< 1 Sarakuna 2 >

1 Da lokacin mutuwar Dawuda ya yi kusa, sai ya gargaɗe Solomon ɗansa, ya ce,
Les jours de David approchaient où il devait mourir, et il donna cet ordre à Salomon, son fils:
2 “Ina gab da bin hanyar da kowa a duniya zai bi. Saboda haka ka yi ƙarfin hali, ka nuna kanka namiji,
« Je m'en vais par le chemin de toute la terre. Sois donc fort, et montre-toi un homme;
3 ka kiyaye abin da Ubangiji Allahnka yake bukata. Yi tafiya a hanyoyinsa, ka kiyaye ƙa’idodi, da umarnai, da dokoki, da kuma farillansa, kamar yadda suke a rubuce a Dokar Musa, don ka yi nasara a cikin kome da za ka yi, da kuma inda za ka tafi.
et garde les instructions de l'Éternel, ton Dieu, pour marcher dans ses voies, pour observer ses lois, ses commandements, ses ordonnances et ses témoignages, selon ce qui est écrit dans la loi de Moïse, afin que tu prospères dans tout ce que tu fais et partout où tu te tournes.
4 Ubangiji kuwa zai kiyaye alkawarinsa gare ni da ya ce, ‘In zuriyarka suka lura da yadda suke rayuwa, in kuma suka yi tafiya da aminci a gabana da dukan zuciyarsu, da kuma dukan ransu, ba za ka kāsa samun mutum a kujerar sarautar Isra’ila ba.’
Alors Yahvé accomplira la parole qu'il a prononcée à mon sujet, en disant: « Si tes enfants prennent garde à leur voie, pour marcher devant moi dans la vérité, de tout leur cœur et de toute leur âme, tu ne manqueras pas, dit-il, d'un homme sur le trône d'Israël ».
5 “Yanzu fa, kai kanka ka san abin da Yowab ɗan Zeruhiya ya yi mini. Abin da ya yi wa shugabanni biyun nan na mayaƙan Isra’ila, wato, Abner ɗan Ner, da Amasa ɗan Yeter. Ya kashe su, ya kuma zub da jininsu a lokacin salama sai ka ce a fage yaƙi, da wannan jini ya yi ɗamara a gindinsa, ya kuma sa takalma a ƙafafunsa.
Vous savez d'ailleurs ce que m'a fait Joab, fils de Tseruja, ce qu'il a fait aux deux chefs des armées d'Israël, à Abner, fils de Ner, et à Amasa, fils de Jéther, qu'il a tués, et qu'il a fait couler en paix le sang de la guerre, en mettant le sang de la guerre sur la ceinture qu'il avait à la taille et sur les sandales qu'il avait aux pieds.
6 Ka yi da shi gwargwadon hikimarka, amma kada ka bari yă gangara kabari da furfura cikin salama. (Sheol h7585)
Fais donc selon ta sagesse, et ne laisse pas sa tête grise descendre en paix au séjour des morts. (Sheol h7585)
7 “Amma ka yi alheri ga’ya’yan Barzillai mutumin Gileyad, ka sa su kasance a cikin waɗanda suke ci a teburinka. Sun goyi bayana sa’ad da nake gudu daga ɗan’uwanka Absalom.
Mais fais preuve de bonté envers les fils de Barzillai, le Galaadite, et qu'ils soient du nombre de ceux qui mangent à ta table, car c'est ainsi qu'ils sont venus à moi lorsque j'ai fui Absalom, ton frère.
8 “Ka tuna, akwai kuma Shimeyi ɗan Gera, mutumin Benyamin daga Bahurim, wanda ya yi ta yin mini muguwar la’ana a ranar da na tafi Mahanayim. Sa’ad da ya gangara ya same ni a Urdun, na rantse masa da sunan Ubangiji na ce, ‘Ba zan kashe ka da takobi ba.’
« Voici qu'il y a avec toi Shimei, fils de Gera, Benjamite de Bahurim, qui m'a maudit d'une manière redoutable le jour où je suis allé à Mahanaïm; mais il est descendu à ma rencontre au Jourdain, et je lui ai juré par Yahvé: 'Je ne te ferai pas mourir par l'épée'.
9 Amma yanzu, kada ka ɗauke shi marar laifi. Kai mutum ne mai hikima; za ka san abin da za ka yi da shi. Ka kawo furfuransa zuwa kabari da jini.” (Sheol h7585)
Maintenant donc, ne le tiens pas pour innocent, car tu es un homme sage; tu sauras ce que tu dois lui faire, et tu feras descendre au séjour des morts sa tête grise dans le sang. » (Sheol h7585)
10 Sa’an nan Dawuda ya huta tare da kakanninsa. Sai aka binne shi a Birnin Dawuda.
David se coucha avec ses pères, et il fut enterré dans la ville de David.
11 Ya yi sarauta shekaru arba’in a bisa Isra’ila. Wato, shekaru bakwai a Hebron da kuma talatin da uku a Urushalima.
Les jours où David régna sur Israël furent de quarante ans; il régna sept ans à Hébron, et il régna trente-trois ans à Jérusalem.
12 Solomon kuwa ya zauna a kan kujerar sarautar mahaifinsa Dawuda, mulkinsa kuwa ya kahu sosai.
Salomon s'assit sur le trône de David, son père, et son royaume fut solidement établi.
13 To, sai Adoniya, ɗan Haggit ya tafi wurin Batsheba mahaifiyar Solomon. Ita kuwa ta tambaye shi ta ce, “Lafiya?” Ya amsa ya ce, “I, lafiya.”
Alors Adonija, fils de Haggith, vint auprès de Bethsabée, mère de Salomon. Elle dit: « Viens-tu paisiblement? » Il a dit: « pacifiquement ».
14 Sa’an nan ya ƙara da cewa, “Ina da ɗan wani abin da zan faɗa miki.” Ta ce, “Faɗa.”
Il dit en outre: « J'ai quelque chose à vous dire. » Elle a dit: « Dis-le. »
15 Sai ya ce, “Kamar yadda kika sani, mulkin nan nawa ne. Dukan Isra’ila suna ɗaukana a matsayin sarki. Amma abubuwa suka canja, sai mulkin ya koma ga ɗan’uwana; gama ya zo masa daga Ubangiji ne.
Il dit: « Vous savez que le royaume était à moi, et que tout Israël s'est tourné vers moi pour que je règne. Mais le royaume s'est retourné et est devenu celui de mon frère, car il lui a été donné par Yahvé.
16 Yanzu ina da roƙo guda da zan yi gare ki. Kada ki hana mini.” Ta ce, “Sai ka faɗa.”
Maintenant, je te demande une chose. Ne me renie pas. » Elle lui a dit: « Dis-le. »
17 Sai ya ci gaba, “In kin yarda, ki yi magana da Sarki Solomon, gama ba zai ƙi jinki ba, ki ce yă ba ni yarinyan nan, Abishag, mutuniyar Shunam, tă zama matata.”
Il dit: « Parle au roi Salomon, car il ne te dira pas non, pour qu'il me donne pour femme Abishag, la Sunamite. »
18 Batsheba ta ce, “Da kyau, zan yi magana da sarki dominka.”
Bethsabée dit: « Très bien. Je parlerai en ton nom au roi. »
19 Sai Batsheba ta tafi wurin Sarki Solomon don tă yi masa magana a kan Adoniya. Sarki ya miƙe tsaye don yă sadu da ita, ya rusuna mata, ya kuma zauna a kujerar sarautarsa. Ya sa aka kawo wa mahaifiyar sarki kujerar sarauta, ta kuwa zauna a gefen damansa.
Bethsabée alla donc vers le roi Salomon, pour lui parler en faveur d'Adonija. Le roi se leva à sa rencontre, se prosterna devant elle, s'assit sur son trône et fit placer un trône pour la mère du roi, et elle s'assit à sa droite.
20 Ta ce, “Ina da ɗan roƙon da zan nema ka yi mini. Ina fata ba za ka hana ni ba.” Sai sarki ya amsa ya ce, “Mahaifiyata, sai ki faɗa in ji, ba zan hana miki ba.”
Elle dit alors: « Je te demande une petite requête; ne me refuse pas. » Le roi lui dit: « Demande, ma mère, car je ne te refuserai pas. »
21 Saboda haka sai ta ce, “Ka sa a ba wa ɗan’uwanka Adoniya, Abishag mutuniyar Shunam tă zama matarsa.”
Elle dit: « Qu'Abishag, la Sunamite, soit donnée pour femme à Adonija, ton frère. »
22 Sarki Solomon ya amsa wa mahaifiyarsa ya ce, “Me ya sa kika roƙar wa Adoniya Abishag mutuniyar Shunam kawai? Ki ma sa a ba shi mulkin mana. Ai, shi yayana ne. I, ki roƙa dominsa, da domin Abiyatar firist, da kuma domin Yowab ɗan Zeruhiya mana!”
Le roi Salomon répondit à sa mère: « Pourquoi demandes-tu à Abischag, la Sunamite, pour Adonija? Demande pour lui aussi le royaume, car il est mon frère aîné; pour lui aussi, pour le prêtre Abiathar, et pour Joab, fils de Tseruja. »
23 Sai Sarki Solomon ya rantse da sunan Ubangiji ya ce, “Bari Allah yă yi mini hukunci mai tsanani, idan ban sa Adoniya ya biya wannan roƙo da ransa ba!
Alors le roi Salomon jura par Yahvé, en disant: « Que Dieu me fasse ainsi, et plus encore, si Adonija n'a pas prononcé cette parole contre sa propre vie.
24 Yanzu kuwa, muddin Ubangiji yana a raye, shi wanda ya kafa ni sosai a kan kujerar sarautar mahaifina Dawuda, ya kuma kafa mini mulki kamar yadda ya yi alkawari; za a kashe Adoniya yau!”
Maintenant que Yahvé est vivant, lui qui m'a affermi et m'a mis sur le trône de mon père David, et qui m'a fait une maison comme il l'avait promis, Adonija sera mis à mort aujourd'hui. »
25 Saboda haka Sarki Solomon ya umarci Benahiya ɗan Yehohiyada yă kashe Adoniya; ya kuwa kashe shi.
Le roi Salomon envoya Benaja, fils de Jehojada, qui tomba sur lui, de sorte qu'il mourut.
26 Ga Abiyatar firist kuwa sarki ya ce, “Tafi gonarka a Anatot. Ka cancanci ka mutu, amma ba zan kashe ka yanzu ba, domin ka ɗauki akwatin alkawarin Ubangiji Mai Iko Duka a gaban mahaifina Dawuda, ka kuma sha wahala tare mahaifina.”
Le roi dit au prêtre Abiathar: « Va à Anathoth, dans tes champs, car tu es digne de mourir. Mais je ne te ferai pas mourir maintenant, parce que tu as porté l'arche du Seigneur Yahvé devant David, mon père, et parce que tu as été affligé dans tout ce que mon père a été affligé. »
27 Saboda haka Solomon ya cire Abiyatar daga aikin firist na Ubangiji, ya cika maganar da Ubangiji ya yi a Shilo game da gidan Eli.
Salomon chassa donc Abiathar de la fonction de prêtre de l'Éternel, afin d'accomplir la parole de l'Éternel qu'il avait prononcée au sujet de la maison d'Éli à Silo.
28 Sa’ad da labarin ya kai wurin Yowab, wanda ya haɗa kai da Adoniya, ko da yake bai haɗa kai da Absalom ba, sai ya gudu zuwa tentin Ubangiji, ya kama ƙahonin bagade ya riƙe.
Cette nouvelle parvint à Joab, car Joab avait suivi Adonija, bien qu'il n'eût pas suivi Absalom. Joab s'enfuit vers la tente de l'Éternel et s'accrocha aux cornes de l'autel.
29 Aka faɗa wa Sarki Solomon cewa Yowab ya gudu zuwa tentin Ubangiji, yana kuma kusa da bagade. Sai Solomon ya umarci Benahiya ɗan Yehohiyada ya ce, “Je ka kashe shi!”
On dit au roi Salomon: « Joab s'est enfui vers la tente de l'Éternel, et voici qu'il est près de l'autel. » Alors Salomon envoya Benaja, fils de Jehoiada, en disant: « Va, tombe sur lui. »
30 Sai Benahiya ya shiga tentin Ubangiji ya ce wa Yowab, “Sarki ya ce, ‘Ka fita!’” Amma Yowab ya amsa ya ce, “A’a, a nan zan mutu.” Sai Benahiya ya ce wa sarki, “Ga yadda Yowab ya amsa mini.”
Benaja vint à la tente de Yahvé et lui dit: « Le roi dit: « Sors! »" Il a dit: « Non; mais je mourrai ici. » Benaiah rapporta de nouveau la parole au roi, en disant: « Voici ce que Joab a dit, et voici comment il m'a répondu. »
31 Sai sarki ya umarci Benahiya ya ce, “Yi kamar yadda ya faɗa. Ka kashe shi, ka kuma binne shi, ka wanke ni da gidan mahaifina daga laifin jini marasa laifin da Yowab ya zubar.
Le roi lui dit: « Fais ce qu'il a dit, tombe sur lui et enterre-le, afin d'ôter de moi et de la maison de mon père le sang que Joab a versé sans raison.
32 Ubangiji zai sāka masa saboda jinin da ya zubar, domin ba da sanin mahaifina Dawuda ne ya fāɗa wa mutum biyun nan da takobi ba. Dukansu biyu, Abner ɗan Ner, shugaban mayaƙan Isra’ila, da Amasa ɗan Yeter, shugaban mayaƙan Yahuda, mutane ne mafi kyau da kuma mafi adalci fiye da shi.
Yahvé fera retomber son sang sur sa propre tête, car il est tombé sur deux hommes plus justes et meilleurs que lui, et les a tués par l'épée, sans que mon père David le sache: Abner, fils de Ner, chef de l'armée d'Israël, et Amasa, fils de Jether, chef de l'armée de Juda.
33 Bari alhakin jininsu yă koma a kan Yowab da kuma zuriyarsa har abada. Amma bari salamar Ubangiji tă kasance a kan Dawuda da zuriyarsa, da gidansa, da kuma mulkinsa, har abada.”
Ainsi leur sang retombera sur la tête de Joab et sur la tête de sa descendance pour toujours. Mais pour David, pour sa descendance, pour sa maison et pour son trône, il y aura une paix éternelle de la part de Yahvé. »
34 Sai Benahiya ɗan Yehohiyada ya haura ya bugi Yowab, ya kashe shi, ya kuwa binne shi a gidansa a ƙauye.
Alors Benaja, fils de Jehojada, monta, se jeta sur lui et le tua; et il fut enterré dans sa maison, dans le désert.
35 Sai sarki ya sa Benahiya ɗan Yehohiyada ya zama shugaba a bisa mayaƙa a matsayin Yowab, ya kuma sa Zadok firist a wurin Abiyatar.
Le roi remit Benaja, fils de Jehojada, à sa place dans l'armée, et le roi mit le sacrificateur Tsadok à la place d'Abiathar.
36 Sa’an nan sarki ya aika aka kawo Shimeyi, ya kuma ce masa, “Ka gina wa kanka gida a nan a Urushalima, ka zauna a ciki, kada ka kuskura ka tafi wani wuri.
Le roi fit appeler Shimei et lui dit: « Construis-toi une maison à Jérusalem, et habite là, et ne va pas ailleurs.
37 Gama ran da ka fita, ka haye Kwarin Kidron, ka tabbata za ka mutu, alhakin jininka kuwa zai koma kanka.”
Car le jour où tu sortiras et passeras le torrent de Cédron, sache que tu mourras certainement. Ton sang sera sur ta tête. »
38 Shimeyi ya amsa wa sarki ya ce, “Abin da ka faɗa yana da kyau. Bawanka zai yi kamar yadda ranka yă daɗe sarki, ya faɗa.” Shimeyi kuwa ya yi zama a Urushalima na dogon lokaci.
Shimei dit au roi: « Ce que tu dis est bien. Ce que mon seigneur le roi a dit, ton serviteur le fera aussi. » Shimei vécut de nombreux jours à Jérusalem.
39 Amma bayan shekaru uku, biyu daga cikin bayin Shimeyi suka gudu zuwa wurin Akish ɗan Ma’aka, sarkin Gat. Aka faɗa wa Shimeyi cewa, “Bayinka suna a Gat.”
Au bout de trois ans, deux des esclaves de Shimei s'enfuirent chez Akish, fils de Maaca, roi de Gath. Ils en informèrent Shimei en disant: « Voici tes esclaves à Gath. »
40 Da jin haka, sai ya tashi ya shimfiɗa wa jakinsa abin zama, ya hau, ya tafi Gat wurin Akish domin neman bayinsa. Shimeyi kuwa ya dawo da su gida daga Gat.
Shimei se leva, sella son âne et alla à Gath, chez Akish, pour chercher ses esclaves; et Shimei alla chercher ses esclaves à Gath.
41 Da aka faɗa wa Solomon cewa Shimeyi ya bar Urushalima zuwa Gat, har ya dawo.
On raconta à Salomon que Shimei était allé de Jérusalem à Gath, et qu'il était revenu.
42 Sai sarki ya aika a kawo Shimeyi, ya ce masa, “Ban sa ka rantse da sunan Ubangiji, na kuma ja maka kunne cewa, ‘A ranar da ka kuskura ka bar nan ka tafi wani wuri, ka tabbata za ka mutu ba’? A lokacin ka ce mini, ‘Abin da ka faɗa yana da kyau. Zan kuwa kiyaye.’
Le roi fit appeler Shimei et lui dit: « Ne t'ai-je pas adjuré par l'Éternel et ne t'ai-je pas averti en disant: « Sache bien que le jour où tu sortiras et marcheras ailleurs, tu mourras certainement? » Tu m'as répondu: « La parole que j'ai entendue est bonne. »
43 To, me ya sa ba ka kiyaye rantsuwar da ka yi ga Ubangiji, ka kuma yi biyayya da umarnin da na ba ka ba?”
Pourquoi donc n'as-tu pas respecté le serment de l'Éternel et le commandement dont je t'ai instruit? »
44 Sarki ya ce wa Shimeyi, “Ka sani a zuciyarka dukan muguntar da ka yi wa mahaifina Dawuda. Yanzu Ubangiji zai sāka maka saboda muguntarka.
Le roi dit encore à Shimei: « Tu sais dans ton cœur toute la méchanceté que tu as commise envers David, mon père. C'est pourquoi Yahvé fera retomber ta méchanceté sur ta propre tête.
45 Amma za a yi wa Sarki Solomon albarka, sarautar Dawuda kuma za tă kasance a tsare a gaban Ubangiji har abada.”
Mais le roi Salomon sera béni, et le trône de David sera affermi devant Yahvé pour toujours. »
46 Sai sarki ya umarci Benahiya ɗan Yehohiyada, yă fita, yă bugi Shimeyi, yă kashe shi. Ya kuwa kashe shi. Mulki kuwa ya kahu sosai a hannun Solomon.
Le roi donna des ordres à Benaja, fils de Jehoïada, qui sortit et tomba sur lui, de sorte qu'il mourut. Le royaume fut établi entre les mains de Salomon.

< 1 Sarakuna 2 >