirent vers Achis, fils de Maacha, roi de Geth; et on annonça à Séméi que ses esclaves étaient allés à Geth.
40 Da jin haka, sai ya tashi ya shimfiɗa wa jakinsa abin zama, ya hau, ya tafi Gat wurin Akish domin neman bayinsa. Shimeyi kuwa ya dawo da su gida daga Gat.
Et Séméi se leva, scella son âne, et s’en alla vers Achis, à Geth, pour redemander ses esclaves, et les ramena de Geth.
41 Da aka faɗa wa Solomon cewa Shimeyi ya bar Urushalima zuwa Gat, har ya dawo.
Or, on annonça à Salomon que Séméi avait été de Jérusalem à Geth, et qu’il était revenu.
42 Sai sarki ya aika a kawo Shimeyi, ya ce masa, “Ban sa ka rantse da sunan Ubangiji, na kuma ja maka kunne cewa, ‘A ranar da ka kuskura ka bar nan ka tafi wani wuri, ka tabbata za ka mutu ba’? A lokacin ka ce mini, ‘Abin da ka faɗa yana da kyau. Zan kuwa kiyaye.’
Et envoyant, il l’appela, et lui dit: Ne t’ai-je pas juré par le Seigneur, et dit par avance: Au jour où, étant sorti, tu iras ici et là, sache que tu mourras? Et tu m’as répondu: Elle est juste la parole que j’ai entendue.
43 To, me ya sa ba ka kiyaye rantsuwar da ka yi ga Ubangiji, ka kuma yi biyayya da umarnin da na ba ka ba?”
Pourquoi donc n’as-tu pas gardé le serment du Seigneur, et l’ordre que je t’avais donné?
44 Sarki ya ce wa Shimeyi, “Ka sani a zuciyarka dukan muguntar da ka yi wa mahaifina Dawuda. Yanzu Ubangiji zai sāka maka saboda muguntarka.
Et le roi dit à Séméi: Tu sais toi-même tout le mal que ton cœur te reproche d’avoir fait à David, mon père: le Seigneur a fait retomber ta malice sur ta tête.
45 Amma za a yi wa Sarki Solomon albarka, sarautar Dawuda kuma za tă kasance a tsare a gaban Ubangiji har abada.”
Elle roi Salomon sera béni, et le trône de David sera stable devant le Seigneur à jamais.
46 Sai sarki ya umarci Benahiya ɗan Yehohiyada, yă fita, yă bugi Shimeyi, yă kashe shi. Ya kuwa kashe shi. Mulki kuwa ya kahu sosai a hannun Solomon.
C’est pourquoi Salomon commanda à Banaïas, fils de Joïada; et Banaïas sortit, frappa Séméi; et il mourut.

< 1 Sarakuna 2 >