< 1 Sarakuna 2 >

1 Da lokacin mutuwar Dawuda ya yi kusa, sai ya gargaɗe Solomon ɗansa, ya ce,
Le jour où David allait mourir était proche; et il parla à son fils Salomon en ces termes:
2 “Ina gab da bin hanyar da kowa a duniya zai bi. Saboda haka ka yi ƙarfin hali, ka nuna kanka namiji,
Je m'en vais dans la voie de toute la terre; quant â toi, sois fort et agis en homme.
3 ka kiyaye abin da Ubangiji Allahnka yake bukata. Yi tafiya a hanyoyinsa, ka kiyaye ƙa’idodi, da umarnai, da dokoki, da kuma farillansa, kamar yadda suke a rubuce a Dokar Musa, don ka yi nasara a cikin kome da za ka yi, da kuma inda za ka tafi.
Observe les commandements du Seigneur ton Dieu, afin de marcher dans ses voies, de garder ses commandements, sa justice, ses jugements, et les préceptes qui sont écrits en la loi de Moïse; conduis-toi sagement en toutes choses, comme je te l'ai prescrit;
4 Ubangiji kuwa zai kiyaye alkawarinsa gare ni da ya ce, ‘In zuriyarka suka lura da yadda suke rayuwa, in kuma suka yi tafiya da aminci a gabana da dukan zuciyarsu, da kuma dukan ransu, ba za ka kāsa samun mutum a kujerar sarautar Isra’ila ba.’
Afin que le Seigneur confirme la parole qu'il a dite: Si tes fils sont attentifs à suivre leur voie, devant moi, dans la vérité et de tout leur cœur, jamais il ne manquera d'homme issu de toi pour monter sur le trône d'Israël.
5 “Yanzu fa, kai kanka ka san abin da Yowab ɗan Zeruhiya ya yi mini. Abin da ya yi wa shugabanni biyun nan na mayaƙan Isra’ila, wato, Abner ɗan Ner, da Amasa ɗan Yeter. Ya kashe su, ya kuma zub da jininsu a lokacin salama sai ka ce a fage yaƙi, da wannan jini ya yi ɗamara a gindinsa, ya kuma sa takalma a ƙafafunsa.
Or, tu sais ce que m'a fait Joab, fils de Sarvia; tu sais comment il a traité les deux chefs de l'armée d'Israël: Abner, fils de Ner, et Amessaï, fils de Jéther. Il les a tués; le sang, réservé au combat, il l'a fait couler pendant la paix; il a versé le sang innocent sur la ceinture qui ceignait ses reins, et sur les sandales qui chaussaient ses pieds.
6 Ka yi da shi gwargwadon hikimarka, amma kada ka bari yă gangara kabari da furfura cikin salama. (Sheol h7585)
Tu feras ce que t'inspirera ta sagesse, et tu ne laisseras pas sa vieillesse descendre en paix au tombeau. (Sheol h7585)
7 “Amma ka yi alheri ga’ya’yan Barzillai mutumin Gileyad, ka sa su kasance a cikin waɗanda suke ci a teburinka. Sun goyi bayana sa’ad da nake gudu daga ɗan’uwanka Absalom.
Et tu seras bienveillant pour les fils de Berzelli le Galaadite; ils seront de ceux qui mangeront à ta table, car c'est ainsi qu'ils ont agi envers moi quand je fuyais devant Absalon ton frère.
8 “Ka tuna, akwai kuma Shimeyi ɗan Gera, mutumin Benyamin daga Bahurim, wanda ya yi ta yin mini muguwar la’ana a ranar da na tafi Mahanayim. Sa’ad da ya gangara ya same ni a Urdun, na rantse masa da sunan Ubangiji na ce, ‘Ba zan kashe ka da takobi ba.’
Tu vois avec toi Sémeï, fils de Géra, de la famille de Jémini de Bathurim; c'est lui qui m'a poursuivi de malédictions bien amères, le jour où je m'en allais au camp; à mon retour, il est venu à ma rencontre vers le Jourdain; je lui ai alors prêté serment au nom du Seigneur, et j'ai dit: Je ne te ferai point mourir par l'épée.
9 Amma yanzu, kada ka ɗauke shi marar laifi. Kai mutum ne mai hikima; za ka san abin da za ka yi da shi. Ka kawo furfuransa zuwa kabari da jini.” (Sheol h7585)
Tu ne l'innocenteras point, car tu es un homme sage; tu sauras comment le traiter, et tu feras descendre sa vieillesse au tombeau dans le sang. (Sheol h7585)
10 Sa’an nan Dawuda ya huta tare da kakanninsa. Sai aka binne shi a Birnin Dawuda.
Et David s'endormit avec ses pères, et il fut enseveli dans la ville de David.
11 Ya yi sarauta shekaru arba’in a bisa Isra’ila. Wato, shekaru bakwai a Hebron da kuma talatin da uku a Urushalima.
Les jours du règne de David sur Israël formèrent quarante ans; il régna sept ans à Hébron et trente-trois ans à Jérusalem.
12 Solomon kuwa ya zauna a kan kujerar sarautar mahaifinsa Dawuda, mulkinsa kuwa ya kahu sosai.
Et Salomon s'assit sur le trône de David son père, et son règne était parfaitement préparé.
13 To, sai Adoniya, ɗan Haggit ya tafi wurin Batsheba mahaifiyar Solomon. Ita kuwa ta tambaye shi ta ce, “Lafiya?” Ya amsa ya ce, “I, lafiya.”
Ensuite, Adonias, fils d'Aggith, entra chez Bethsabée, mère de Salomon; il se prosterna devant elle, et elle lui dit: En entrant, nous apportes-tu la paix? Et il répondit: La paix;
14 Sa’an nan ya ƙara da cewa, “Ina da ɗan wani abin da zan faɗa miki.” Ta ce, “Faɗa.”
J'ai à te dire un mot. Parle, reprit-elle.
15 Sai ya ce, “Kamar yadda kika sani, mulkin nan nawa ne. Dukan Isra’ila suna ɗaukana a matsayin sarki. Amma abubuwa suka canja, sai mulkin ya koma ga ɗan’uwana; gama ya zo masa daga Ubangiji ne.
Tu sais, lui dit-il, que la royauté m'appartenait, et que tout Israël avait jeté les yeux sur moi pour que je régnasse; mais la royauté a été détournée de moi, et elle a passé à mon frère, parce que telle était la volonté du Seigneur.
16 Yanzu ina da roƙo guda da zan yi gare ki. Kada ki hana mini.” Ta ce, “Sai ka faɗa.”
Maintenant, j'ai à te faire une seule demande; ne détourne pas de moi ton visage. Et Bethsabée lui dit: Parle.
17 Sai ya ci gaba, “In kin yarda, ki yi magana da Sarki Solomon, gama ba zai ƙi jinki ba, ki ce yă ba ni yarinyan nan, Abishag, mutuniyar Shunam, tă zama matata.”
Et il continua: Parle au roi Salomon; car il ne détournera pas de toi son visage; qu'il me donne pour femme Abisag la Sunamite.
18 Batsheba ta ce, “Da kyau, zan yi magana da sarki dominka.”
A quoi Bethsabée reprit: Bien; je parlerai au roi en ta faveur.
19 Sai Batsheba ta tafi wurin Sarki Solomon don tă yi masa magana a kan Adoniya. Sarki ya miƙe tsaye don yă sadu da ita, ya rusuna mata, ya kuma zauna a kujerar sarautarsa. Ya sa aka kawo wa mahaifiyar sarki kujerar sarauta, ta kuwa zauna a gefen damansa.
Bethsabée alla trouver le roi Salomon, afin de lui parler en faveur d'Adonias. Le roi se leva, alla au-devant d'elle, la baisa et s'assit sur son trône; puis on plaça un trône pour la mère du roi, et elle s'assit à sa droite.
20 Ta ce, “Ina da ɗan roƙon da zan nema ka yi mini. Ina fata ba za ka hana ni ba.” Sai sarki ya amsa ya ce, “Mahaifiyata, sai ki faɗa in ji, ba zan hana miki ba.”
Et elle lui dit: J'ai à te faire une petite demande; ne repousse pas mon visage. Et le roi répondit: Demande, ma mère, et je ne te repousserai point.
21 Saboda haka sai ta ce, “Ka sa a ba wa ɗan’uwanka Adoniya, Abishag mutuniyar Shunam tă zama matarsa.”
Et elle dit: Que la Sunamite Abisag soit donnée pour femme à ton frère Adonias.
22 Sarki Solomon ya amsa wa mahaifiyarsa ya ce, “Me ya sa kika roƙar wa Adoniya Abishag mutuniyar Shunam kawai? Ki ma sa a ba shi mulkin mana. Ai, shi yayana ne. I, ki roƙa dominsa, da domin Abiyatar firist, da kuma domin Yowab ɗan Zeruhiya mana!”
Le roi Salomon répondit, et il dit à sa mère: Pourquoi as-tu demandé Abisag pour Adonias? Demande aussi pour lui la royauté, car il est mon frère, il est plus âgé que moi, et il a pour compagnon Abiathar le prêtre, et Joab, fils de Sarvia, général en chef.
23 Sai Sarki Solomon ya rantse da sunan Ubangiji ya ce, “Bari Allah yă yi mini hukunci mai tsanani, idan ban sa Adoniya ya biya wannan roƙo da ransa ba!
Et le roi jura au nom du Seigneur, disant: Que le Seigneur me punisse, et qu'il me punisse encore, si, en faisant cette demande, Adonias n'a pas parlé contre sa vie.
24 Yanzu kuwa, muddin Ubangiji yana a raye, shi wanda ya kafa ni sosai a kan kujerar sarautar mahaifina Dawuda, ya kuma kafa mini mulki kamar yadda ya yi alkawari; za a kashe Adoniya yau!”
Maintenant, vive le Seigneur qui m'a préparé, qui m'a placé sur le trône de David mon père, qui a établi ma maison comme il l'avait promis! aujourd'hui même Adonias mourra.
25 Saboda haka Sarki Solomon ya umarci Benahiya ɗan Yehohiyada yă kashe Adoniya; ya kuwa kashe shi.
Salomon confia l'exécution de ce dessein à Banaïas, fils de Joïada. Celui- ci tua Adonias, qui mourut le jour même.
26 Ga Abiyatar firist kuwa sarki ya ce, “Tafi gonarka a Anatot. Ka cancanci ka mutu, amma ba zan kashe ka yanzu ba, domin ka ɗauki akwatin alkawarin Ubangiji Mai Iko Duka a gaban mahaifina Dawuda, ka kuma sha wahala tare mahaifina.”
Et le roi dit à Abiathar le prêtre: Retourne vite à ton champ en Astaroth, car tu es, en ce jour-ci, un homme digne de mort; toutefois, je ne te ferai point périr, parce que tu as porté devant mon père l'arche de l'alliance du Seigneur, et que tu as souffert en tout ce qu'a souffert David.
27 Saboda haka Solomon ya cire Abiyatar daga aikin firist na Ubangiji, ya cika maganar da Ubangiji ya yi a Shilo game da gidan Eli.
Et Salomon interdit le sacerdoce à Abiathar, pour que s'accomplît la parole que le Seigneur avait prononcée contre la maison d'Héli.
28 Sa’ad da labarin ya kai wurin Yowab, wanda ya haɗa kai da Adoniya, ko da yake bai haɗa kai da Absalom ba, sai ya gudu zuwa tentin Ubangiji, ya kama ƙahonin bagade ya riƙe.
La nouvelle en arriva jusqu'à Joab, fils de Sarvia; or, Joab avait été l'un des convives d'Adonias, et il ne s'était point rapproché de Salomon. Joab se réfugia dans le tabernacle du Seigneur, et il embrassa la corne de l'autel.
29 Aka faɗa wa Sarki Solomon cewa Yowab ya gudu zuwa tentin Ubangiji, yana kuma kusa da bagade. Sai Solomon ya umarci Benahiya ɗan Yehohiyada ya ce, “Je ka kashe shi!”
Et l'on vint l'annoncer au roi Salomon; on lui dit: Joab s'est réfugié dans le tabernacle du Seigneur, et le voilà qui tient la corne de l'autel. Aussitôt, Salomon envoya auprès de Joab, et il lui dit: Que t'arrive-t-il, pour que tu te réfugies à l'autel? Joab répondit: J'ai eu crainte de toi, et je me suis réfugié auprès du Seigneur. Et Salomon envoya Banaïas, fils de Joïada, disant: Va, tue-le, et ensevelis-le.
30 Sai Benahiya ya shiga tentin Ubangiji ya ce wa Yowab, “Sarki ya ce, ‘Ka fita!’” Amma Yowab ya amsa ya ce, “A’a, a nan zan mutu.” Sai Benahiya ya ce wa sarki, “Ga yadda Yowab ya amsa mini.”
Banaïas, fils de Joïada, alla trouver Joab dans le tabernacle du Seigneur, et il lui dit: Voici ce que dit le roi: Sors; mais Joab répondit: Je ne sortirai point, c'est ici que je mourrai. Banaïas retourna chez le roi, et il lui dit: Voici ce que j'ai dit à Joab, voici ce qu'il m'a répondu.
31 Sai sarki ya umarci Benahiya ya ce, “Yi kamar yadda ya faɗa. Ka kashe shi, ka kuma binne shi, ka wanke ni da gidan mahaifina daga laifin jini marasa laifin da Yowab ya zubar.
Le roi reprit: Va et fais-lui comme il a dit: Tue-le, ensevelis-le, et tu auras aujourd'hui détourné de moi et de la maison de mon père le sang que Joab a versé sans motif.
32 Ubangiji zai sāka masa saboda jinin da ya zubar, domin ba da sanin mahaifina Dawuda ne ya fāɗa wa mutum biyun nan da takobi ba. Dukansu biyu, Abner ɗan Ner, shugaban mayaƙan Isra’ila, da Amasa ɗan Yeter, shugaban mayaƙan Yahuda, mutane ne mafi kyau da kuma mafi adalci fiye da shi.
Le Seigneur a ramené sur sa tête le sang de son iniquité, car il est allé à la rencontre de deux hommes plus justes et meilleurs que lui; il les a fait périr par le glaive, et mon père David ne savait rien du meurtre d'Abner, fils de Ner, général en chef d'Israël, ni du meurtre d'Amessaï, fils de Jéther, général en chef de Juda.
33 Bari alhakin jininsu yă koma a kan Yowab da kuma zuriyarsa har abada. Amma bari salamar Ubangiji tă kasance a kan Dawuda da zuriyarsa, da gidansa, da kuma mulkinsa, har abada.”
Leur sang est retombé sur sa tête, et sur la tête de sa postérité à jamais. Que la paix du Seigneur soit toujours avec David, avec sa race, avec sa maison et avec son trône.
34 Sai Benahiya ɗan Yehohiyada ya haura ya bugi Yowab, ya kashe shi, ya kuwa binne shi a gidansa a ƙauye.
Et Banaïas, fils de Joïada, alla retrouver Joab; il le tua, et il l'inhuma dans sa maison près du désert.
35 Sai sarki ya sa Benahiya ɗan Yehohiyada ya zama shugaba a bisa mayaƙa a matsayin Yowab, ya kuma sa Zadok firist a wurin Abiyatar.
Le roi, à sa place, donna le commandement de l'armée à Banaïas, et la royauté fut affermie dans Jérusalem. Sadoc fut premier prêtre à la place d'Abiathar.
36 Sa’an nan sarki ya aika aka kawo Shimeyi, ya kuma ce masa, “Ka gina wa kanka gida a nan a Urushalima, ka zauna a ciki, kada ka kuskura ka tafi wani wuri.
Et le roi appela Semeï, et il lui dit: Bâtis pour toi une maison dans Jérusalem, demeures-y, et de là tu n'iras en aucun lieu.
37 Gama ran da ka fita, ka haye Kwarin Kidron, ka tabbata za ka mutu, alhakin jininka kuwa zai koma kanka.”
Le jour où tu en sortirais, où tu passerais le torrent de Cédron, sache-le bien, tu mourrais de mort; et ton sang retomberait sur ta tête. Et le roi, ce jour-là, lui fit prêter serment.
38 Shimeyi ya amsa wa sarki ya ce, “Abin da ka faɗa yana da kyau. Bawanka zai yi kamar yadda ranka yă daɗe sarki, ya faɗa.” Shimeyi kuwa ya yi zama a Urushalima na dogon lokaci.
Ensuite, Sémeï dit au roi: La parole que tu as dite est bonne, ô roi mon maître, ainsi fera ton serviteur. Et Sémeï demeura trois ans à Jérusalem.
39 Amma bayan shekaru uku, biyu daga cikin bayin Shimeyi suka gudu zuwa wurin Akish ɗan Ma’aka, sarkin Gat. Aka faɗa wa Shimeyi cewa, “Bayinka suna a Gat.”
Après trois ans, deux serviteurs de Sémeï s'enfuirent chez Achis, fils de Maacha, roi de Geth. On l'apprit à Sémeï en lui disant: Voilà tes serviteurs à Geth.
40 Da jin haka, sai ya tashi ya shimfiɗa wa jakinsa abin zama, ya hau, ya tafi Gat wurin Akish domin neman bayinsa. Shimeyi kuwa ya dawo da su gida daga Gat.
Et Sémeï se leva, bâta son ânesse et, s'en alla chez Achis à Geth, pour réclamer ses deux serviteurs; puis il revint, et les ramena de Geth.
41 Da aka faɗa wa Solomon cewa Shimeyi ya bar Urushalima zuwa Gat, har ya dawo.
Or, on l'apprit à Salomon en lui disant: Sémeï est allé de Jérusalem à Geth, et il a ramené ses serviteurs.
42 Sai sarki ya aika a kawo Shimeyi, ya ce masa, “Ban sa ka rantse da sunan Ubangiji, na kuma ja maka kunne cewa, ‘A ranar da ka kuskura ka bar nan ka tafi wani wuri, ka tabbata za ka mutu ba’? A lokacin ka ce mini, ‘Abin da ka faɗa yana da kyau. Zan kuwa kiyaye.’
Aussitôt, le roi envoya querir Sémeï, et il lui dit: Ne t'ai-je point fait prêter serment par le Seigneur, ne t'ai-je pas attesté, disant: Le jour où tu sortiras de Jérusalem, où tu iras à droite ou à gauche, sache-le bien, tu mourras?
43 To, me ya sa ba ka kiyaye rantsuwar da ka yi ga Ubangiji, ka kuma yi biyayya da umarnin da na ba ka ba?”
Pourquoi n'as-tu point gardé le serment du Seigneur, et le commandement que je t'avais donné?
44 Sarki ya ce wa Shimeyi, “Ka sani a zuciyarka dukan muguntar da ka yi wa mahaifina Dawuda. Yanzu Ubangiji zai sāka maka saboda muguntarka.
Et le roi ajouta: Tu connais, ton cœur sait tout le mal que tu as fait à David mon père; le Seigneur a fait retomber ta méchanceté sur ta tête.
45 Amma za a yi wa Sarki Solomon albarka, sarautar Dawuda kuma za tă kasance a tsare a gaban Ubangiji har abada.”
Cependant, Salomon est béni, et le trône de David est affermi devant le Seigneur à jamais.
46 Sai sarki ya umarci Benahiya ɗan Yehohiyada, yă fita, yă bugi Shimeyi, yă kashe shi. Ya kuwa kashe shi. Mulki kuwa ya kahu sosai a hannun Solomon.
Et le roi donna ses ordres à Banaïas, fils de Joïada, qui sortit avec Sémeï et le tua. Le roi Salomon était doué d'une grande intelligence et d'une grande sagesse.

< 1 Sarakuna 2 >