< 1 Sarakuna 19 >

1 Ahab fa ya faɗa wa Yezebel kome da Iliya ya yi, da yadda ya karkashe dukan annabawan da takobi.
UAhabi wasetshela uJezebeli konke uElija ayekwenzile, labo bonke ababulalayo, bonke abaprofethi, ngenkemba.
2 Saboda haka Yezebel ta aika da ɗan aika wa Iliya yă faɗa masa, “Bari alloli su hukunta ni da tsanani, in war haka gobe ban mai da ranka kamar na ɗaya daga cikin annabawan Ba’al ba.”
Khona uJezebeli wathuma isithunywa kuElija esithi: Kabenze njalo onkulunkulu, bengezelele njalo, uba ngalesisikhathi kusasa ngingenzi impilo yakho ibe njengempilo yomunye wabo.
3 Iliya ya ji tsoro, ya gudu don yă ceci ransa. Sa’ad da ya kai Beyersheba a Yahuda, sai ya bar bawansa a can.
Esekubonile, wasukuma, wahamba ngenxa yempilo yakhe, wafika eBherishebha engeyakoJuda, watshiya khona inceku yakhe.
4 Shi kuma ya yi tafiya yini guda zuwa cikin hamada. Ya zo wurin wani itacen tsintsiya, ya zauna a ƙarƙashinsa, ya roƙa yă mutu. Ya ce, “Ya ishe ni haka, Ubangiji, ka ɗauki raina; ban fi kakannina ba.”
Kodwa yena wahamba uhambo losuku enkangala, wafika wahlala ngaphansi kwesihlahla serotemu, wacela ukuthi umphefumulo wakhe ufe, wathi: Kwanele, khathesi, Nkosi, thatha impilo yami, ngoba kangingcono kulabobaba.
5 Sa’an nan ya kwanta a ƙarƙashin itacen ya yi barci. Farat ɗaya sai wani mala’ika ya taɓa shi, ya ce, “Tashi ka ci abinci.”
Esecambalele elele ngaphansi kwesihlahla esithile serotemu, khangela-ke, khonokho ingilosi yamthinta, yathi kuye: Vuka udle.
6 Ya duba kewaye, sai ga wainar burodi kusa da kansa a bisa garwashin wuta mai zafi, da kuma tulun ruwa. Ya ci, ya sha, sa’an nan ya sāke kwanta.
Wasethalaza, khangela-ke, ekhanda lakhe iqebelengwana losiwe emalahleni, lesigxingi samanzi; wasesidla wanatha, waphinda walala.
7 Mala’ikan Ubangiji ya sāke dawowa sau na biyu ya taɓa shi, ya ce, “Tashi ka ci abinci, gama tafiyar za tă yi maka yawa.”
Ingilosi yeNkosi yasifika ngokwesibili, yamthinta yathi: Vuka udle; ngoba uhambo lwakho lukhulu kakhulu kuwe.
8 Saboda haka ya tashi ya ci, ya kuma sha. Ta wurin ƙarfin da ya samu saboda wannan abinci, ya yi tafiya yini arba’in da dare arba’in, sai da ya kai Horeb, dutsen Allah.
Wasevuka wadla wanatha, wahamba ngamandla alokhokudla insuku ezingamatshumi amane lobusuku obungamatshumi amane, waze wafika eHorebe intaba kaNkulunkulu.
9 A can ya shiga kogo ya kwana. Sai maganar Ubangiji ta zo masa, ta ce, “Me kake yi a nan, Iliya?”
Wasengena lapho ebhalwini, walala khona ubusuku. Khangela-ke, ilizwi leNkosi lafika kuye lathi kuye: Wenzani lapha, Elija?
10 Ya amsa, ya ce, “Ina kishi dominka Ubangiji, Allah Maɗaukaki. Isra’ilawa sun ƙi alkawarinka, suka rurrushe bagadanka, suka kuma kashe annabawanka da takobi. Ni ne kaɗai na rage, yanzu, ni ma suna ƙoƙari su kashe ni.”
Wathi: Bengitshiseka lokutshisekela iNkosi, uNkulunkulu wamabandla, ngoba abantwana bakoIsrayeli basitshiyile isivumelwano sakho, badiliza amalathi akho, babulala abaprofethi bakho ngenkemba; yimi ngedwa engiseleyo, njalo badinga impilo yami ukuyisusa.
11 Sai Ubangiji ya ce, “Fita ka tsaya a kan dutse a gaban Ubangiji, gama Ubangiji yana shirin wucewa.” Sai ga babbar iska mai ƙarfi ta tsage duwatsu, ta kuma ragargaza duwatsu a gaban Ubangiji, amma Ubangiji ba ya cikin iskar. Bayan iskar sai aka yi girgizar ƙasa, amma Ubangiji ba ya cikin girgizar ƙasa.
Wasesithi: Phuma ume entabeni phambi kweNkosi. Khangela-ke, iNkosi yadlula. Umoya omkhulu olamandla wasudabula izintaba, waqhekeza amadwala phambi kweNkosi; kodwa iNkosi yayingekho emoyeni. Lemva komoya ukunyikinyeka komhlaba; kodwa iNkosi yayingekho ekunyikinyekeni komhlaba.
12 Bayan girgizar ƙasa, sai ga wuta, amma Ubangiji ba ya cikin wuta. Bayan wutar kuma sai ga wata’yar murya.
Lemva kokunyikinyeka komhlaba umlilo; kodwa iNkosi yayingekho emlilweni. Njalo emva komlilo ilizwi elincinyane elinyenyezayo.
13 Sa’ad da Iliya ya ji ta, ya ja mayafinsa ya rufe fuskarsa, ya fita ya tsaya a bakin kogon. Sai ya ji murya ta ce masa, “Me kake yi a nan, Iliya?”
Kwasekuthi uElija elizwa, wathandela ubuso bakhe ngesembatho sakhe, waphuma wema emlonyeni wobhalu. Khangela-ke, leza kuye ilizwi lathi: Wenzani lapha, Elija?
14 Ya amsa, ya ce, “Ina kishi dominka Ubangiji, Allah Maɗaukaki. Isra’ilawa sun ƙi alkawarinka, suka rurrushe bagadanka, suka kuma kashe annabawanka da takobi. Ni ne kaɗai na rage, yanzu, ni ma suna ƙoƙari su kashe ni.”
Wathi: Bengitshisekela lokutshisekela iNkosi, uNkulunkulu wamabandla, ngoba abantwana bakoIsrayeli basitshiyile isivumelwano sakho, badiliza amalathi akho, babulala abaprofethi bakho ngenkemba; yimi ngedwa engiseleyo, njalo badinga impilo yami ukuyisusa.
15 Sai Ubangiji ya ce masa, “Ka koma ta hanyar da ka zo, ka tafi Hamadan Damaskus. Sa’ad da ka kai can, ka shafe Hazayel yă zama sarki bisa Aram.
INkosi yasisithi kuye: Hamba, ubuyele ngendlela yakho uye enkangala yeDamaseko; lapho usufikile ugcobe uHazayeli abe yinkosi phezu kweSiriya,
16 Ka kuma shafe Yehu ɗan Nimshi yă zama sarkin Isra’ila, ka shafe Elisha ɗan Shafat daga Abel-Mehola yă gāje ka a matsayin annabi.
loJehu indodana kaNimshi umgcobe abe yinkosi phezu kukaIsrayeli, loElisha indodana kaShafati weAbeli-Mehola umgcobe abe ngumprofethi esikhundleni sakho.
17 Yehu zai kashe duk wani wanda ya tsere wa takobin Hazayel, Elisha kuwa zai kashe duk wani wanda ya tsere wa takobin Yehu.
Kuzakuthi-ke ozaphepha enkembeni kaHazayeli uJehu uzambulala, lozaphepha enkembeni kaJehu uElisha uzambulala.
18 Duk da haka zan bar mutane dubu bakwai na Isra’ila waɗanda ba su rusuna da gwiwansu wa Ba’al ba, ba su kuma sumbace shi da bakinsu ba.”
Kodwa ngitshiyile koIsrayeli abazinkulungwane eziyisikhombisa, wonke amadolo angazanga aguqe kuBhali, lawo wonke umlomo ongazanga umange.
19 Sai Iliya ya tafi daga can ya sami Elisha ɗan Shafat, yana noma da shanu goma sha biyu masu garman noma, shi kansa yana jan na goma sha biyun. Iliya ya tafi wurinsa ya jefa mayafinsa a kan Elisha.
Wasesuka lapho, wafica uElisha indodana kaShafati; wayelima ngezipani zenkabi zamajogwe alitshumi lambili phambi kwakhe, yena wayelesetshumi lambili. UElija wesesedlula eceleni kwakhe, waphosela isembatho sakhe phezu kwakhe.
20 Sai Elisha ya bar shanun, ya ruga ya bi Iliya. Ya ce, “Bari in sumbace mahaifina da mahaifiyata, in yi musu bankwana, sa’an nan in zo in bi ka.” Iliya ya ce, “Koma! Me na yi maka?”
Wasetshiya izinkabi, wagijima elandela uElija, wathi: Ake ngange ubaba lomama, besengikulandela. Wasesithi kuye: Hamba ubuyele, ngoba ngenzeni kuwe?
21 Sai Elisha ya bar shi, ya koma, ya ɗauki shanunsa ya yayyanka. Ya ƙone kayan garman noman don yă dafa naman, ya kuma ba wa mutane naman, suka kuwa ci. Sa’an nan ya tashi, ya bi Iliya, ya kuma zama mai hidimarsa.
Wasebuyela ekumlandeleni, wathatha isipani senkabi, wasihlaba, langezikhali zenkabi wapheka inyama yazo, wayinika abantu, bayidla. Wasesuka elandela uElija, wamsebenzela.

< 1 Sarakuna 19 >