< 1 Sarakuna 2 >

1 Da lokacin mutuwar Dawuda ya yi kusa, sai ya gargaɗe Solomon ɗansa, ya ce,
And when the days of David drew near that he should die, he charged Solomon his son, saying,
2 “Ina gab da bin hanyar da kowa a duniya zai bi. Saboda haka ka yi ƙarfin hali, ka nuna kanka namiji,
I am going the way of all the earth; but be thou strong, and become a man;
3 ka kiyaye abin da Ubangiji Allahnka yake bukata. Yi tafiya a hanyoyinsa, ka kiyaye ƙa’idodi, da umarnai, da dokoki, da kuma farillansa, kamar yadda suke a rubuce a Dokar Musa, don ka yi nasara a cikin kome da za ka yi, da kuma inda za ka tafi.
And keep the charge of the Lord thy God, to walk in his ways, to keep his statutes, his commandments, and his ordinances, and his testimonies, as it is written in the law of Moses; in order that thou mayest prosper in all that thou doest, and whithersoever thou turnest thyself;
4 Ubangiji kuwa zai kiyaye alkawarinsa gare ni da ya ce, ‘In zuriyarka suka lura da yadda suke rayuwa, in kuma suka yi tafiya da aminci a gabana da dukan zuciyarsu, da kuma dukan ransu, ba za ka kāsa samun mutum a kujerar sarautar Isra’ila ba.’
In order that the Lord may fulfill his word which he hath spoken concerning me, saying, If thy children take heed to their way, to walk before me in truth with all their heart and with all their soul, there shall never fail thee, said he, a man on the throne of Israel.
5 “Yanzu fa, kai kanka ka san abin da Yowab ɗan Zeruhiya ya yi mini. Abin da ya yi wa shugabanni biyun nan na mayaƙan Isra’ila, wato, Abner ɗan Ner, da Amasa ɗan Yeter. Ya kashe su, ya kuma zub da jininsu a lokacin salama sai ka ce a fage yaƙi, da wannan jini ya yi ɗamara a gindinsa, ya kuma sa takalma a ƙafafunsa.
And thou also knowest well what Joab the son of Zeruyah hath done to me, what he did to the two captains of the armies of Israel, unto Abner the son of Ner, and unto 'Amassa the son of Yether, whom he slew, and shed the blood of war in peace, and put the blood of war upon his girdle that was about his loins, and on his shoes that were on his feet.
6 Ka yi da shi gwargwadon hikimarka, amma kada ka bari yă gangara kabari da furfura cikin salama. (Sheol h7585)
Do therefore according to thy wisdom, and let not his hoary head go down in peace to the grave. (Sheol h7585)
7 “Amma ka yi alheri ga’ya’yan Barzillai mutumin Gileyad, ka sa su kasance a cikin waɗanda suke ci a teburinka. Sun goyi bayana sa’ad da nake gudu daga ɗan’uwanka Absalom.
But unto the sons of Barzillai the Gil'adite show thou kindness, and let them be of those that eat at thy table; for so they came near to me when I fled from before Abshalom thy brother.
8 “Ka tuna, akwai kuma Shimeyi ɗan Gera, mutumin Benyamin daga Bahurim, wanda ya yi ta yin mini muguwar la’ana a ranar da na tafi Mahanayim. Sa’ad da ya gangara ya same ni a Urdun, na rantse masa da sunan Ubangiji na ce, ‘Ba zan kashe ka da takobi ba.’
And, behold, thou hast with thee Shim'i the son of Gera, the Benjamite of Bachurim, who cursed me with a grievous curse on the day when I went to Machanayim; but who came down to meet me at the Jordan, and I swore to him by the Lord, saying, I will not put thee to death with the sword.
9 Amma yanzu, kada ka ɗauke shi marar laifi. Kai mutum ne mai hikima; za ka san abin da za ka yi da shi. Ka kawo furfuransa zuwa kabari da jini.” (Sheol h7585)
But now leave him not unpunished; for thou art a wise man; know then what thou oughtest to do unto him, and bring thou down his hoary head with blood to the grave. (Sheol h7585)
10 Sa’an nan Dawuda ya huta tare da kakanninsa. Sai aka binne shi a Birnin Dawuda.
And David slept with his fathers, and was buried in the city of David.
11 Ya yi sarauta shekaru arba’in a bisa Isra’ila. Wato, shekaru bakwai a Hebron da kuma talatin da uku a Urushalima.
And the days that David reigned over Israel were forty years: in Hebron he reigned seven years, and in Jerusalem he reigned thirty and three years.
12 Solomon kuwa ya zauna a kan kujerar sarautar mahaifinsa Dawuda, mulkinsa kuwa ya kahu sosai.
Then sat Solomon upon the throne of David his father; and his kingdom was established greatly.
13 To, sai Adoniya, ɗan Haggit ya tafi wurin Batsheba mahaifiyar Solomon. Ita kuwa ta tambaye shi ta ce, “Lafiya?” Ya amsa ya ce, “I, lafiya.”
And Adoniyah the son of Chaggith came to Bath-sheba' the mother of Solomon: and she said, Is thy coming for peace? And he said, For peace.
14 Sa’an nan ya ƙara da cewa, “Ina da ɗan wani abin da zan faɗa miki.” Ta ce, “Faɗa.”
He said moreover, I have a word for thee. And she said, Speak.
15 Sai ya ce, “Kamar yadda kika sani, mulkin nan nawa ne. Dukan Isra’ila suna ɗaukana a matsayin sarki. Amma abubuwa suka canja, sai mulkin ya koma ga ɗan’uwana; gama ya zo masa daga Ubangiji ne.
And he said, Thou well knowest that mine was the kingdom, and that on me all Israel had set their faces, that I should reign: nevertheless the kingdom was turned about, and became my brother's; for from the Lord was it [made] his.
16 Yanzu ina da roƙo guda da zan yi gare ki. Kada ki hana mini.” Ta ce, “Sai ka faɗa.”
And now there is one petition I am going to ask of thee, do not turn me away. And she said unto him, Speak.
17 Sai ya ci gaba, “In kin yarda, ki yi magana da Sarki Solomon, gama ba zai ƙi jinki ba, ki ce yă ba ni yarinyan nan, Abishag, mutuniyar Shunam, tă zama matata.”
And he said, Speak, I pray thee, unto Solomon the king, [for he will not turn thee away, ] that he may give me Abishag the Shunammite for wife.
18 Batsheba ta ce, “Da kyau, zan yi magana da sarki dominka.”
And Bath-sheba' said, Well: I will speak for thee unto the king.
19 Sai Batsheba ta tafi wurin Sarki Solomon don tă yi masa magana a kan Adoniya. Sarki ya miƙe tsaye don yă sadu da ita, ya rusuna mata, ya kuma zauna a kujerar sarautarsa. Ya sa aka kawo wa mahaifiyar sarki kujerar sarauta, ta kuwa zauna a gefen damansa.
Bath-sheba' thereupon went unto king Solomon, to speak unto him for Adoniyah; and the king rose up to meet her, and bowed himself unto her, and then sat down on his throne, and placed a chair for the king's mother; and she sat on his right hand.
20 Ta ce, “Ina da ɗan roƙon da zan nema ka yi mini. Ina fata ba za ka hana ni ba.” Sai sarki ya amsa ya ce, “Mahaifiyata, sai ki faɗa in ji, ba zan hana miki ba.”
Then said she, There is one small petition I am going to ask of thee; do not turn me away. And the king said unto her, Ask on, my mother; for I will not turn thee away.
21 Saboda haka sai ta ce, “Ka sa a ba wa ɗan’uwanka Adoniya, Abishag mutuniyar Shunam tă zama matarsa.”
And she said, Let Abishag the Shunammite be given to Adoniyah thy brother for wife.
22 Sarki Solomon ya amsa wa mahaifiyarsa ya ce, “Me ya sa kika roƙar wa Adoniya Abishag mutuniyar Shunam kawai? Ki ma sa a ba shi mulkin mana. Ai, shi yayana ne. I, ki roƙa dominsa, da domin Abiyatar firist, da kuma domin Yowab ɗan Zeruhiya mana!”
And king Solomon answered and said unto his mother, And why dost thou ask Abishag the Shunammite for Adoniyah? rather ask for him the kingdom; for he is my elder brother; — even for him, and for Ebyathar the priest, and for Joab the son of Zeruyah.
23 Sai Sarki Solomon ya rantse da sunan Ubangiji ya ce, “Bari Allah yă yi mini hukunci mai tsanani, idan ban sa Adoniya ya biya wannan roƙo da ransa ba!
Then swore king Solomon by the Lord, saying, May God do so to me, and may he thus continue, if Adoniyah have not spoken this word against his own life.
24 Yanzu kuwa, muddin Ubangiji yana a raye, shi wanda ya kafa ni sosai a kan kujerar sarautar mahaifina Dawuda, ya kuma kafa mini mulki kamar yadda ya yi alkawari; za a kashe Adoniya yau!”
And now, as the Lord liveth, who hath established me, and seated me on the throne of David my father, and who hath made me a house, as he hath spoken, this very day shall Adoniyah be put to death.
25 Saboda haka Sarki Solomon ya umarci Benahiya ɗan Yehohiyada yă kashe Adoniya; ya kuwa kashe shi.
And king Solomon sent by the hand of Benayahu the son of Yehoyada'; and he fell upon him so that he died.
26 Ga Abiyatar firist kuwa sarki ya ce, “Tafi gonarka a Anatot. Ka cancanci ka mutu, amma ba zan kashe ka yanzu ba, domin ka ɗauki akwatin alkawarin Ubangiji Mai Iko Duka a gaban mahaifina Dawuda, ka kuma sha wahala tare mahaifina.”
And unto Ebyathar the priest said the king, Go to 'Anathoth, unto thy own fields; for thou art a man worthy of death; but on this day will I not put thee to death; because thou hast borne the ark of the Lord Eternal before David my father, and because thou was afflicted in all wherein my father was afflicted.
27 Saboda haka Solomon ya cire Abiyatar daga aikin firist na Ubangiji, ya cika maganar da Ubangiji ya yi a Shilo game da gidan Eli.
So Solomon banished Ebyathar that he should not be priest unto the Lord, to fulfill the word of the Lord, which he had spoken concerning the house of 'Eli in Shiloh.
28 Sa’ad da labarin ya kai wurin Yowab, wanda ya haɗa kai da Adoniya, ko da yake bai haɗa kai da Absalom ba, sai ya gudu zuwa tentin Ubangiji, ya kama ƙahonin bagade ya riƙe.
And the report came to Joab; for Joab had turned after Adoniyah, though he had not turned after Abshalom. And Joab fled unto the tabernacle of the Lord, and caught hold on the horns of the altar.
29 Aka faɗa wa Sarki Solomon cewa Yowab ya gudu zuwa tentin Ubangiji, yana kuma kusa da bagade. Sai Solomon ya umarci Benahiya ɗan Yehohiyada ya ce, “Je ka kashe shi!”
And it was told to king Solomon that Joab had fled unto the tabernacle of the Lord; and that, behold, he was close by the altar. Then sent Solomon Benayahu the son of Yehoyada,' saying, Go, fall upon him.
30 Sai Benahiya ya shiga tentin Ubangiji ya ce wa Yowab, “Sarki ya ce, ‘Ka fita!’” Amma Yowab ya amsa ya ce, “A’a, a nan zan mutu.” Sai Benahiya ya ce wa sarki, “Ga yadda Yowab ya amsa mini.”
And Benayahu came to the tabernacle of the Lord, and said unto him, Thus hath said the king, Come forth. And he said, No; but here will I die. And Benayahu brought the king word again, saying, Thus hath Joab spoken, and thus hath he answered me.
31 Sai sarki ya umarci Benahiya ya ce, “Yi kamar yadda ya faɗa. Ka kashe shi, ka kuma binne shi, ka wanke ni da gidan mahaifina daga laifin jini marasa laifin da Yowab ya zubar.
Then said the king unto him, Do as he hath spoken, and fall upon him, and bury him; and remove [thus] the innocent blood, which Joab hath shed, from me, and from the house of my father.
32 Ubangiji zai sāka masa saboda jinin da ya zubar, domin ba da sanin mahaifina Dawuda ne ya fāɗa wa mutum biyun nan da takobi ba. Dukansu biyu, Abner ɗan Ner, shugaban mayaƙan Isra’ila, da Amasa ɗan Yeter, shugaban mayaƙan Yahuda, mutane ne mafi kyau da kuma mafi adalci fiye da shi.
And may the Lord bring back his blood-guiltiness upon his own head, because he fell upon two men more righteous and better than he, and slew them with the sword, while my father David knew it not, Abner the son of Ner, the captain of the army of Israel, and 'Amassa the son of Yether, the captain of the army of Judah.
33 Bari alhakin jininsu yă koma a kan Yowab da kuma zuriyarsa har abada. Amma bari salamar Ubangiji tă kasance a kan Dawuda da zuriyarsa, da gidansa, da kuma mulkinsa, har abada.”
And their blood shall return upon the head of Joab, and upon the head of his seed for ever; but unto David, and unto his seed, and unto his house, and unto his throne, may there be peace for ever from the Lord.
34 Sai Benahiya ɗan Yehohiyada ya haura ya bugi Yowab, ya kashe shi, ya kuwa binne shi a gidansa a ƙauye.
So Benayahu the son of Yehoyada' went up, and fell upon him, and slew him: and he was buried in his own house in the wilderness.
35 Sai sarki ya sa Benahiya ɗan Yehohiyada ya zama shugaba a bisa mayaƙa a matsayin Yowab, ya kuma sa Zadok firist a wurin Abiyatar.
And the king appointed Benayahu the son of Yehoyada' in his place over the army; and Zadok the priest did the king appoint in the place of Ebyathar.
36 Sa’an nan sarki ya aika aka kawo Shimeyi, ya kuma ce masa, “Ka gina wa kanka gida a nan a Urushalima, ka zauna a ciki, kada ka kuskura ka tafi wani wuri.
And the king sent and called for Shim'i, and said unto him, Build thee a house in Jerusalem, and dwell there, and thou shalt not go forth from there hither or thither.
37 Gama ran da ka fita, ka haye Kwarin Kidron, ka tabbata za ka mutu, alhakin jininka kuwa zai koma kanka.”
And it shall be, that on the day thou goest out, and passest over the brook Kidron, thou shalt know for certain that thou shalt surely die: thy blood shall be upon thy own head.
38 Shimeyi ya amsa wa sarki ya ce, “Abin da ka faɗa yana da kyau. Bawanka zai yi kamar yadda ranka yă daɗe sarki, ya faɗa.” Shimeyi kuwa ya yi zama a Urushalima na dogon lokaci.
And Shim'i said unto the king, It is well: as my Lord the king hath spoken, so will thy servant do. And Shim'i dwelt in Jerusalem many days.
39 Amma bayan shekaru uku, biyu daga cikin bayin Shimeyi suka gudu zuwa wurin Akish ɗan Ma’aka, sarkin Gat. Aka faɗa wa Shimeyi cewa, “Bayinka suna a Gat.”
And it came to pass at the end of three years, that two servants of Shim'i ran away unto Achish the son of Ma'achah the king of Gath: and they told unto Shim'i, saying, Behold, thy servants are in Gath.
40 Da jin haka, sai ya tashi ya shimfiɗa wa jakinsa abin zama, ya hau, ya tafi Gat wurin Akish domin neman bayinsa. Shimeyi kuwa ya dawo da su gida daga Gat.
And Shim'i arose, and saddled his ass, and went to Gath to Achish to seek his servants; and Shim'i went, and brought his servants from Gath.
41 Da aka faɗa wa Solomon cewa Shimeyi ya bar Urushalima zuwa Gat, har ya dawo.
And it was told to Solomon that Shim'i had gone from Jerusalem to Gath, and had returned.
42 Sai sarki ya aika a kawo Shimeyi, ya ce masa, “Ban sa ka rantse da sunan Ubangiji, na kuma ja maka kunne cewa, ‘A ranar da ka kuskura ka bar nan ka tafi wani wuri, ka tabbata za ka mutu ba’? A lokacin ka ce mini, ‘Abin da ka faɗa yana da kyau. Zan kuwa kiyaye.’
And the king sent and called for Shim'i, and said unto him, Did I not make thee swear by the Lord, and warned thee, saying, On that day thou goest out, and walkest abroad hither or thither, know for certain that thou shalt surely die? and thou saidst unto me, It is well, I have heard?
43 To, me ya sa ba ka kiyaye rantsuwar da ka yi ga Ubangiji, ka kuma yi biyayya da umarnin da na ba ka ba?”
Why then hast thou not kept the oath of the Lord, and the commandment with which I charged thee?
44 Sarki ya ce wa Shimeyi, “Ka sani a zuciyarka dukan muguntar da ka yi wa mahaifina Dawuda. Yanzu Ubangiji zai sāka maka saboda muguntarka.
The king said moreover to Shim'i, Thou well knowest all the wickedness of which thy heart is conscious, that thou hast done to David my father: and the Lord bringeth back thy wickedness upon thy own head;
45 Amma za a yi wa Sarki Solomon albarka, sarautar Dawuda kuma za tă kasance a tsare a gaban Ubangiji har abada.”
But king Solomon will be blessed, and the throne of David will be established before the Lord for ever.
46 Sai sarki ya umarci Benahiya ɗan Yehohiyada, yă fita, yă bugi Shimeyi, yă kashe shi. Ya kuwa kashe shi. Mulki kuwa ya kahu sosai a hannun Solomon.
So the king commanded Benayahu the son of Yehoyada', who went out, and fell upon him, so that he died. And the kingdom was established in the hand of Solomon.

< 1 Sarakuna 2 >