< 1 Sarakuna 19 >

1 Ahab fa ya faɗa wa Yezebel kome da Iliya ya yi, da yadda ya karkashe dukan annabawan da takobi.
When Ahab got home, he told [his wife] Jezebel what Elijah had done. He told her that Elijah had killed all the prophets of Baal.
2 Saboda haka Yezebel ta aika da ɗan aika wa Iliya yă faɗa masa, “Bari alloli su hukunta ni da tsanani, in war haka gobe ban mai da ranka kamar na ɗaya daga cikin annabawan Ba’al ba.”
So Jezebel sent this message to Elijah: “By this time tomorrow I will have [killed] you, just like you [killed all those prophets of Baal]. If I do not do that, I hope the gods will kill me.”
3 Iliya ya ji tsoro, ya gudu don yă ceci ransa. Sa’ad da ya kai Beyersheba a Yahuda, sai ya bar bawansa a can.
When Elijah received [her message], he was afraid. So [taking his servant with him], he fled in order that he would not be killed. He went [far south] to Beersheba, in Judah. He left his servant there.
4 Shi kuma ya yi tafiya yini guda zuwa cikin hamada. Ya zo wurin wani itacen tsintsiya, ya zauna a ƙarƙashinsa, ya roƙa yă mutu. Ya ce, “Ya ishe ni haka, Ubangiji, ka ɗauki raina; ban fi kakannina ba.”
Then he went by himself further [south] into the desert. He walked all day. He sat down under a broom tree and prayed that [Yahweh] would allow him to die. He said, “Yahweh, I’ve had enough. So allow me to die, because for me to live is no better than [being with] my ancestors [who have died].”
5 Sa’an nan ya kwanta a ƙarƙashin itacen ya yi barci. Farat ɗaya sai wani mala’ika ya taɓa shi, ya ce, “Tashi ka ci abinci.”
Then he lay down under the broom tree and slept. But while he was sleeping, an angel touched him and [woke him up and] said to him, “Get up and eat some food!”
6 Ya duba kewaye, sai ga wainar burodi kusa da kansa a bisa garwashin wuta mai zafi, da kuma tulun ruwa. Ya ci, ya sha, sa’an nan ya sāke kwanta.
Elijah looked around and saw some bread which had been baked on hot stones, and he also saw a jar of water. So he ate some bread and drank some water and lay down [to sleep] again.
7 Mala’ikan Ubangiji ya sāke dawowa sau na biyu ya taɓa shi, ya ce, “Tashi ka ci abinci, gama tafiyar za tă yi maka yawa.”
Then the angel [who had been sent by] Yahweh came again and touched him, and said, “Get up and eat some [more] food, because you need [more strength] to go on a long journey.”
8 Saboda haka ya tashi ya ci, ya kuma sha. Ta wurin ƙarfin da ya samu saboda wannan abinci, ya yi tafiya yini arba’in da dare arba’in, sai da ya kai Horeb, dutsen Allah.
So he got up and ate and drank some more, and because of doing that, he got enough strength to enable him to travel for forty days and nights to Sinai Mountain, the mountain [that was dedicated to] God.
9 A can ya shiga kogo ya kwana. Sai maganar Ubangiji ta zo masa, ta ce, “Me kake yi a nan, Iliya?”
He went into a cave there and slept there that night. [The next morning, ] Yahweh said to him “Elijah, why are you here?”
10 Ya amsa, ya ce, “Ina kishi dominka Ubangiji, Allah Maɗaukaki. Isra’ilawa sun ƙi alkawarinka, suka rurrushe bagadanka, suka kuma kashe annabawanka da takobi. Ni ne kaɗai na rage, yanzu, ni ma suna ƙoƙari su kashe ni.”
Elijah replied, “I have zealously served you, Yahweh, God Almighty. But the Israeli people have broken the agreement that they made with you. They have torn down your altars, and they have killed all of your prophets. I am the only one whom they have not killed, and now they are trying to kill me, too. [So I am running away from them].”
11 Sai Ubangiji ya ce, “Fita ka tsaya a kan dutse a gaban Ubangiji, gama Ubangiji yana shirin wucewa.” Sai ga babbar iska mai ƙarfi ta tsage duwatsu, ta kuma ragargaza duwatsu a gaban Ubangiji, amma Ubangiji ba ya cikin iskar. Bayan iskar sai aka yi girgizar ƙasa, amma Ubangiji ba ya cikin girgizar ƙasa.
Yahweh said to him, “Go out and stand in front of me on this mountain while I pass by.” [Suddenly] a strong windstorm struck the mountain. As a result, rocks were loosened from the mountainside. But Yahweh was not in the wind. Then there was an earthquake, but Yahweh was not in the earthquake.
12 Bayan girgizar ƙasa, sai ga wuta, amma Ubangiji ba ya cikin wuta. Bayan wutar kuma sai ga wata’yar murya.
Then there was a fire, but Yahweh was not in the fire. Then there was a sound like someone whispering quietly.
13 Sa’ad da Iliya ya ji ta, ya ja mayafinsa ya rufe fuskarsa, ya fita ya tsaya a bakin kogon. Sai ya ji murya ta ce masa, “Me kake yi a nan, Iliya?”
When Elijah heard that, he wrapped his cloak around his face. He went out of the cave and stood at its entrance. And he heard Yahweh speaking to him, saying again, “Elijah, why are you here?”
14 Ya amsa, ya ce, “Ina kishi dominka Ubangiji, Allah Maɗaukaki. Isra’ilawa sun ƙi alkawarinka, suka rurrushe bagadanka, suka kuma kashe annabawanka da takobi. Ni ne kaɗai na rage, yanzu, ni ma suna ƙoƙari su kashe ni.”
He replied again, “I have zealously served you, Yahweh, God Almighty. But the Israeli people have broken the agreement that they made with you. They have torn down your altars, and they have killed all of your prophets. I am the only one whom they have not killed, and now they are trying to kill me, too. [So I am running away from them].”
15 Sai Ubangiji ya ce masa, “Ka koma ta hanyar da ka zo, ka tafi Hamadan Damaskus. Sa’ad da ka kai can, ka shafe Hazayel yă zama sarki bisa Aram.
Then Yahweh told him, “Go back to the desert near Damascus. When you arrive there, anoint [with olive oil] a man named Hazael, [to appoint him] to be the king of Syria.
16 Ka kuma shafe Yehu ɗan Nimshi yă zama sarkin Isra’ila, ka shafe Elisha ɗan Shafat daga Abel-Mehola yă gāje ka a matsayin annabi.
Then anoint Jehu, the son of Nimshi, to be the king of Israel, and also anoint Elisha the son of Shaphat, from Abel-Meholah [town], to become my prophet after you are dead.
17 Yehu zai kashe duk wani wanda ya tsere wa takobin Hazayel, Elisha kuwa zai kashe duk wani wanda ya tsere wa takobin Yehu.
Hazael’s army [will kill many people, and] those who escape from [being killed by] his army will be killed by Jehu’s [army], and those who escape from [being killed by] Jehu’s army will be killed by Elisha.
18 Duk da haka zan bar mutane dubu bakwai na Isra’ila waɗanda ba su rusuna da gwiwansu wa Ba’al ba, ba su kuma sumbace shi da bakinsu ba.”
But [you need to know that] there are still 7,000 people in Israel who have never bowed to [worship] Baal or kissed his [idol].”
19 Sai Iliya ya tafi daga can ya sami Elisha ɗan Shafat, yana noma da shanu goma sha biyu masu garman noma, shi kansa yana jan na goma sha biyun. Iliya ya tafi wurinsa ya jefa mayafinsa a kan Elisha.
So Elijah went [to Syria] and found Elisha as he was plowing a field with a team of oxen. There were eleven other men who were in front of him, plowing with teams of oxen in the same field. Elijah went to Elisha, and took off his own coat and put it on Elisha, [to show Elisha that he wanted him to take his place as a prophet. Then he started to walk away].
20 Sai Elisha ya bar shanun, ya ruga ya bi Iliya. Ya ce, “Bari in sumbace mahaifina da mahaifiyata, in yi musu bankwana, sa’an nan in zo in bi ka.” Iliya ya ce, “Koma! Me na yi maka?”
Elisha left the oxen standing there and ran after Elijah, and said to him, “I will go with you, but first let me kiss my parents goodbye.” Elijah replied, “Okay, go home. But do not forget why I have [given my cloak] to you!”
21 Sai Elisha ya bar shi, ya koma, ya ɗauki shanunsa ya yayyanka. Ya ƙone kayan garman noman don yă dafa naman, ya kuma ba wa mutane naman, suka kuwa ci. Sa’an nan ya tashi, ya bi Iliya, ya kuma zama mai hidimarsa.
So Elisha went back [to his oxen]. He killed them [and cut them in pieces] and used the wood from the plow to build a fire to roast the meat. He distributed the meat to the other people [in his town], and they all ate some. Then he went with Elijah and became his helper.

< 1 Sarakuna 19 >