< 1 Sarakuna 19 >
1 Ahab fa ya faɗa wa Yezebel kome da Iliya ya yi, da yadda ya karkashe dukan annabawan da takobi.
Ahab gave Jezebel news of all Elijah had done, and how he had put all the prophets to death with the sword.
2 Saboda haka Yezebel ta aika da ɗan aika wa Iliya yă faɗa masa, “Bari alloli su hukunta ni da tsanani, in war haka gobe ban mai da ranka kamar na ɗaya daga cikin annabawan Ba’al ba.”
Then Jezebel sent a servant to Elijah, saying, May the gods' punishment be on me if I do not make your life like the life of one of them by tomorrow about this time.
3 Iliya ya ji tsoro, ya gudu don yă ceci ransa. Sa’ad da ya kai Beyersheba a Yahuda, sai ya bar bawansa a can.
And he got up, fearing for his life, and went in flight, and came to Beer-sheba in Judah, parting there from his servant;
4 Shi kuma ya yi tafiya yini guda zuwa cikin hamada. Ya zo wurin wani itacen tsintsiya, ya zauna a ƙarƙashinsa, ya roƙa yă mutu. Ya ce, “Ya ishe ni haka, Ubangiji, ka ɗauki raina; ban fi kakannina ba.”
While he himself went a day's journey into the waste land, and took a seat under a broom-plant, desiring for himself only death; for he said, It is enough: now, O Lord, take away my life, for I am no better than my fathers.
5 Sa’an nan ya kwanta a ƙarƙashin itacen ya yi barci. Farat ɗaya sai wani mala’ika ya taɓa shi, ya ce, “Tashi ka ci abinci.”
And stretching himself on the earth, he went to sleep under the broom-plant; but an angel, touching him, said to him, Get up and have some food.
6 Ya duba kewaye, sai ga wainar burodi kusa da kansa a bisa garwashin wuta mai zafi, da kuma tulun ruwa. Ya ci, ya sha, sa’an nan ya sāke kwanta.
And looking up, he saw by his head a cake cooked on the stones and a bottle of water. So he took food and drink and went to sleep again.
7 Mala’ikan Ubangiji ya sāke dawowa sau na biyu ya taɓa shi, ya ce, “Tashi ka ci abinci, gama tafiyar za tă yi maka yawa.”
And the angel of the Lord came again a second time, and touching him said, Get up and have some food, or the journey will be overmuch for your strength.
8 Saboda haka ya tashi ya ci, ya kuma sha. Ta wurin ƙarfin da ya samu saboda wannan abinci, ya yi tafiya yini arba’in da dare arba’in, sai da ya kai Horeb, dutsen Allah.
So he got up and took food and drink, and in the strength of that food he went on for forty days and nights, to Horeb, the mountain of God.
9 A can ya shiga kogo ya kwana. Sai maganar Ubangiji ta zo masa, ta ce, “Me kake yi a nan, Iliya?”
And there he went into a hole in the rock for the night; then the word of the Lord came to him, saying, What are you doing here, Elijah?
10 Ya amsa, ya ce, “Ina kishi dominka Ubangiji, Allah Maɗaukaki. Isra’ilawa sun ƙi alkawarinka, suka rurrushe bagadanka, suka kuma kashe annabawanka da takobi. Ni ne kaɗai na rage, yanzu, ni ma suna ƙoƙari su kashe ni.”
And he said, I have been burning for the honour of the Lord, the God of armies; for the children of Israel have not kept your agreement; they have made destruction of your altars, and have put your prophets to death with the sword: till I, even I, am the only one living; and now they are attempting to take away my life.
11 Sai Ubangiji ya ce, “Fita ka tsaya a kan dutse a gaban Ubangiji, gama Ubangiji yana shirin wucewa.” Sai ga babbar iska mai ƙarfi ta tsage duwatsu, ta kuma ragargaza duwatsu a gaban Ubangiji, amma Ubangiji ba ya cikin iskar. Bayan iskar sai aka yi girgizar ƙasa, amma Ubangiji ba ya cikin girgizar ƙasa.
Then he said, Go out and take your place on the mountain before the Lord. Then the Lord went by, and mountains were parted by the force of a great wind, and rocks were broken before the Lord; but the Lord was not in the wind. And after the wind there was an earth-shock, but the Lord was not in the earth-shock.
12 Bayan girgizar ƙasa, sai ga wuta, amma Ubangiji ba ya cikin wuta. Bayan wutar kuma sai ga wata’yar murya.
And after the earth-shock a fire, but the Lord was not in the fire. And after the fire, the sound of a soft breath.
13 Sa’ad da Iliya ya ji ta, ya ja mayafinsa ya rufe fuskarsa, ya fita ya tsaya a bakin kogon. Sai ya ji murya ta ce masa, “Me kake yi a nan, Iliya?”
And Elijah, hearing it, went out, covering his face with his robe, and took his place in the opening of the hole. And there a voice came to him saying, What are you doing here, Elijah?
14 Ya amsa, ya ce, “Ina kishi dominka Ubangiji, Allah Maɗaukaki. Isra’ilawa sun ƙi alkawarinka, suka rurrushe bagadanka, suka kuma kashe annabawanka da takobi. Ni ne kaɗai na rage, yanzu, ni ma suna ƙoƙari su kashe ni.”
And he said, I have been burning for the honour of the Lord, the God of armies; for the children of Israel have not kept your agreement; they have had your altars broken down, and have put your prophets to death with the sword: till I, even I, am the only one living; and now they are attempting to take away my life.
15 Sai Ubangiji ya ce masa, “Ka koma ta hanyar da ka zo, ka tafi Hamadan Damaskus. Sa’ad da ka kai can, ka shafe Hazayel yă zama sarki bisa Aram.
And the Lord said to him, Go back on your way through the waste land to Damascus; and when you come there, put the holy oil on Hazael to make him king over Aram;
16 Ka kuma shafe Yehu ɗan Nimshi yă zama sarkin Isra’ila, ka shafe Elisha ɗan Shafat daga Abel-Mehola yă gāje ka a matsayin annabi.
And on Jehu, son of Nimshi, making him king over Israel; and on Elisha, the son of Shaphat of Abel-meholah, to be prophet in your place.
17 Yehu zai kashe duk wani wanda ya tsere wa takobin Hazayel, Elisha kuwa zai kashe duk wani wanda ya tsere wa takobin Yehu.
And it will come about that the man who gets away safe from the sword of Hazael, Jehu will put to death; and whoever gets away safe from the sword of Jehu, Elisha will put to death.
18 Duk da haka zan bar mutane dubu bakwai na Isra’ila waɗanda ba su rusuna da gwiwansu wa Ba’al ba, ba su kuma sumbace shi da bakinsu ba.”
But I will keep safe seven thousand in Israel, all those whose knees have not been bent to Baal, and whose mouths have given him no kisses.
19 Sai Iliya ya tafi daga can ya sami Elisha ɗan Shafat, yana noma da shanu goma sha biyu masu garman noma, shi kansa yana jan na goma sha biyun. Iliya ya tafi wurinsa ya jefa mayafinsa a kan Elisha.
So he went away from there and came across Elisha, the son of Shaphat, ploughing with twelve yoke of oxen, he himself walking with the twelfth; and Elijah went up to him and put his robe on him.
20 Sai Elisha ya bar shanun, ya ruga ya bi Iliya. Ya ce, “Bari in sumbace mahaifina da mahaifiyata, in yi musu bankwana, sa’an nan in zo in bi ka.” Iliya ya ce, “Koma! Me na yi maka?”
And letting the oxen be where they were, he came running after Elijah, and said, Only let me give a kiss to my father and mother, and then I will come after you. But he said to him, Go back again; for what have I done to you?
21 Sai Elisha ya bar shi, ya koma, ya ɗauki shanunsa ya yayyanka. Ya ƙone kayan garman noman don yă dafa naman, ya kuma ba wa mutane naman, suka kuwa ci. Sa’an nan ya tashi, ya bi Iliya, ya kuma zama mai hidimarsa.
And he went back, and took the oxen and put them to death, and cooking their flesh with the yokes of the oxen, he gave the people a feast. Then he got up and went after Elijah and became his servant.