< 1 Sarakuna 2 >

1 Da lokacin mutuwar Dawuda ya yi kusa, sai ya gargaɗe Solomon ɗansa, ya ce,
Kane kinde ochopo machiegni mondo Daudi otho, nosiemo Solomon wuode.
2 “Ina gab da bin hanyar da kowa a duniya zai bi. Saboda haka ka yi ƙarfin hali, ka nuna kanka namiji,
Kowacho niya, “Achiegni dhi kuma ji duto manie piny dhiye.” Omiyo bed motegno kendo jiwri ka dichwo,
3 ka kiyaye abin da Ubangiji Allahnka yake bukata. Yi tafiya a hanyoyinsa, ka kiyaye ƙa’idodi, da umarnai, da dokoki, da kuma farillansa, kamar yadda suke a rubuce a Dokar Musa, don ka yi nasara a cikin kome da za ka yi, da kuma inda za ka tafi.
kendo irit gima Jehova Nyasaye ma Nyasachi dwaro: Kiwuotho e yorene kendo irit puonjne gi chikene kod gik moko duto modwaro kaka ondiki e chik Musa mondo idhi nyime maber e gik moko duto mitimo, kendo kamoro amora midhiye,
4 Ubangiji kuwa zai kiyaye alkawarinsa gare ni da ya ce, ‘In zuriyarka suka lura da yadda suke rayuwa, in kuma suka yi tafiya da aminci a gabana da dukan zuciyarsu, da kuma dukan ransu, ba za ka kāsa samun mutum a kujerar sarautar Isra’ila ba.’
eka Jehova Nyasaye nyalo rito singruokne mane omiya ni, Ka nyikwayi onono kaka gidak kendo ka giwuotho gi adiera e nyima gi chunygi duto kod parogi duto to ok nibedi maonge ngʼat manyalo bedo e kom duongʼ e Israel.
5 “Yanzu fa, kai kanka ka san abin da Yowab ɗan Zeruhiya ya yi mini. Abin da ya yi wa shugabanni biyun nan na mayaƙan Isra’ila, wato, Abner ɗan Ner, da Amasa ɗan Yeter. Ya kashe su, ya kuma zub da jininsu a lokacin salama sai ka ce a fage yaƙi, da wannan jini ya yi ɗamara a gindinsa, ya kuma sa takalma a ƙafafunsa.
Koro in iwuon ingʼeyo gima Joab wuod Zeruya notimona, gima notimo ni jotend lweny ariyo mag Israel, Abner wuod Ner gi Amasa wuod Jetha. Ne onegogi, kochwero rembgi e ndalo kwe mana ka ndalo mag lweny kendo remono nomienogo okandane mane otweyo e nungone kod wuochene manie tiendene.
6 Ka yi da shi gwargwadon hikimarka, amma kada ka bari yă gangara kabari da furfura cikin salama. (Sheol h7585)
Ti kode kaluwore gi riekoni, to kik iwe lwar mantie e wiye dhi e bur gi kwe. (Sheol h7585)
7 “Amma ka yi alheri ga’ya’yan Barzillai mutumin Gileyad, ka sa su kasance a cikin waɗanda suke ci a teburinka. Sun goyi bayana sa’ad da nake gudu daga ɗan’uwanka Absalom.
To bed mangʼwon ni yawuot Barzilai ja-Gilead kendo we gibed achiel kuom joma chiemo e mesani. Negidok jokora kane aringo e nyim Abisalom owadu.
8 “Ka tuna, akwai kuma Shimeyi ɗan Gera, mutumin Benyamin daga Bahurim, wanda ya yi ta yin mini muguwar la’ana a ranar da na tafi Mahanayim. Sa’ad da ya gangara ya same ni a Urdun, na rantse masa da sunan Ubangiji na ce, ‘Ba zan kashe ka da takobi ba.’
Bende par, ni nitie Shimei wuod Gera, ja-Benjamin moa Bahurim mane okwongʼa malit kane adhi Mahanaim. Kane obiro romona e dho Jordan, ne akwongʼorane gi nying Jehova Nyasaye niya, Ok ananegi gi ligangla.
9 Amma yanzu, kada ka ɗauke shi marar laifi. Kai mutum ne mai hikima; za ka san abin da za ka yi da shi. Ka kawo furfuransa zuwa kabari da jini.” (Sheol h7585)
To koro kik ikwane ka ngʼama onge ketho. In ngʼama riek; iningʼe gima nitimne. Kik iwe lwar mantie e wiye dhi e bur gi kwe. (Sheol h7585)
10 Sa’an nan Dawuda ya huta tare da kakanninsa. Sai aka binne shi a Birnin Dawuda.
Eka Daudi notho gi wuonene kendo noyike e Dala Maduongʼ mar Daudi.
11 Ya yi sarauta shekaru arba’in a bisa Isra’ila. Wato, shekaru bakwai a Hebron da kuma talatin da uku a Urushalima.
Daudi noyudo osetelo ne Israel kuom higni piero angʼwen, ka higni abiriyo ne en Hebron to higni piero adek gadek ka en Jerusalem.
12 Solomon kuwa ya zauna a kan kujerar sarautar mahaifinsa Dawuda, mulkinsa kuwa ya kahu sosai.
Omiyo Solomon nobet e kom loch wuon mare Daudi, kendo lochne nogurore.
13 To, sai Adoniya, ɗan Haggit ya tafi wurin Batsheba mahaifiyar Solomon. Ita kuwa ta tambaye shi ta ce, “Lafiya?” Ya amsa ya ce, “I, lafiya.”
Koro Adonija wuod Hagith nodhi ir Bathsheba min Solomon. Bathsheba nopenje niya, “Ibiro gi kwe?” Eka nodwoko niya, “Ee abiro gi kwe.”
14 Sa’an nan ya ƙara da cewa, “Ina da ɗan wani abin da zan faɗa miki.” Ta ce, “Faɗa.”
Eka nomedo wacho niya, “An gi wach moro madwaro wachoni.” Nodwoko niya, “Inyalo wacho.”
15 Sai ya ce, “Kamar yadda kika sani, mulkin nan nawa ne. Dukan Isra’ila suna ɗaukana a matsayin sarki. Amma abubuwa suka canja, sai mulkin ya koma ga ɗan’uwana; gama ya zo masa daga Ubangiji ne.
Eka nowacho niya, “Kaka ingʼeyo, pinyruoth ne mara. Jo-Israel duto nongʼiya kaka ruodhgi. To gik moko nolokore ma pinyruoth nodok ni owadwa; nimar Jehova Nyasaye ema osemiyego.
16 Yanzu ina da roƙo guda da zan yi gare ki. Kada ki hana mini.” Ta ce, “Sai ka faɗa.”
Koro an gi kwayo achiel madwaro kwayo. Ka iyie to kik itama.” Bathsheba nowachone niya, “Wachi.”
17 Sai ya ci gaba, “In kin yarda, ki yi magana da Sarki Solomon, gama ba zai ƙi jinki ba, ki ce yă ba ni yarinyan nan, Abishag, mutuniyar Shunam, tă zama matata.”
Eka Adonija nomedo wacho niya, “Yie ikwa ruoth Solomon omiya Abishag nyar Shunam obed jaoda nikech angʼeyo ni ok obi tami.”
18 Batsheba ta ce, “Da kyau, zan yi magana da sarki dominka.”
Bathsheba to ne odwoke niya, “Mano ber, abiro wuoyoni gi ruoth.”
19 Sai Batsheba ta tafi wurin Sarki Solomon don tă yi masa magana a kan Adoniya. Sarki ya miƙe tsaye don yă sadu da ita, ya rusuna mata, ya kuma zauna a kujerar sarautarsa. Ya sa aka kawo wa mahaifiyar sarki kujerar sarauta, ta kuwa zauna a gefen damansa.
Kane Bathsheba odhi ir Ruoth Solomon mondo owuo kuom Adonija, ruoth nochungʼ malo mokulorene eka nobet e kome mar duongʼ. Nokwayo mondo okel ni min-gi kom duongʼ eka nobet e bade korachwich.
20 Ta ce, “Ina da ɗan roƙon da zan nema ka yi mini. Ina fata ba za ka hana ni ba.” Sai sarki ya amsa ya ce, “Mahaifiyata, sai ki faɗa in ji, ba zan hana miki ba.”
Bathsheba nowachone niya, “An-gi kwayo matin madwaro kwayo to yie kik itama.” Ruoth to nodwoke niya, “Kwaye akwaya minwa nimar ok anatami.”
21 Saboda haka sai ta ce, “Ka sa a ba wa ɗan’uwanka Adoniya, Abishag mutuniyar Shunam tă zama matarsa.”
Omiyo nowacho niya, “Yie iwe Abishag nyar Shunam mondo okend gi owadu Adonija.”
22 Sarki Solomon ya amsa wa mahaifiyarsa ya ce, “Me ya sa kika roƙar wa Adoniya Abishag mutuniyar Shunam kawai? Ki ma sa a ba shi mulkin mana. Ai, shi yayana ne. I, ki roƙa dominsa, da domin Abiyatar firist, da kuma domin Yowab ɗan Zeruhiya mana!”
Ruoth Solomon nodwoko min niya, “Angʼo momiyo ikwayo Abishag nyar Shunam ni Adonija? Inyalo anyala kata mana kwayone pinyruoth nimar en owadwa maduongʼ, bende inyalo kwaye ni Abiathar jadolo kod Joab wuod Zeruya!”
23 Sai Sarki Solomon ya rantse da sunan Ubangiji ya ce, “Bari Allah yă yi mini hukunci mai tsanani, idan ban sa Adoniya ya biya wannan roƙo da ransa ba!
Eka Ruoth Solomon nokwongʼore gi nying Jehova Nyasaye niya, “Mad Nyasaye kweda ka Adonija ok otho nikech kwayoni.
24 Yanzu kuwa, muddin Ubangiji yana a raye, shi wanda ya kafa ni sosai a kan kujerar sarautar mahaifina Dawuda, ya kuma kafa mini mulki kamar yadda ya yi alkawari; za a kashe Adoniya yau!”
Akwongʼora gi nying Jehova Nyasaye mangima ni en mosegura e kom loch mar Daudi wuora kendo mosesingo ni nyikwaya pinyruoth ni Adonija nyaka negi kawuono!”
25 Saboda haka Sarki Solomon ya umarci Benahiya ɗan Yehohiyada yă kashe Adoniya; ya kuwa kashe shi.
Omiyo Ruoth Solomon nochiwo chik ne Benaya wuod Jehoyada, mi nonego Adonija.
26 Ga Abiyatar firist kuwa sarki ya ce, “Tafi gonarka a Anatot. Ka cancanci ka mutu, amma ba zan kashe ka yanzu ba, domin ka ɗauki akwatin alkawarin Ubangiji Mai Iko Duka a gaban mahaifina Dawuda, ka kuma sha wahala tare mahaifina.”
To kuom Abiathar jadolo, ruoth nowacho niya, “Dog e puotheni mantie Anathoth. Iwinjori gi tho, to ok ananegi sani, nikech nitingʼo Sandug Muma mar Jehova Nyasaye Manyalo Gik Moko Duto e nyim Daudi wuonwa kendo nineno chandruok duto mane wuonwa oneno.”
27 Saboda haka Solomon ya cire Abiyatar daga aikin firist na Ubangiji, ya cika maganar da Ubangiji ya yi a Shilo game da gidan Eli.
Omiyo Solomon nogolo Abiathar e tich dolo mar Jehova Nyasaye kochopogo wach mane Jehova Nyasaye owacho Shilo kuom od Eli.
28 Sa’ad da labarin ya kai wurin Yowab, wanda ya haɗa kai da Adoniya, ko da yake bai haɗa kai da Absalom ba, sai ya gudu zuwa tentin Ubangiji, ya kama ƙahonin bagade ya riƙe.
Kane wechego olandore mochopo ni Joab mane joriwore gi Adonija kata obedo ni ne ok oriwore gi Abisalom, ne oringo modhi e Hemb Jehova Nyasaye mi nomako tunge kendo mar misango.
29 Aka faɗa wa Sarki Solomon cewa Yowab ya gudu zuwa tentin Ubangiji, yana kuma kusa da bagade. Sai Solomon ya umarci Benahiya ɗan Yehohiyada ya ce, “Je ka kashe shi!”
Ruoth Solomon nowachne ni Joab oseringo modhi e hemb Jehova Nyasaye kendo ni ne en but kendo mar misango. Eka Solomon nochiko Benaya wuod Jehoyada niya, “Dhiyo mondo inege.”
30 Sai Benahiya ya shiga tentin Ubangiji ya ce wa Yowab, “Sarki ya ce, ‘Ka fita!’” Amma Yowab ya amsa ya ce, “A’a, a nan zan mutu.” Sai Benahiya ya ce wa sarki, “Ga yadda Yowab ya amsa mini.”
Omiyo Benaya nodonjo e Hemb Jehova Nyasaye kendo nowacho ni Joab niya, “Ruoth wacho ni, ‘Wuog oko!’” To nodwoke niya, “Ooyo, abiro mana tho ka.” Benaya nodwoko wach Joab ni ruoth.
31 Sai sarki ya umarci Benahiya ya ce, “Yi kamar yadda ya faɗa. Ka kashe shi, ka kuma binne shi, ka wanke ni da gidan mahaifina daga laifin jini marasa laifin da Yowab ya zubar.
Eka ruoth nochiko Benaya niya, “Tim kaka osewacho. Nege kendo yike mondo ipwodha kod od wuonwa kuom richo mar remo makare mane Joab ochwero.
32 Ubangiji zai sāka masa saboda jinin da ya zubar, domin ba da sanin mahaifina Dawuda ne ya fāɗa wa mutum biyun nan da takobi ba. Dukansu biyu, Abner ɗan Ner, shugaban mayaƙan Isra’ila, da Amasa ɗan Yeter, shugaban mayaƙan Yahuda, mutane ne mafi kyau da kuma mafi adalci fiye da shi.
Jehova Nyasaye enochule kuom remo mane ochwero, nikech nonego ji ariyo gi ligangla ka wuonwa Daudi kia. Nonego Abner wuod Ner jatend lweny mar Israel kod Amasa wuod Jetha jatend lweny mar Juda mane gin joma ber kendo mobidhore moloye.
33 Bari alhakin jininsu yă koma a kan Yowab da kuma zuriyarsa har abada. Amma bari salamar Ubangiji tă kasance a kan Dawuda da zuriyarsa, da gidansa, da kuma mulkinsa, har abada.”
Mad rembgi obedi ewi Joab gi nyikwaye nyaka chiengʼ. To kuom Daudi gi nyikwaye gi ode kod kuom lochne, mad kwe Jehova Nyasaye obedie nyaka chiengʼ.”
34 Sai Benahiya ɗan Yehohiyada ya haura ya bugi Yowab, ya kashe shi, ya kuwa binne shi a gidansa a ƙauye.
Omiyo Benaya wuod Jehoyada nodhi monego Joab kendo noyike mana e lope e thim.
35 Sai sarki ya sa Benahiya ɗan Yehohiyada ya zama shugaba a bisa mayaƙa a matsayin Yowab, ya kuma sa Zadok firist a wurin Abiyatar.
Ruoth noketo Benaya wuod Jehoyada jatend lweny kar Joab mi noketo Zadok jadolo kar Abiathar jadolo.
36 Sa’an nan sarki ya aika aka kawo Shimeyi, ya kuma ce masa, “Ka gina wa kanka gida a nan a Urushalima, ka zauna a ciki, kada ka kuskura ka tafi wani wuri.
Eka ruoth noluongo Shimei ire, mowachone niya, ger ot Jerusalem mondo idagie to kik iwuogi ni idhi kamoro amora.
37 Gama ran da ka fita, ka haye Kwarin Kidron, ka tabbata za ka mutu, alhakin jininka kuwa zai koma kanka.”
Chiengʼ ma iniwuogi ma ingʼadi Holo mar Kidron, to bed gadiera ni initho; kendo rembi enobed e wiyi.
38 Shimeyi ya amsa wa sarki ya ce, “Abin da ka faɗa yana da kyau. Bawanka zai yi kamar yadda ranka yă daɗe sarki, ya faɗa.” Shimeyi kuwa ya yi zama a Urushalima na dogon lokaci.
To Shimei nodwoko ruoth niya, “Gima iwacho ber, jatichni biro timo kaka ruodhe osewacho.” Shimei nodak Jerusalem kuom ndalo mangʼeny.
39 Amma bayan shekaru uku, biyu daga cikin bayin Shimeyi suka gudu zuwa wurin Akish ɗan Ma’aka, sarkin Gat. Aka faɗa wa Shimeyi cewa, “Bayinka suna a Gat.”
To bangʼ higni adek jotich Shimei ariyo noringo modhi ir Akish wuod Maaka, ruodh Gath kendo nowach ne Shimei niya, “Wasumbinigi ni Gath.”
40 Da jin haka, sai ya tashi ya shimfiɗa wa jakinsa abin zama, ya hau, ya tafi Gat wurin Akish domin neman bayinsa. Shimeyi kuwa ya dawo da su gida daga Gat.
Gikanyono noidho pundane kendo nodhi ir Akish kane en Gath komanyo wasumbinige, omiyo Shimei nodhi moduogogi.
41 Da aka faɗa wa Solomon cewa Shimeyi ya bar Urushalima zuwa Gat, har ya dawo.
Kane onyis Solomon ni Shimei nowuok Jerusalem modhi nyaka Gath kendo odwogo,
42 Sai sarki ya aika a kawo Shimeyi, ya ce masa, “Ban sa ka rantse da sunan Ubangiji, na kuma ja maka kunne cewa, ‘A ranar da ka kuskura ka bar nan ka tafi wani wuri, ka tabbata za ka mutu ba’? A lokacin ka ce mini, ‘Abin da ka faɗa yana da kyau. Zan kuwa kiyaye.’
ruoth noluongo Shimei mowachone niya, “Donge ne akwongʼora gi nying Jehova Nyasaye ka asiemi ni chiengʼ ma iniwuogi mondo idhi kamoro amora to ibed kingʼeyo ni initho? To e kindeno niwachona niya, ‘Gima iwacho ber, abiro luwo.’
43 To, me ya sa ba ka kiyaye rantsuwar da ka yi ga Ubangiji, ka kuma yi biyayya da umarnin da na ba ka ba?”
Angʼo momiyo ne ok irito singruokni ni Jehova Nyasaye kendo rito chik mane amiyi?”
44 Sarki ya ce wa Shimeyi, “Ka sani a zuciyarka dukan muguntar da ka yi wa mahaifina Dawuda. Yanzu Ubangiji zai sāka maka saboda muguntarka.
Ruoth nomedo wachone Shimei niya, “Ingʼeyo e chunyi richo duto mane itimone wuonwa Daudi. Koro Jehova Nyasaye biro chuli kuom richo duto mane itimo.
45 Amma za a yi wa Sarki Solomon albarka, sarautar Dawuda kuma za tă kasance a tsare a gaban Ubangiji har abada.”
To Ruoth Solomon ibiro gwedhi kendo kom loch mar Daudi biro siko kogurore e nyim Jehova Nyasaye nyaka chiengʼ.”
46 Sai sarki ya umarci Benahiya ɗan Yehohiyada, yă fita, yă bugi Shimeyi, yă kashe shi. Ya kuwa kashe shi. Mulki kuwa ya kahu sosai a hannun Solomon.
Eka ruoth nogolo chik ni Benaya wuod Jehoyada, mi nowuok modhi mogoyo Shimei monege. Pinyruoth koro nogurore e lwet Solomon.

< 1 Sarakuna 2 >