< 1 Sarakuna 2 >

1 Da lokacin mutuwar Dawuda ya yi kusa, sai ya gargaɗe Solomon ɗansa, ya ce,
And the days of David to die draw near, and he charges his son Solomon, saying,
2 “Ina gab da bin hanyar da kowa a duniya zai bi. Saboda haka ka yi ƙarfin hali, ka nuna kanka namiji,
“I am going in the way of all the earth, and you have been strong, and become a man,
3 ka kiyaye abin da Ubangiji Allahnka yake bukata. Yi tafiya a hanyoyinsa, ka kiyaye ƙa’idodi, da umarnai, da dokoki, da kuma farillansa, kamar yadda suke a rubuce a Dokar Musa, don ka yi nasara a cikin kome da za ka yi, da kuma inda za ka tafi.
and you have kept the charge of your God YHWH, to walk in His ways, to keep His statutes, His commands, and His judgments, and His testimonies, as it is written in the Law of Moses, so that you do wisely [in] all that you do, and wherever you turn,
4 Ubangiji kuwa zai kiyaye alkawarinsa gare ni da ya ce, ‘In zuriyarka suka lura da yadda suke rayuwa, in kuma suka yi tafiya da aminci a gabana da dukan zuciyarsu, da kuma dukan ransu, ba za ka kāsa samun mutum a kujerar sarautar Isra’ila ba.’
so that YHWH establishes His word which He spoke to me, saying, If your sons observe their way to walk before Me in truth, with all their heart, and with all their soul; saying, A man of yours is never cut off from the throne of Israel.
5 “Yanzu fa, kai kanka ka san abin da Yowab ɗan Zeruhiya ya yi mini. Abin da ya yi wa shugabanni biyun nan na mayaƙan Isra’ila, wato, Abner ɗan Ner, da Amasa ɗan Yeter. Ya kashe su, ya kuma zub da jininsu a lokacin salama sai ka ce a fage yaƙi, da wannan jini ya yi ɗamara a gindinsa, ya kuma sa takalma a ƙafafunsa.
And also, you have known that which he did to me—Joab son of Zeruiah—that which he did to two heads of the hosts of Israel, to Abner son of Ner, and to Amasa son of Jether—that he slays them, and makes the blood of war in peace, and puts the blood of war in his girdle, that [is] on his loins, and in his sandals that [are] on his feet;
6 Ka yi da shi gwargwadon hikimarka, amma kada ka bari yă gangara kabari da furfura cikin salama. (Sheol h7585)
and you have done according to your wisdom, and do not let his old age go down in peace to Sheol. (Sheol h7585)
7 “Amma ka yi alheri ga’ya’yan Barzillai mutumin Gileyad, ka sa su kasance a cikin waɗanda suke ci a teburinka. Sun goyi bayana sa’ad da nake gudu daga ɗan’uwanka Absalom.
And you do kindness to the sons of Barzillai the Gileadite, and they have been among those eating at your table, for so they drew near to me in my fleeing from the face of your brother Absalom.
8 “Ka tuna, akwai kuma Shimeyi ɗan Gera, mutumin Benyamin daga Bahurim, wanda ya yi ta yin mini muguwar la’ana a ranar da na tafi Mahanayim. Sa’ad da ya gangara ya same ni a Urdun, na rantse masa da sunan Ubangiji na ce, ‘Ba zan kashe ka da takobi ba.’
And behold, Shimei son of Gera, the Benjamite of Bahurim, [is] with you, and he reviled me—a grievous reviling—in the day of my going to Mahanaim; and he has come down to meet me at the Jordan, and I swear to him by YHWH, saying, I do not put you to death by the sword;
9 Amma yanzu, kada ka ɗauke shi marar laifi. Kai mutum ne mai hikima; za ka san abin da za ka yi da shi. Ka kawo furfuransa zuwa kabari da jini.” (Sheol h7585)
and now, do not acquit him, for you [are] a wise man, and you have known that which you do to him, and have brought down his old age with blood to Sheol.” (Sheol h7585)
10 Sa’an nan Dawuda ya huta tare da kakanninsa. Sai aka binne shi a Birnin Dawuda.
And David lies down with his fathers, and is buried in the City of David,
11 Ya yi sarauta shekaru arba’in a bisa Isra’ila. Wato, shekaru bakwai a Hebron da kuma talatin da uku a Urushalima.
and the days that David has reigned over Israel [are] forty years; he has reigned seven years in Hebron, and he has reigned thirty-three years in Jerusalem.
12 Solomon kuwa ya zauna a kan kujerar sarautar mahaifinsa Dawuda, mulkinsa kuwa ya kahu sosai.
And Solomon has sat on the throne of his father David, and his kingdom is established greatly,
13 To, sai Adoniya, ɗan Haggit ya tafi wurin Batsheba mahaifiyar Solomon. Ita kuwa ta tambaye shi ta ce, “Lafiya?” Ya amsa ya ce, “I, lafiya.”
and Adonijah son of Haggith comes to Bathsheba, mother of Solomon, and she says, “Is your coming peace?” And he says, “Peace.”
14 Sa’an nan ya ƙara da cewa, “Ina da ɗan wani abin da zan faɗa miki.” Ta ce, “Faɗa.”
And he says, “I have a word for you,” and she says, “Speak.”
15 Sai ya ce, “Kamar yadda kika sani, mulkin nan nawa ne. Dukan Isra’ila suna ɗaukana a matsayin sarki. Amma abubuwa suka canja, sai mulkin ya koma ga ɗan’uwana; gama ya zo masa daga Ubangiji ne.
And he says, “You have known that the kingdom was mine, and all Israel had set their faces toward me for reigning, and the kingdom is turned around, and is my brother’s, for it was his from YHWH;
16 Yanzu ina da roƙo guda da zan yi gare ki. Kada ki hana mini.” Ta ce, “Sai ka faɗa.”
and now, I am asking one petition of you—do not turn back my face”; and she says to him, “Speak.”
17 Sai ya ci gaba, “In kin yarda, ki yi magana da Sarki Solomon, gama ba zai ƙi jinki ba, ki ce yă ba ni yarinyan nan, Abishag, mutuniyar Shunam, tă zama matata.”
And he says, “Please speak to Solomon the king, for he does not turn back your face, and he gives Abishag the Shunammite to me for a wife.”
18 Batsheba ta ce, “Da kyau, zan yi magana da sarki dominka.”
And Bathsheba says, “Good; I speak to the king for you.”
19 Sai Batsheba ta tafi wurin Sarki Solomon don tă yi masa magana a kan Adoniya. Sarki ya miƙe tsaye don yă sadu da ita, ya rusuna mata, ya kuma zauna a kujerar sarautarsa. Ya sa aka kawo wa mahaifiyar sarki kujerar sarauta, ta kuwa zauna a gefen damansa.
And Bathsheba comes to King Solomon to speak to him for Adonijah, and the king rises to meet her, and bows himself to her, and sits on his throne, and places a throne for the mother of the king, and she sits at his right hand.
20 Ta ce, “Ina da ɗan roƙon da zan nema ka yi mini. Ina fata ba za ka hana ni ba.” Sai sarki ya amsa ya ce, “Mahaifiyata, sai ki faɗa in ji, ba zan hana miki ba.”
And she says, “I ask one small petition of you, do not turn back my face”; and the king says to her, “Ask, my mother, for I do not turn back your face.”
21 Saboda haka sai ta ce, “Ka sa a ba wa ɗan’uwanka Adoniya, Abishag mutuniyar Shunam tă zama matarsa.”
And she says, “Let Abishag the Shunammite be given to your brother Adonijah for a wife.”
22 Sarki Solomon ya amsa wa mahaifiyarsa ya ce, “Me ya sa kika roƙar wa Adoniya Abishag mutuniyar Shunam kawai? Ki ma sa a ba shi mulkin mana. Ai, shi yayana ne. I, ki roƙa dominsa, da domin Abiyatar firist, da kuma domin Yowab ɗan Zeruhiya mana!”
And King Solomon answers and says to his mother, “And why are you asking [for] Abishag the Shunammite for Adonijah? Also ask [for] the kingdom for him—for he [is] my elder brother—even for him, and for Abiathar the priest, and for Joab son of Zeruiah.”
23 Sai Sarki Solomon ya rantse da sunan Ubangiji ya ce, “Bari Allah yă yi mini hukunci mai tsanani, idan ban sa Adoniya ya biya wannan roƙo da ransa ba!
And King Solomon swears by YHWH, saying, “Thus God does to me, and thus He adds—surely Adonijah has spoken this word against his [own] soul;
24 Yanzu kuwa, muddin Ubangiji yana a raye, shi wanda ya kafa ni sosai a kan kujerar sarautar mahaifina Dawuda, ya kuma kafa mini mulki kamar yadda ya yi alkawari; za a kashe Adoniya yau!”
and now, YHWH lives, who has established me, and causes me to sit on the throne of my father David, and who has made a house for me as He spoke—surely Adonijah is put to death today.”
25 Saboda haka Sarki Solomon ya umarci Benahiya ɗan Yehohiyada yă kashe Adoniya; ya kuwa kashe shi.
And King Solomon sends by the hand of Benaiah son of Jehoiada, and he falls on him, and he dies.
26 Ga Abiyatar firist kuwa sarki ya ce, “Tafi gonarka a Anatot. Ka cancanci ka mutu, amma ba zan kashe ka yanzu ba, domin ka ɗauki akwatin alkawarin Ubangiji Mai Iko Duka a gaban mahaifina Dawuda, ka kuma sha wahala tare mahaifina.”
And the king said to Abiathar the priest, “Go to Anathoth, to your fields; for you [are] a man of death, but I do not put you to death in this day, because you have carried the Ark of Lord YHWH before my father David, and because you were afflicted in all that my father was afflicted in.”
27 Saboda haka Solomon ya cire Abiyatar daga aikin firist na Ubangiji, ya cika maganar da Ubangiji ya yi a Shilo game da gidan Eli.
And Solomon casts out Abiathar from being priest of YHWH, to fulfill the word of YHWH which He spoke concerning the house of Eli in Shiloh.
28 Sa’ad da labarin ya kai wurin Yowab, wanda ya haɗa kai da Adoniya, ko da yake bai haɗa kai da Absalom ba, sai ya gudu zuwa tentin Ubangiji, ya kama ƙahonin bagade ya riƙe.
And the report has come to Joab—for Joab has turned aside after Adonijah, though he did not turn aside after Absalom—and Joab flees to the tent of YHWH, and lays hold on the horns of the altar.
29 Aka faɗa wa Sarki Solomon cewa Yowab ya gudu zuwa tentin Ubangiji, yana kuma kusa da bagade. Sai Solomon ya umarci Benahiya ɗan Yehohiyada ya ce, “Je ka kashe shi!”
And it is declared to King Solomon that Joab has fled to the tent of YHWH, and behold, [is] near the altar; and Solomon sends Benaiah son of Jehoiada, saying, “Go, fall on him.”
30 Sai Benahiya ya shiga tentin Ubangiji ya ce wa Yowab, “Sarki ya ce, ‘Ka fita!’” Amma Yowab ya amsa ya ce, “A’a, a nan zan mutu.” Sai Benahiya ya ce wa sarki, “Ga yadda Yowab ya amsa mini.”
And Benaiah comes into the tent of YHWH and says to him, “Thus said the king: Come out”; and he says, “No, but I die here.” And Benaiah brings back word [to] the king, saying, “Thus spoke Joab, indeed, thus he answered me.”
31 Sai sarki ya umarci Benahiya ya ce, “Yi kamar yadda ya faɗa. Ka kashe shi, ka kuma binne shi, ka wanke ni da gidan mahaifina daga laifin jini marasa laifin da Yowab ya zubar.
And the king says to him, “Do as he has spoken, and fall on him, and you have buried him, and turned aside the causeless blood which Joab shed from off me, and from off the house of my father;
32 Ubangiji zai sāka masa saboda jinin da ya zubar, domin ba da sanin mahaifina Dawuda ne ya fāɗa wa mutum biyun nan da takobi ba. Dukansu biyu, Abner ɗan Ner, shugaban mayaƙan Isra’ila, da Amasa ɗan Yeter, shugaban mayaƙan Yahuda, mutane ne mafi kyau da kuma mafi adalci fiye da shi.
and YHWH has turned back his blood on his own head, [on him] who has fallen on two men more righteous and better than he, and slays them with the sword—and my father David did not know—Abner son of Ner, head of the host of Israel, and Amasa son of Jether, head of the host of Judah;
33 Bari alhakin jininsu yă koma a kan Yowab da kuma zuriyarsa har abada. Amma bari salamar Ubangiji tă kasance a kan Dawuda da zuriyarsa, da gidansa, da kuma mulkinsa, har abada.”
indeed, their blood has turned back on the head of Joab, and on the head of his seed for all time; and for David, and for his seed, and for his house, and for his throne, there is peace for all time, from YHWH.”
34 Sai Benahiya ɗan Yehohiyada ya haura ya bugi Yowab, ya kashe shi, ya kuwa binne shi a gidansa a ƙauye.
And Benaiah son of Jehoiada goes up and falls on him, and puts him to death, and he is buried in his own house in the wilderness,
35 Sai sarki ya sa Benahiya ɗan Yehohiyada ya zama shugaba a bisa mayaƙa a matsayin Yowab, ya kuma sa Zadok firist a wurin Abiyatar.
and the king puts Benaiah son of Jehoiada over the host in his stead, and the king has put Zadok the priest in the stead of Abiathar.
36 Sa’an nan sarki ya aika aka kawo Shimeyi, ya kuma ce masa, “Ka gina wa kanka gida a nan a Urushalima, ka zauna a ciki, kada ka kuskura ka tafi wani wuri.
And the king sends and calls for Shimei, and says to him, “Build a house for yourself in Jerusalem, and you have dwelt there, and do not go out [from] there anywhere;
37 Gama ran da ka fita, ka haye Kwarin Kidron, ka tabbata za ka mutu, alhakin jininka kuwa zai koma kanka.”
and it has been, in the day of your going out, and you have passed over the Brook of Kidron, you certainly know that you surely die—your blood is on your head.”
38 Shimeyi ya amsa wa sarki ya ce, “Abin da ka faɗa yana da kyau. Bawanka zai yi kamar yadda ranka yă daɗe sarki, ya faɗa.” Shimeyi kuwa ya yi zama a Urushalima na dogon lokaci.
And Shimei says to the king, “The word [is] good; as my lord the king has spoken so your servant does”; and Shimei dwells in Jerusalem many days.
39 Amma bayan shekaru uku, biyu daga cikin bayin Shimeyi suka gudu zuwa wurin Akish ɗan Ma’aka, sarkin Gat. Aka faɗa wa Shimeyi cewa, “Bayinka suna a Gat.”
And it comes to pass, at the end of three years, that two of the servants of Shimei flee to Achish son of Maachah, king of Gath, and they declare to Shimei, saying, “Behold, your servants [are] in Gath”;
40 Da jin haka, sai ya tashi ya shimfiɗa wa jakinsa abin zama, ya hau, ya tafi Gat wurin Akish domin neman bayinsa. Shimeyi kuwa ya dawo da su gida daga Gat.
and Shimei rises, and saddles his donkey, and goes to Gath, to Achish, to seek his servants, and Shimei goes and brings his servants from Gath.
41 Da aka faɗa wa Solomon cewa Shimeyi ya bar Urushalima zuwa Gat, har ya dawo.
And it is declared to Solomon that Shimei has gone from Jerusalem to Gath, and returns,
42 Sai sarki ya aika a kawo Shimeyi, ya ce masa, “Ban sa ka rantse da sunan Ubangiji, na kuma ja maka kunne cewa, ‘A ranar da ka kuskura ka bar nan ka tafi wani wuri, ka tabbata za ka mutu ba’? A lokacin ka ce mini, ‘Abin da ka faɗa yana da kyau. Zan kuwa kiyaye.’
and the king sends and calls for Shimei, and says to him, “Have I not caused you to swear by YHWH—and I testify against you, saying, In the day of your going out, and you have gone anywhere, you certainly know that you surely die; and you say to me, The word I have heard [is] good?
43 To, me ya sa ba ka kiyaye rantsuwar da ka yi ga Ubangiji, ka kuma yi biyayya da umarnin da na ba ka ba?”
And why have you not kept the oath of YHWH, and the charge that I charged on you?”
44 Sarki ya ce wa Shimeyi, “Ka sani a zuciyarka dukan muguntar da ka yi wa mahaifina Dawuda. Yanzu Ubangiji zai sāka maka saboda muguntarka.
And the king says to Shimei, “You have known all the evil that your heart has known, which you did to my father David, and YHWH has turned back your evil on your head,
45 Amma za a yi wa Sarki Solomon albarka, sarautar Dawuda kuma za tă kasance a tsare a gaban Ubangiji har abada.”
and King Solomon [is] blessed, and the throne of David is established before YHWH for all time.”
46 Sai sarki ya umarci Benahiya ɗan Yehohiyada, yă fita, yă bugi Shimeyi, yă kashe shi. Ya kuwa kashe shi. Mulki kuwa ya kahu sosai a hannun Solomon.
And the king charges Benaiah son of Jehoiada, and he goes out and falls on him, and he dies, and the kingdom is established in the hand of Solomon.

< 1 Sarakuna 2 >