< 1 Sarakuna 2 >

1 Da lokacin mutuwar Dawuda ya yi kusa, sai ya gargaɗe Solomon ɗansa, ya ce,
Le temps de la mort de David approchant, il donna ses commandements à son fils Salomon, et lui dit:
2 “Ina gab da bin hanyar da kowa a duniya zai bi. Saboda haka ka yi ƙarfin hali, ka nuna kanka namiji,
Je m'en vais par le chemin de toute la terre; fortifie-toi et sois un homme.
3 ka kiyaye abin da Ubangiji Allahnka yake bukata. Yi tafiya a hanyoyinsa, ka kiyaye ƙa’idodi, da umarnai, da dokoki, da kuma farillansa, kamar yadda suke a rubuce a Dokar Musa, don ka yi nasara a cikin kome da za ka yi, da kuma inda za ka tafi.
Et garde ce que l'Éternel ton Dieu veut que tu gardes, en marchant dans ses voies, et en gardant ses statuts, ses commandements, ses ordonnances et ses témoignages, selon ce qui est écrit dans la loi de Moïse; afin que tu réussisses dans tout ce que tu feras et dans tout ce que tu entreprendras;
4 Ubangiji kuwa zai kiyaye alkawarinsa gare ni da ya ce, ‘In zuriyarka suka lura da yadda suke rayuwa, in kuma suka yi tafiya da aminci a gabana da dukan zuciyarsu, da kuma dukan ransu, ba za ka kāsa samun mutum a kujerar sarautar Isra’ila ba.’
Et que l'Éternel accomplisse la parole qu'il a prononcée à mon égard, en disant: Si tes fils prennent garde à leur voie, pour marcher devant moi dans la vérité, de tout leur cœur et de toute leur âme, alors ta descendance ne sera jamais retranchée du trône d'Israël.
5 “Yanzu fa, kai kanka ka san abin da Yowab ɗan Zeruhiya ya yi mini. Abin da ya yi wa shugabanni biyun nan na mayaƙan Isra’ila, wato, Abner ɗan Ner, da Amasa ɗan Yeter. Ya kashe su, ya kuma zub da jininsu a lokacin salama sai ka ce a fage yaƙi, da wannan jini ya yi ɗamara a gindinsa, ya kuma sa takalma a ƙafafunsa.
Au reste, tu sais ce que m'a fait Joab, fils de Tséruja, ce qu'il a fait à deux chefs des armées d'Israël, à Abner, fils de Ner, et à Amasa, fils de Jéther, qu'il a tués, versant dans la paix le sang de la guerre, et ensanglantant du sang de la guerre la ceinture qu'il avait aux reins et les souliers qu'il avait aux pieds.
6 Ka yi da shi gwargwadon hikimarka, amma kada ka bari yă gangara kabari da furfura cikin salama. (Sheol h7585)
Tu agiras selon ta sagesse, et ne laisseras point descendre en paix ses cheveux blancs au Sépulcre. (Sheol h7585)
7 “Amma ka yi alheri ga’ya’yan Barzillai mutumin Gileyad, ka sa su kasance a cikin waɗanda suke ci a teburinka. Sun goyi bayana sa’ad da nake gudu daga ɗan’uwanka Absalom.
Quant aux fils de Barzillaï, le Galaadite, tu useras de bonté à leur égard, et ils seront de ceux qui mangent à ta table; car c'est ainsi qu'ils sont venus vers moi, lorsque je fuyais devant Absalom, ton frère.
8 “Ka tuna, akwai kuma Shimeyi ɗan Gera, mutumin Benyamin daga Bahurim, wanda ya yi ta yin mini muguwar la’ana a ranar da na tafi Mahanayim. Sa’ad da ya gangara ya same ni a Urdun, na rantse masa da sunan Ubangiji na ce, ‘Ba zan kashe ka da takobi ba.’
Et voici, tu as avec toi Shimeï, fils de Guéra, le Benjamite, de Bachurim, qui prononça contre moi des malédictions atroces, le jour que je m'en allais à Mahanaïm; mais il descendit au-devant de moi vers le Jourdain, et je lui jurai par l'Éternel et lui dis: Je ne te ferai pas mourir par l'épée.
9 Amma yanzu, kada ka ɗauke shi marar laifi. Kai mutum ne mai hikima; za ka san abin da za ka yi da shi. Ka kawo furfuransa zuwa kabari da jini.” (Sheol h7585)
Maintenant donc, tu ne le laisseras point impuni; car tu es sage pour savoir ce que tu lui devras faire; mais tu feras descendre ensanglantés ses cheveux blancs au Sépulcre. (Sheol h7585)
10 Sa’an nan Dawuda ya huta tare da kakanninsa. Sai aka binne shi a Birnin Dawuda.
Ainsi David s'endormit avec ses pères, et il fut enseveli dans la cité de David.
11 Ya yi sarauta shekaru arba’in a bisa Isra’ila. Wato, shekaru bakwai a Hebron da kuma talatin da uku a Urushalima.
Et le temps que David régna sur Israël fut de quarante ans. Il régna sept ans à Hébron, et trente-trois ans à Jérusalem.
12 Solomon kuwa ya zauna a kan kujerar sarautar mahaifinsa Dawuda, mulkinsa kuwa ya kahu sosai.
Et Salomon s'assit sur le trône de David, son père, et son règne fut très affermi.
13 To, sai Adoniya, ɗan Haggit ya tafi wurin Batsheba mahaifiyar Solomon. Ita kuwa ta tambaye shi ta ce, “Lafiya?” Ya amsa ya ce, “I, lafiya.”
Alors Adonija, fils de Hagguith, vint chez Bath-Shéba, mère de Salomon. Et elle dit: Viens-tu pour la paix? Et il répondit: Pour la paix.
14 Sa’an nan ya ƙara da cewa, “Ina da ɗan wani abin da zan faɗa miki.” Ta ce, “Faɗa.”
Puis il dit: J'ai un mot à te dire. Elle répondit: Parle!
15 Sai ya ce, “Kamar yadda kika sani, mulkin nan nawa ne. Dukan Isra’ila suna ɗaukana a matsayin sarki. Amma abubuwa suka canja, sai mulkin ya koma ga ɗan’uwana; gama ya zo masa daga Ubangiji ne.
Et il dit: Tu sais bien que le royaume m'appartenait, et que tout Israël s'attendait à ce que je régnasse; mais la royauté a été transférée, et elle est échue à mon frère, parce que l'Éternel la lui a donnée.
16 Yanzu ina da roƙo guda da zan yi gare ki. Kada ki hana mini.” Ta ce, “Sai ka faɗa.”
Maintenant donc j'ai une demande à te faire; ne me la refuse pas. Et elle lui dit: Parle!
17 Sai ya ci gaba, “In kin yarda, ki yi magana da Sarki Solomon, gama ba zai ƙi jinki ba, ki ce yă ba ni yarinyan nan, Abishag, mutuniyar Shunam, tă zama matata.”
Et il dit: Je te prie, dis au roi Salomon (car il ne te refusera pas), qu'il me donne pour femme Abishag, la Sunamite.
18 Batsheba ta ce, “Da kyau, zan yi magana da sarki dominka.”
Bath-Shéba répondit: Bien; je parlerai pour toi au roi.
19 Sai Batsheba ta tafi wurin Sarki Solomon don tă yi masa magana a kan Adoniya. Sarki ya miƙe tsaye don yă sadu da ita, ya rusuna mata, ya kuma zauna a kujerar sarautarsa. Ya sa aka kawo wa mahaifiyar sarki kujerar sarauta, ta kuwa zauna a gefen damansa.
Et Bath-Shéba alla vers le roi Salomon, afin de lui parler pour Adonija. Et le roi, se levant, vint au-devant d'elle et se prosterna devant elle; puis il s'assit sur son trône, et fit mettre un siège pour la mère du roi; et elle s'assit à sa droite.
20 Ta ce, “Ina da ɗan roƙon da zan nema ka yi mini. Ina fata ba za ka hana ni ba.” Sai sarki ya amsa ya ce, “Mahaifiyata, sai ki faɗa in ji, ba zan hana miki ba.”
Et elle dit: J'ai une petite demande à te faire; ne me la refuse pas. Et le roi lui répondit: Fais-la, ma mère; car je ne te la refuserai pas.
21 Saboda haka sai ta ce, “Ka sa a ba wa ɗan’uwanka Adoniya, Abishag mutuniyar Shunam tă zama matarsa.”
Et elle dit: Qu'on donne Abishag, la Sunamite, pour femme à Adonija, ton frère.
22 Sarki Solomon ya amsa wa mahaifiyarsa ya ce, “Me ya sa kika roƙar wa Adoniya Abishag mutuniyar Shunam kawai? Ki ma sa a ba shi mulkin mana. Ai, shi yayana ne. I, ki roƙa dominsa, da domin Abiyatar firist, da kuma domin Yowab ɗan Zeruhiya mana!”
Mais le roi Salomon répondit et dit à sa mère: Et pourquoi demandes-tu Abishag, la Sunamite, pour Adonija? Demande donc le royaume pour lui, car il est mon frère aîné; pour lui, et pour Abiathar, le sacrificateur, et pour Joab, fils de Tséruja!
23 Sai Sarki Solomon ya rantse da sunan Ubangiji ya ce, “Bari Allah yă yi mini hukunci mai tsanani, idan ban sa Adoniya ya biya wannan roƙo da ransa ba!
Alors le roi Salomon jura par l'Éternel, en disant: Que Dieu me traite dans toute sa rigueur, si Adonija n'a dit cette parole contre sa propre vie!
24 Yanzu kuwa, muddin Ubangiji yana a raye, shi wanda ya kafa ni sosai a kan kujerar sarautar mahaifina Dawuda, ya kuma kafa mini mulki kamar yadda ya yi alkawari; za a kashe Adoniya yau!”
Et maintenant, l'Éternel est vivant, qui m'a établi et fait asseoir sur le trône de David, mon père, et qui a établi ma maison comme il l'avait dit! Certainement Adonija sera mis à mort aujourd'hui.
25 Saboda haka Sarki Solomon ya umarci Benahiya ɗan Yehohiyada yă kashe Adoniya; ya kuwa kashe shi.
Et le roi Salomon donna commission à Bénaja, fils de Jéhojada, qui se jeta sur lui; et il mourut.
26 Ga Abiyatar firist kuwa sarki ya ce, “Tafi gonarka a Anatot. Ka cancanci ka mutu, amma ba zan kashe ka yanzu ba, domin ka ɗauki akwatin alkawarin Ubangiji Mai Iko Duka a gaban mahaifina Dawuda, ka kuma sha wahala tare mahaifina.”
Puis le roi dit à Abiathar, le sacrificateur: Va-t'en à Anathoth, dans ta possession; car tu mérites la mort; toutefois je ne te ferai pas mourir aujourd'hui; car tu as porté l'arche du Seigneur l'Éternel devant David, mon père, et tu as eu part à toutes les afflictions de mon père.
27 Saboda haka Solomon ya cire Abiyatar daga aikin firist na Ubangiji, ya cika maganar da Ubangiji ya yi a Shilo game da gidan Eli.
Ainsi Salomon chassa Abiathar, afin qu'il ne fût plus sacrificateur de l'Éternel; et cela, pour accomplir la parole de l'Éternel, qu'il avait prononcée à Silo contre la maison d'Héli.
28 Sa’ad da labarin ya kai wurin Yowab, wanda ya haɗa kai da Adoniya, ko da yake bai haɗa kai da Absalom ba, sai ya gudu zuwa tentin Ubangiji, ya kama ƙahonin bagade ya riƙe.
Cette nouvelle étant parvenue à Joab (qui s'était révolté pour suivre Adonija, bien qu'il ne se fût point révolté pour suivre Absalom), il s'enfuit au tabernacle de l'Éternel, et il saisit les cornes de l'autel.
29 Aka faɗa wa Sarki Solomon cewa Yowab ya gudu zuwa tentin Ubangiji, yana kuma kusa da bagade. Sai Solomon ya umarci Benahiya ɗan Yehohiyada ya ce, “Je ka kashe shi!”
Et on vint dire au roi Salomon: Joab s'est enfui au tabernacle de l'Éternel, et le voilà près de l'autel. Alors Salomon envoya Bénaja, fils de Jéhojada, et lui dit: Va, jette-toi sur lui.
30 Sai Benahiya ya shiga tentin Ubangiji ya ce wa Yowab, “Sarki ya ce, ‘Ka fita!’” Amma Yowab ya amsa ya ce, “A’a, a nan zan mutu.” Sai Benahiya ya ce wa sarki, “Ga yadda Yowab ya amsa mini.”
Bénaja vint donc au tabernacle de l'Éternel, et il lui dit: Ainsi a dit le roi: Sors de là! Et il dit: Non; mais je mourrai ici. Et Bénaja fit rapport au roi, et dit: Joab m'a parlé ainsi, et il m'a ainsi répondu.
31 Sai sarki ya umarci Benahiya ya ce, “Yi kamar yadda ya faɗa. Ka kashe shi, ka kuma binne shi, ka wanke ni da gidan mahaifina daga laifin jini marasa laifin da Yowab ya zubar.
Et le roi lui dit: Fais comme il a dit. Jette-toi sur lui, et l'ensevelis; et tu ôteras de dessus moi et de dessus la maison de mon père le sang que Joab a répandu sans cause.
32 Ubangiji zai sāka masa saboda jinin da ya zubar, domin ba da sanin mahaifina Dawuda ne ya fāɗa wa mutum biyun nan da takobi ba. Dukansu biyu, Abner ɗan Ner, shugaban mayaƙan Isra’ila, da Amasa ɗan Yeter, shugaban mayaƙan Yahuda, mutane ne mafi kyau da kuma mafi adalci fiye da shi.
Et l'Éternel fera retomber son sang sur sa tête; car il s'est jeté sur deux hommes plus justes et meilleurs que lui, et il les a tués avec l'épée, sans que David, mon père, en sût rien: Abner, fils de Ner, chef de l'armée d'Israël, et Amasa, fils de Jéther, chef de l'armée de Juda.
33 Bari alhakin jininsu yă koma a kan Yowab da kuma zuriyarsa har abada. Amma bari salamar Ubangiji tă kasance a kan Dawuda da zuriyarsa, da gidansa, da kuma mulkinsa, har abada.”
Et leur sang retombera sur la tête de Joab, et sur la tête de sa postérité à toujours; mais il y aura paix de la part de l'Éternel, à toujours, pour David, pour sa postérité, pour sa maison et pour son trône.
34 Sai Benahiya ɗan Yehohiyada ya haura ya bugi Yowab, ya kashe shi, ya kuwa binne shi a gidansa a ƙauye.
Bénaja, fils de Jéhojada, monta donc, et se jeta sur lui, et le tua; et on l'ensevelit dans sa maison, au désert.
35 Sai sarki ya sa Benahiya ɗan Yehohiyada ya zama shugaba a bisa mayaƙa a matsayin Yowab, ya kuma sa Zadok firist a wurin Abiyatar.
Alors le roi établit Bénaja, fils de Jéhojada, sur l'armée, à la place de Joab; et le sacrificateur Tsadok fut mis par le roi à la place d'Abiathar.
36 Sa’an nan sarki ya aika aka kawo Shimeyi, ya kuma ce masa, “Ka gina wa kanka gida a nan a Urushalima, ka zauna a ciki, kada ka kuskura ka tafi wani wuri.
Puis le roi envoya appeler Shimeï et lui dit: Bâtis-toi une maison à Jérusalem, et demeures-y, et n'en sors point pour aller de côté ou d'autre.
37 Gama ran da ka fita, ka haye Kwarin Kidron, ka tabbata za ka mutu, alhakin jininka kuwa zai koma kanka.”
Car sache bien qu'au jour où tu en sortiras et passeras le torrent de Cédron, tu mourras sans rémission: ton sang sera sur ta tête.
38 Shimeyi ya amsa wa sarki ya ce, “Abin da ka faɗa yana da kyau. Bawanka zai yi kamar yadda ranka yă daɗe sarki, ya faɗa.” Shimeyi kuwa ya yi zama a Urushalima na dogon lokaci.
Et Shimeï répondit au roi: Cette parole est bonne; ton serviteur fera tout ce qu'a dit le roi, mon seigneur. Ainsi Shimeï demeura un certain temps à Jérusalem.
39 Amma bayan shekaru uku, biyu daga cikin bayin Shimeyi suka gudu zuwa wurin Akish ɗan Ma’aka, sarkin Gat. Aka faɗa wa Shimeyi cewa, “Bayinka suna a Gat.”
Mais il arriva qu'au bout de trois ans, deux serviteurs de Shimeï s'enfuirent vers Akish, fils de Maaca, roi de Gath; et on le rapporta à Shimeï, en disant: Voici, tes serviteurs sont à Gath.
40 Da jin haka, sai ya tashi ya shimfiɗa wa jakinsa abin zama, ya hau, ya tafi Gat wurin Akish domin neman bayinsa. Shimeyi kuwa ya dawo da su gida daga Gat.
Et Shimeï se leva et sella son âne, et s'en alla à Gath vers Akish, pour chercher ses serviteurs. Shimeï s'en alla donc et ramena de Gath ses serviteurs.
41 Da aka faɗa wa Solomon cewa Shimeyi ya bar Urushalima zuwa Gat, har ya dawo.
Or on rapporta à Salomon que Shimeï était allé de Jérusalem à Gath, et qu'il était de retour.
42 Sai sarki ya aika a kawo Shimeyi, ya ce masa, “Ban sa ka rantse da sunan Ubangiji, na kuma ja maka kunne cewa, ‘A ranar da ka kuskura ka bar nan ka tafi wani wuri, ka tabbata za ka mutu ba’? A lokacin ka ce mini, ‘Abin da ka faɗa yana da kyau. Zan kuwa kiyaye.’
Et le roi envoya appeler Shimeï et lui dit: Ne t'avais-je pas fait jurer par l'Éternel, et ne t'avais-je pas protesté, en disant: Sache bien qu'au jour où tu sortiras et où tu iras de côté ou d'autre, tu mourras sans rémission? Et ne me répondis-tu pas: Cette parole est bonne; j'ai entendu?
43 To, me ya sa ba ka kiyaye rantsuwar da ka yi ga Ubangiji, ka kuma yi biyayya da umarnin da na ba ka ba?”
Pourquoi donc n'as-tu pas gardé le serment de l'Éternel et le commandement que je t'avais donné?
44 Sarki ya ce wa Shimeyi, “Ka sani a zuciyarka dukan muguntar da ka yi wa mahaifina Dawuda. Yanzu Ubangiji zai sāka maka saboda muguntarka.
Et le roi dit à Shimeï: Tu sais tout le mal que tu as fait à David, mon père, et tu en es convaincu dans ton cœur; aussi l'Éternel fait retomber ta méchanceté sur ta tête.
45 Amma za a yi wa Sarki Solomon albarka, sarautar Dawuda kuma za tă kasance a tsare a gaban Ubangiji har abada.”
Mais le roi Salomon sera béni, et le trône de David sera affermi devant l'Éternel à jamais.
46 Sai sarki ya umarci Benahiya ɗan Yehohiyada, yă fita, yă bugi Shimeyi, yă kashe shi. Ya kuwa kashe shi. Mulki kuwa ya kahu sosai a hannun Solomon.
Et le roi donna ordre à Bénaja, fils de Jéhojada, qui sortit et se jeta sur lui; et il mourut. Et la royauté fut affermie entre les mains de Salomon.

< 1 Sarakuna 2 >