< 1 Sarakuna 2 >
1 Da lokacin mutuwar Dawuda ya yi kusa, sai ya gargaɗe Solomon ɗansa, ya ce,
Kad su se dani Davidovi približavali svome svršetku, zapovjedi David svome sinu Salomonu:
2 “Ina gab da bin hanyar da kowa a duniya zai bi. Saboda haka ka yi ƙarfin hali, ka nuna kanka namiji,
“Sada polazim na put sviju smrtnika. Ti budi hrabar i pokaži se čovjekom!
3 ka kiyaye abin da Ubangiji Allahnka yake bukata. Yi tafiya a hanyoyinsa, ka kiyaye ƙa’idodi, da umarnai, da dokoki, da kuma farillansa, kamar yadda suke a rubuce a Dokar Musa, don ka yi nasara a cikin kome da za ka yi, da kuma inda za ka tafi.
Slušaj naredbe Jahve, Boga svoga, idi njegovim stazama, drži se njegovih zakona, zapovijedi, naredaba i njegovih pouka, kako je napisano u Zakonu Mojsijevu, da bi uspio u svemu što poduzmeš i svagdje kamo se okreneš;
4 Ubangiji kuwa zai kiyaye alkawarinsa gare ni da ya ce, ‘In zuriyarka suka lura da yadda suke rayuwa, in kuma suka yi tafiya da aminci a gabana da dukan zuciyarsu, da kuma dukan ransu, ba za ka kāsa samun mutum a kujerar sarautar Isra’ila ba.’
da bi Jahve ispunio svoje obećanje koje mi je dao: 'Ako sinovi tvoji budu pazili na svome putu, vjerno hodeći preda mnom, svim srcem svojim i svom dušom svojom, uvijek će jedan od njih sjediti na prijestolju Izraelovu.'
5 “Yanzu fa, kai kanka ka san abin da Yowab ɗan Zeruhiya ya yi mini. Abin da ya yi wa shugabanni biyun nan na mayaƙan Isra’ila, wato, Abner ɗan Ner, da Amasa ɗan Yeter. Ya kashe su, ya kuma zub da jininsu a lokacin salama sai ka ce a fage yaƙi, da wannan jini ya yi ɗamara a gindinsa, ya kuma sa takalma a ƙafafunsa.
I sam znaš što mi je učinio Joab, sin Sarvijin, kako je učinio obojici vojskovođa Izraelovih: Abneru, sinu Nerovu, i Amasi, sinu Jeterovu, kad ih je ubio i time prolio krv u miru kao u ratu te omastio krvlju pojas oko bokova svojih i obuću na nogama svojim.
6 Ka yi da shi gwargwadon hikimarka, amma kada ka bari yă gangara kabari da furfura cikin salama. (Sheol )
Ti postupi po svom razboru i ne daj da mu sijeda kosa mirno počine u Podzemlju. (Sheol )
7 “Amma ka yi alheri ga’ya’yan Barzillai mutumin Gileyad, ka sa su kasance a cikin waɗanda suke ci a teburinka. Sun goyi bayana sa’ad da nake gudu daga ɗan’uwanka Absalom.
A sinovima Barzilaja Gileađanina vrati ljubav: neka budu među onima koji jedu za tvojim stolom jer su mi pomogli kad sam bježao pred tvojim bratom Abšalomom.
8 “Ka tuna, akwai kuma Shimeyi ɗan Gera, mutumin Benyamin daga Bahurim, wanda ya yi ta yin mini muguwar la’ana a ranar da na tafi Mahanayim. Sa’ad da ya gangara ya same ni a Urdun, na rantse masa da sunan Ubangiji na ce, ‘Ba zan kashe ka da takobi ba.’
Pred sobom imaš Šimeja, sina Gerina, Benjaminovca iz Bahurima, koji me užasnim kletvama proklinjao onoga dana kad sam bježao u Mahanajim. Ali mi je on sišao u susret na Jordan i zakleh mu se Jahvom: 'Neću te pogubiti mačem.'
9 Amma yanzu, kada ka ɗauke shi marar laifi. Kai mutum ne mai hikima; za ka san abin da za ka yi da shi. Ka kawo furfuransa zuwa kabari da jini.” (Sheol )
Ali mu ti toga ne opraštaj, jer si čovjek razborit, i već ćeš znati kako treba da postupiš te mu sijedu kosu s krvlju u Podzemlje spremiš.” (Sheol )
10 Sa’an nan Dawuda ya huta tare da kakanninsa. Sai aka binne shi a Birnin Dawuda.
I potom počinu David kraj otaca svojih i bi pokopan u Davidovu gradu.
11 Ya yi sarauta shekaru arba’in a bisa Isra’ila. Wato, shekaru bakwai a Hebron da kuma talatin da uku a Urushalima.
David je kraljevao nad Izraelom četrdeset godina: u Hebronu je kraljevao sedam godina, u Jeruzalemu je kraljevao trideset i tri godine.
12 Solomon kuwa ya zauna a kan kujerar sarautar mahaifinsa Dawuda, mulkinsa kuwa ya kahu sosai.
Salomon sjede na prijestolje Davida, svoga oca, i njegova se vlast veoma učvrsti.
13 To, sai Adoniya, ɗan Haggit ya tafi wurin Batsheba mahaifiyar Solomon. Ita kuwa ta tambaye shi ta ce, “Lafiya?” Ya amsa ya ce, “I, lafiya.”
Ali Adonija, sin Hagitin, dođe Bat-Šebi, majci Salomonovoj, i pade ničice pred njom. Ona ga upita: “Je li miroljubiv tvoj dolazak?” On odgovori: “Jest, miroljubiv je.”
14 Sa’an nan ya ƙara da cewa, “Ina da ɗan wani abin da zan faɗa miki.” Ta ce, “Faɗa.”
I nastavi: “Imam ti nešto reći.” Ona reče: “Govori.”
15 Sai ya ce, “Kamar yadda kika sani, mulkin nan nawa ne. Dukan Isra’ila suna ɗaukana a matsayin sarki. Amma abubuwa suka canja, sai mulkin ya koma ga ɗan’uwana; gama ya zo masa daga Ubangiji ne.
Tada će on: “Znaš i sama da je kraljevstvo pripadalo meni i da je sav Izrael očekivao da ću ja biti kralj. Ali mi je kraljevstvo izmaklo i pripalo je mome bratu, jer mu ga je Jahve namijenio.
16 Yanzu ina da roƙo guda da zan yi gare ki. Kada ki hana mini.” Ta ce, “Sai ka faɗa.”
Ja te sada samo jedno molim: nemoj me odbiti.” Ona reče: “Govori.”
17 Sai ya ci gaba, “In kin yarda, ki yi magana da Sarki Solomon, gama ba zai ƙi jinki ba, ki ce yă ba ni yarinyan nan, Abishag, mutuniyar Shunam, tă zama matata.”
A on nastavi: “Reci, molim te, kralju Salomonu - jer tebe neće odbiti - neka mi dade za ženu Abišagu Šunamku!”
18 Batsheba ta ce, “Da kyau, zan yi magana da sarki dominka.”
A Bat-Šeba odgovori: “Dobro, govorit ću kralju o tebi.”
19 Sai Batsheba ta tafi wurin Sarki Solomon don tă yi masa magana a kan Adoniya. Sarki ya miƙe tsaye don yă sadu da ita, ya rusuna mata, ya kuma zauna a kujerar sarautarsa. Ya sa aka kawo wa mahaifiyar sarki kujerar sarauta, ta kuwa zauna a gefen damansa.
Kada dakle uđe Bat-Šeba kralju Salomonu da govori o Adoniji, ustade kralj i pođe joj u susret, pokloni se pred njom, zatim sjede na svoje prijestolje i zapovjedi te namjestiše sjedalicu za kraljicu majku, i ona mu sjede s desne strane.
20 Ta ce, “Ina da ɗan roƙon da zan nema ka yi mini. Ina fata ba za ka hana ni ba.” Sai sarki ya amsa ya ce, “Mahaifiyata, sai ki faɗa in ji, ba zan hana miki ba.”
Tada mu reče: “Nešto bih zaiskala od tebe, nemoj me odbiti.” Kralj joj odgovori: “Traži, majko, jer te neću odbiti.”
21 Saboda haka sai ta ce, “Ka sa a ba wa ɗan’uwanka Adoniya, Abishag mutuniyar Shunam tă zama matarsa.”
Ona nastavi: “Neka se dade Abišaga Šunamka tvome bratu Adoniji za ženu.”
22 Sarki Solomon ya amsa wa mahaifiyarsa ya ce, “Me ya sa kika roƙar wa Adoniya Abishag mutuniyar Shunam kawai? Ki ma sa a ba shi mulkin mana. Ai, shi yayana ne. I, ki roƙa dominsa, da domin Abiyatar firist, da kuma domin Yowab ɗan Zeruhiya mana!”
Kralj Salomon odgovori i reče svojoj majci: “Zašto tražiš Abišagu Šunamku za Adoniju? Traži odmah i kraljevstvo za njega! Jer on je moj stariji brat, a uz njega je svećenik Ebjatar i Joab, sin Sarvijin!”
23 Sai Sarki Solomon ya rantse da sunan Ubangiji ya ce, “Bari Allah yă yi mini hukunci mai tsanani, idan ban sa Adoniya ya biya wannan roƙo da ransa ba!
Tada se kralj Salomon zakle Jahvom: “Neka mi Bog učini ovo zlo i neka mi doda drugo ako Adonija nije to izrekao danas po cijenu svoga života!
24 Yanzu kuwa, muddin Ubangiji yana a raye, shi wanda ya kafa ni sosai a kan kujerar sarautar mahaifina Dawuda, ya kuma kafa mini mulki kamar yadda ya yi alkawari; za a kashe Adoniya yau!”
Živoga mi Jahve, koji me potvrdio i posadio na prijestolje oca moga Davida i koji mi je dao dom kako je obećao: još danas će Adonija umrijeti.”
25 Saboda haka Sarki Solomon ya umarci Benahiya ɗan Yehohiyada yă kashe Adoniya; ya kuwa kashe shi.
I kralj Salomon posla Benaju, sina Jojadina, koji ga udari te Adonija umrije.
26 Ga Abiyatar firist kuwa sarki ya ce, “Tafi gonarka a Anatot. Ka cancanci ka mutu, amma ba zan kashe ka yanzu ba, domin ka ɗauki akwatin alkawarin Ubangiji Mai Iko Duka a gaban mahaifina Dawuda, ka kuma sha wahala tare mahaifina.”
Svećeniku Ebjataru kralj zatim naredi: “Idi u Anatot na svoj posjed. Zaslužio si smrt, ali te neću pogubiti danas jer si nosio Jahvin Kovčeg pred ocem mojim Davidom i podijelio si sve patnje s mojim ocem.”
27 Saboda haka Solomon ya cire Abiyatar daga aikin firist na Ubangiji, ya cika maganar da Ubangiji ya yi a Shilo game da gidan Eli.
I Salomon isključi Ebjatara iz svećenstva Jahvina da tako ispuni Jahvinu riječ koju je izrekao protiv doma Elijeva u Šilu.
28 Sa’ad da labarin ya kai wurin Yowab, wanda ya haɗa kai da Adoniya, ko da yake bai haɗa kai da Absalom ba, sai ya gudu zuwa tentin Ubangiji, ya kama ƙahonin bagade ya riƙe.
Kada je glas stigao Joabu - Joab bijaše pristao uz Adoniju, premda se nije priključio Abšalomu - on uteče u Šator Jahvin i uhvati se za rogove žrtvenika.
29 Aka faɗa wa Sarki Solomon cewa Yowab ya gudu zuwa tentin Ubangiji, yana kuma kusa da bagade. Sai Solomon ya umarci Benahiya ɗan Yehohiyada ya ce, “Je ka kashe shi!”
I dojaviše kralju Salomonu: “Joab je pobjegao u Šator Jahvin, eno ga pokraj žrtvenika.” Tada Salomon poruči Joabu: “Što se držiš žrtvenika?” Joab odgovori: “Uplašio sam se tebe i pobjegao sam pred Jahvu.” Tada Salomon naredi Benaji, sinu Jojadinu: “Idi i ubij ga!”
30 Sai Benahiya ya shiga tentin Ubangiji ya ce wa Yowab, “Sarki ya ce, ‘Ka fita!’” Amma Yowab ya amsa ya ce, “A’a, a nan zan mutu.” Sai Benahiya ya ce wa sarki, “Ga yadda Yowab ya amsa mini.”
Benaja ode u Šator Jahvin i reče Joabu: “Po naredbi kraljevoj: iziđi!” On odgovori: “Neću, želim ovdje umrijeti!” Benaja javi kralju: “Eto što mi je rekao Joab i što mi je odgovorio.”
31 Sai sarki ya umarci Benahiya ya ce, “Yi kamar yadda ya faɗa. Ka kashe shi, ka kuma binne shi, ka wanke ni da gidan mahaifina daga laifin jini marasa laifin da Yowab ya zubar.
Kralj mu reče: “Učini kako je rekao: ubij ga, zatim pokopaj. Tako ćeš danas skinuti s mene i doma oca moga nevinu krv koju je Joab prolio.
32 Ubangiji zai sāka masa saboda jinin da ya zubar, domin ba da sanin mahaifina Dawuda ne ya fāɗa wa mutum biyun nan da takobi ba. Dukansu biyu, Abner ɗan Ner, shugaban mayaƙan Isra’ila, da Amasa ɗan Yeter, shugaban mayaƙan Yahuda, mutane ne mafi kyau da kuma mafi adalci fiye da shi.
Jahve će učiniti da krv njegova padne na njegovu glavu, jer je ubio dva čovjeka pravednika i bolja od sebe; ubio ih je mačem bez znanja moga oca Davida: Abnera, sina Nerova, vođu vojske Izraelove, i Amasu, sina Jeterova, vojvodu judejskoga.
33 Bari alhakin jininsu yă koma a kan Yowab da kuma zuriyarsa har abada. Amma bari salamar Ubangiji tă kasance a kan Dawuda da zuriyarsa, da gidansa, da kuma mulkinsa, har abada.”
Neka njihova krv padne na glavu Joaba i njegova potomstva dovijeka, a Davidu, njegovu potomstvu, vladalačkoj kući i prijestolju neka od Jahve bude trajan mir.”
34 Sai Benahiya ɗan Yehohiyada ya haura ya bugi Yowab, ya kashe shi, ya kuwa binne shi a gidansa a ƙauye.
I ode Benaja, sin Jojadin, obori se na Joaba i usmrti ga. Pokopali su Joaba u njegovu domu u pustinji.
35 Sai sarki ya sa Benahiya ɗan Yehohiyada ya zama shugaba a bisa mayaƙa a matsayin Yowab, ya kuma sa Zadok firist a wurin Abiyatar.
Mjesto njega postavi kralj na čelo vojske Benaju, sina Jojadina, a na mjesto Ebjatara postavi svećenika Sadoka.
36 Sa’an nan sarki ya aika aka kawo Shimeyi, ya kuma ce masa, “Ka gina wa kanka gida a nan a Urushalima, ka zauna a ciki, kada ka kuskura ka tafi wani wuri.
Salomon pozva Šimeja i reče mu: “Sagradi sebi kuću u Jeruzalemu: tu stanuj, i nikamo odatle ne izlazi.
37 Gama ran da ka fita, ka haye Kwarin Kidron, ka tabbata za ka mutu, alhakin jininka kuwa zai koma kanka.”
Onoga dana kad iziđeš i prijeđeš potok Kidron, znaj dobro da ćeš umrijeti. Krv tvoja na glavu tvoju.”
38 Shimeyi ya amsa wa sarki ya ce, “Abin da ka faɗa yana da kyau. Bawanka zai yi kamar yadda ranka yă daɗe sarki, ya faɗa.” Shimeyi kuwa ya yi zama a Urushalima na dogon lokaci.
Šimej odgovori kralju: “Dobro. Kako moj gospodar kralj kaže, tako će učiniti sluga tvoj.” I Šimej dugo življaše u Jeruzalemu.
39 Amma bayan shekaru uku, biyu daga cikin bayin Shimeyi suka gudu zuwa wurin Akish ɗan Ma’aka, sarkin Gat. Aka faɗa wa Shimeyi cewa, “Bayinka suna a Gat.”
Ali poslije tri godine dogodi se te Šimeju pobjegoše dvojica slugu k Akišu, sinu Maakinu, kralju gatskom. I dojaviše Šimeju: “Eno ti slugu u Gatu.”
40 Da jin haka, sai ya tashi ya shimfiɗa wa jakinsa abin zama, ya hau, ya tafi Gat wurin Akish domin neman bayinsa. Shimeyi kuwa ya dawo da su gida daga Gat.
Tada usta Šimej, osedla magarca i ode u Gat, k Akišu, da traži svoje sluge. I vratio se Šimej i doveo svoje sluge iz Gata.
41 Da aka faɗa wa Solomon cewa Shimeyi ya bar Urushalima zuwa Gat, har ya dawo.
I javiše Salomonu: “Šimej otišao iz Jeruzalema u Gat i vratio se.”
42 Sai sarki ya aika a kawo Shimeyi, ya ce masa, “Ban sa ka rantse da sunan Ubangiji, na kuma ja maka kunne cewa, ‘A ranar da ka kuskura ka bar nan ka tafi wani wuri, ka tabbata za ka mutu ba’? A lokacin ka ce mini, ‘Abin da ka faɗa yana da kyau. Zan kuwa kiyaye.’
Kralj pozva Šimeja i reče mu: “Nisam li ti se zakleo Jahvom i strogo te opomenuo: 'Onoga dana kad budeš izišao i pošao bilo kamo, znaj dobro da ćeš umrijeti!' A ti si mi tada odgovorio: 'Dobra je riječ koju sam čuo.'
43 To, me ya sa ba ka kiyaye rantsuwar da ka yi ga Ubangiji, ka kuma yi biyayya da umarnin da na ba ka ba?”
Zašto nisi održao zakletvu Jahvinu i zapovijed koju sam ti dao?”
44 Sarki ya ce wa Shimeyi, “Ka sani a zuciyarka dukan muguntar da ka yi wa mahaifina Dawuda. Yanzu Ubangiji zai sāka maka saboda muguntarka.
Još reče kralj Šimeju: “Ti znaš sve zlo koje si učinio mome ocu Davidu. Tvoje je srce toga svjesno. Jahve neka učini da se tvoja zloća obori na tvoju glavu.
45 Amma za a yi wa Sarki Solomon albarka, sarautar Dawuda kuma za tă kasance a tsare a gaban Ubangiji har abada.”
A blagoslovljen je kralj Salomon, i prijestolje će Davidovo biti čvrsto pred Jahvom dovijeka.”
46 Sai sarki ya umarci Benahiya ɗan Yehohiyada, yă fita, yă bugi Shimeyi, yă kashe shi. Ya kuwa kashe shi. Mulki kuwa ya kahu sosai a hannun Solomon.
I zapovjedi kralj Benaji, sinu Jojadinu, te on iziđe i udari Šimeja i tako Šimej umrije. Tako se učvrstilo kraljevstvo u ruci Salomonovoj.