< 1 Sarakuna 18 >

1 Bayan dogon lokaci, a cikin shekara ta uku, maganar Ubangiji ta zo wa Iliya, ta ce, “Tafi, ka gabatar da kanka ga Ahab, zan kuwa aika da ruwan sama a ƙasar.”
Plusieurs jours après il arriva que la parole de l'Eternel fut [adressée] à Elie, en la troisième année, en disant: Va, montre-toi à Achab, et je donnerai de la pluie sur la terre.
2 Saboda haka Iliya ya tafi ya gabatar da kansa ga Ahab. Yanzu dai yunwa ta tsananta a Samariya,
Elie donc s'en alla pour se montrer à Achab; or il y avait une grande famine dans la Samarie.
3 Ahab kuma ya aika a kawo Obadiya, sarkin fadansa (Obadiya dai cikakken mai gaskata da Ubangiji ne.
Et Achab avait appelé Abdias son maître d'hôtel, (or Abdias craignait fort l'Eternel;
4 Yayinda Yezebel tana kisan annabawan Ubangiji, Obadiya ya ɗauki annabawa ɗari ya ɓoye a kogwanni biyu, hamsin a kowanne, ya kuma tanada musu abinci da kuma ruwa.)
Car quand Izebel exterminait les Prophètes de l'Eternel, Abdias prit cent Prophètes, et les cacha, cinquante dans une caverne, et cinquante dans une autre, et les y nourrit de pain et d'eau.)
5 Ahab ya ce wa Obadiya, “Ka ratsa ƙasar zuwa dukan maɓulɓulai da fadamu. Mai yiwuwa ka sami ciyawa mu ba dawakai da alfadarai don su rayu, don kada mu kashe dabbobinmu.”
Et Achab avait dit à Abdias: Va par le pays vers toutes les fontaines d'eaux, et vers tous les torrents; peut-être que nous trouverons de l'herbe, et que nous sauverons la vie aux chevaux et aux mulets, et nous ne laisserons point dépeupler le pays de bêtes.
6 Saboda haka suka raba ƙasar da za su ratsa, Ahab zai tafi gefe ɗaya, Obadiya kuma yă bi gefe ɗaya.
Ils partagèrent donc entr'eux le pays, afin d'aller partout; Achab allait séparément par un chemin, et Abdias allait séparément par un autre chemin.
7 Yayinda Obadiya yana tafiya, sai Iliya ya sadu da shi. Obadiya ya gane shi, ya rusuna har ƙasa, ya ce, “Kai ne, shugabana, Iliya?”
Et comme Abdias était en chemin, voilà, Elie le rencontra, et il reconnut Elie, et s'inclinant sur son visage, il lui dit: N'es-tu pas mon Seigneur Elie?
8 Iliya ya amsa, ya ce, “I, je ka faɗa wa maigidanka cewa, ‘Iliya yana a nan.’”
Et [Elie] lui répondit: C'est moi-même; va, [et] dis à ton Seigneur, voici Elie.
9 Obadiya ya yi tambaya, “Me na yi da ba daidai ba, da kake miƙa bawanka ga Ahab don yă kashe?
Et Abdias dit: Quel crime ai-je fait, que tu livres ton serviteur entre les mains d'Achab pour me faire mourir?
10 Na rantse da Ubangiji Allahnka, babu al’umma ko masarauta da mai girma sarki bai aika a nemo ka ba. In suka ce ba ka can, sai yă sa mulkin ko al’ummar su rantse, cewa ai, ba su same ka ba.
L'Eternel ton Dieu est vivant, qu'il n'y a ni nation, ni Royaume, où mon Seigneur n'ait envoyé pour te chercher; et on a répondu; il n'y est point. Il a même fait jurer les Royaumes et les nations [pour découvrir] si l'on ne pourrait point te trouver.
11 Amma yanzu kana faɗa mini in tafi wurin mai girma in ce, ‘Iliya yana a nan.’
Et maintenant tu dis: Va, [et] dis à ton Seigneur, voici Elie.
12 Ban san inda Ruhun Ubangiji zai kai ka sa’ad da na bar ka ba. In na tafi na faɗa wa Ahab bai kuma same ka a nan ba, zai sa a kashe ni. Tuna fa, ni bawanka, na yi wa Ubangiji sujada tun ina saurayi.
Et il arrivera que quand je serai parti d'avec toi, l'Esprit de l'Eternel te transportera en quelque endroit que je ne saurai point, et je viendrai vers Achab pour lui déclarer [ce que tu m'as dit], et ne te trouvant point, il me tuera; or ton serviteur craint l'Eternel dès sa jeunesse.
13 Ranka yă daɗe, ashe, ba a faɗa maka abin da na yi lokacin da Yezebel ta karkashe annabawan Ubangiji ba? Yadda na ɓoye annabawa ɗari, na sa su hamsin-hamsin a kogwanni biyu, na yi ta ba su abinci da ruwa.
N'a-t-on point dit à mon Seigneur ce que je fis quand Izebel tuait les Prophètes de l'Eternel, comment j'en cachai cent, cinquante dans une caverne, et cinquante dans une autre, et les y nourris de pain et d'eau?
14 Yanzu fa, kana ce in tafi wurin mai girma sarki, in ce, ‘Iliya yana a nan.’ Ai, zai kashe ni!”
Et maintenant tu dis, va; [et] dis à ton Seigneur, voici Elie; car il me tuera.
15 Iliya ya ce, “Na rantse da Ubangiji Maɗaukaki, wanda nake bauta wa, tabbatacce zan gabatar da kaina ga Ahab a yau.”
Mais Elie lui répondit: L'Eternel des armées, devant lequel je me tiens, est vivant, que certainement je me montrerai aujourd'hui à Achab.
16 Saboda haka sai Obadiya ya tafi wurin Ahab ya faɗa masa, Ahab kuwa ya tafi wurin Iliya.
Abdias donc s'en alla pour rencontrer Achab, et il lui fit entendre le tout; puis Achab alla au devant d'Elie.
17 Sa’ad da Ahab ya ga Iliya, sai ya ce masa, “Kai ne wannan, kai mai tā-da-na-zaune-tsaye a Isra’ila?”
Et aussitôt qu'Achab eut vu Elie, il lui dit: N'es-tu pas celui qui trouble Israël?
18 Iliya ya amsa, ya ce, “Ban tā-da-na-zaune-tsaye a Isra’ila ba. Amma kai da iyalin mahaifinka, ku kuka tā-da-na-zaune-tsaye. Ka ƙyale umarnai Ubangiji, ka bi Ba’al.
Et [Elie] lui répondit: Je n'ai point troublé Israël; mais [c'est] toi et la maison de ton père [qui avez troublé Israël], en ce que vous avez abandonné les commandements de l'Eternel, et que vous avez marché après les Bahalins.
19 Yanzu ka tara mutane daga dukan Isra’ila su sadu da ni a kan Dutsen Karmel. Ka kuma kawo annabawa ɗari huɗu da hamsin na Ba’al, da kuma annabawa ɗari huɗu na Ashera, waɗanda suke ci a teburin Yezebel.”
Or maintenant envoie, et fais assembler vers moi tout Israël sur la montagne de Carmel, avec les quatre cent cinquante prophètes de Bahal, et les quatre cents prophètes des bocages qui mangent à la table d'Izebel.
20 Sai Ahab ya aika a duk fāɗin Isra’ila, ya kuma tattara annabawan a kan Dutsen Karmel.
Ainsi Achab envoya vers tous les enfants d'Israël, et il assembla ces prophètes-là sur la montagne de Carmel.
21 Iliya ya je gaban mutane ya ce, “Har yaushe za ku yi ta yawo tsakanin ra’ayoyi biyu? In Ubangiji ne Allah, ku bi shi; amma in Ba’al Allah ne, ku bi shi.” Mutane dai ba su ce uffam ba.
Puis Elie s'approcha de tout le peuple, et dit: Jusqu'à quand clocherez-vous des deux côtés? Si l'Eternel est Dieu, suivez-le; mais si Bahal [est Dieu], suivez-le. Et le peuple ne lui répondit pas un seul mot.
22 Sai Iliya ya ce musu, “Ni ne kaɗai annabin Ubangiji da ya rage, amma Ba’al yana da annabawa ɗari huɗu da hamsin.
Alors Elie dit au peuple: Je suis demeuré seul Prophète de l'Eternel; et les prophètes de Bahal [sont au nombre de] quatre cent cinquante.
23 Ku samo mana bijimai biyu. Bari su zaɓa ɗaya wa kansu, bari kuma su yanka shi kucu-kucu su sa a itace, sai dai, kada su sa wuta a kansa. Ni kuwa zan shirya ɗaya bijimin in sa a kan itace, ni ma, ba zan sa wuta a kansa ba.
Or qu'on nous donne deux veaux, qu'ils en choisissent l'un pour eux, qu'ils le coupent en pièces, et qu'ils le mettent sur du bois; mais qu'ils n'y mettent point de feu; et je préparerai l'autre veau, je le mettrai sur du bois, et je n'y mettrai point de feu.
24 Sa’an nan ku kira bisa sunan allahnku, ni kuwa zan kira bisa sunan Ubangiji. Duk allahn da ya amsa ta wurin wuta, shi ne Allah.” Sai dukan jama’a suka ce, “Abin nan da faɗa yana da kyau.”
Puis invoquez le nom de vos dieux, et moi j'invoquerai le Nom de l'Eternel; et que le Dieu qui aura exaucé par feu, soit [reconnu pour] Dieu. Et tout le peuple répondit et dit: C'est bien dit.
25 Iliya ya ce wa annabawan Ba’al, “Ku ku fara zaɓi bijimi ɗaya, ku shirya, da yake kuna da yawa. Ku kira a bisa sunan allahnku, amma kada ku ƙuna wuta.”
Et Elie dit aux Prophètes de Bahal: Choisissez un veau, et préparez-le les premiers; car vous êtes en plus grand nombre, et invoquez le nom de vos dieux; mais n'y mettez point de feu.
26 Sai suka ɗauki bijimin da aka ba su suka shirya shi. Sa’an nan suka kira bisa sunan Ba’al daga safe har tsakar rana. Suna ihu, “Ya Ba’al, ka amsa mana!” Amma babu wata amsa, babu wani da ya amsa. Suka yi ta rawa kewaye da bagaden da suka yi.
Ils prirent donc un veau qu'on leur donna, ils l'apprêtèrent, et ils invoquèrent le nom de Bahal depuis le matin jusqu'à midi, en disant: Bahal exauce-nous! Mais il n'y avait ni voix ni réponse, et ils sautaient par dessus l'autel qu'on avait fait.
27 Da tsakar rana, Iliya ya fara yin musu ba’a. Ya ce, “Ku yi ihu da ƙarfi, tabbatacce shi allah ne! Mai yiwuwa yana cikin zurfin tunani, ko dai aiki ya yi masa yawa, ko ya yi tafiya. Mai yiwuwa yana barci ne, dole a tashe shi.”
Et sur le midi Elie se moquait d'eux, et disait: Criez à haute voix, car il est dieu; mais il pense à quelque chose, ou il est après quelque affaire, ou il est en voyage; peut-être qu'il dort; et il s'éveillera.
28 Sai suka yi ta ihu da ƙarfi suna tsattsaga kansu da takuba da māsu, yadda al’adarsu take, sai da jininsu ya yi ta zuba.
Ils criaient donc à haute voix, et ils se faisaient des incisions avec des couteaux, et des lancettes; selon leur coutume, en sorte que le sang coulait sur eux.
29 Tsakar rana ta wuce, suka ci gaba da ƙoƙari, suna annabci har lokacin miƙa hadayar yamma ya yi. Amma babu wani da ya tanƙa, babu wani da ya amsa, babu wanda ya kula.
Et quand le midi fut passé, et qu'ils eurent fait les prophètes jusqu'au temps qu'on offre l'oblation, sans qu'il y eût ni voix, ni réponse, ni apparence aucune qu'on eût égard à ce qu'ils faisaient;
30 Sa’an nan Iliya ya ce wa dukan mutane, “Ku zo nan wurina.” Suka zo wurinsa, ya kuma shirya bagaden Ubangiji, da ya riga ya zama kufai.
Elie dit alors à tout le peuple: Approchez-vous de moi. Et tout le peuple s'approcha de lui, et il répara l'autel de l'Eternel, qui était démoli.
31 Iliya ya ɗauki duwatsu goma sha biyu, ɗaya don kowace kabila zuriyar Yaƙub, wanda maganar Ubangiji ta zo masa, cewa, “Sunanka zai zama Isra’ila.”
Puis Elie prit douze pierres, selon le nombre des Tribus des enfants de Jacob, auquel la parole de l'Eternel avait été adressée, en disant: Israël sera ton nom.
32 Da waɗannan duwatsun ya gina bagade cikin sunan Ubangiji, ya kuma haƙa wuriya kewaye da shi, isashe da zai ci garwa biyu na irin ƙwayar gyada.
Et il rebâtit de ces pierres l'autel au Nom de l'Eternel; puis il fit un conduit de la capacité de deux sats de semence à l'entour de l'autel.
33 Ya shirya itace, ya yayyanka bijimin kucu-kucu, ya shimfiɗa shi a itacen. Sa’an nan ya ce musu, “Ku cika manyan tuluna da ruwa, ku zuba a kan hadayar da kuma a kan itacen.” Suka zuba.
Il rangea le bois, il coupa le veau en pièces, et il le mit sur le bois.
34 Ya ce, “Ku sāke yin haka,” sai suka sāke yin haka. Ya umarta, “Ku yi haka sau na uku,” suka kuma yi haka sau na uku.
Puis il dit: Emplissez quatre cruches d'eau, et les versez sur l'holocauste, et sur le bois. Puis il leur dit: Faites-le encore pour la deuxième fois; et ils le firent pour la deuxième fois. De nouveau il leur dit: Faites-le encore pour la troisième fois; et ils le firent pour la troisième fois;
35 Ruwan ya gangara kewaye da bagaden har ma ya cika wuriyar.
De sorte que les eaux allaient à l'entour de l'autel; et il remplit même le conduit d'eau.
36 A lokacin hadaya, sai annabi Iliya ya zo gaba ya yi addu’a, ya ce, “Ya Ubangiji Allah na Ibrahim, na Isra’ila da kuma na Yaƙub, bari a sani a yau cewa kai Allah ne a cikin Isra’ila, a kuma san cewa ni bawanka ne, na kuma yi dukan waɗannan abubuwa bisa umarninka.
Et au temps qu'on offre l'oblation, Elie le Prophète s'approcha, et dit: Ô Eternel! Dieu d'Abraham, d'Isaac, et d'Israël! [fais] qu'on connaisse aujourd'hui que tu es Dieu en Israël, et que je suis ton serviteur, et que j'ai fait toutes ces choses, selon ta parole.
37 Ka amsa mini, ya Ubangiji, ka amsa mini, saboda waɗannan mutane su san cewa kai, ya Ubangiji, kai ne Allah, su kuma san cewa kana sāke juye zukatansu zuwa gare ka.”
Exauce-moi, ô Eternel! exauce-moi; et [fais] que ce peuple connaisse que tu es l'Eternel Dieu, et que c'est toi qui auras fait retourner leurs cœurs en arrière.
38 Sai wutar Ubangiji ya fāɗo, ya cinye hadayar, itacen, duwatsun da kuma ƙasar, ya lashe ruwan da yake cikin wuriyar.
Alors le feu de l'Eternel tomba, et consuma l'holocauste, le bois, les pierres, et la poudre, et huma toute l'eau qui était au conduit.
39 Sa’ad da mutane suka ga wannan, sai suka rusuna, suka sunkuyar da kai suka ce, “Ubangiji, shi ne Allah! Ubangiji, shi ne Allah!”
Et tout le peuple voyant cela, tomba sur son visage, et dit: C'est l'Eternel qui est Dieu; c'est l'Eternel qui est Dieu.
40 Sa’an nan Iliya ya umarce su, ya ce, “Ku kama annabawan Ba’al, kada ku bar waninsu yă tsere!” Suka kama su, Iliya kuwa ya sa aka gangara da su zuwa Kwarin Kishon, aka yayyanka su a can.
Et Elie leur dit: Saisissez les Prophètes de Bahal, [et] qu'il n'en échappe pas un. Ils les saisirent donc, et Elie les fit descendre au torrent de Kison, et les fit égorger là.
41 Sai Iliya ya ce wa Ahab, “Ka haura gida, ka ci, ka sha, gama ina jin motsin ruwan sama mai yawa.”
Puis Elie dit à Achab: Monte, mange, et bois; car il y a un son bruyant de pluie.
42 Sai Ahab ya ruga don yă ci, yă sha, amma Iliya ya hau kan ƙwanƙolin Karmel, ya rusuna ƙasa, ya sa fuska a tsakanin gwiwarsa.
Ainsi Achab monta pour manger et pour boire; et Elie monta au sommet du Carmel, et se penchant contre terre, il mit son visage entre ses genoux;
43 Ya ce wa bawansa, “Tafi ka dubi wajen teku.” Sai bawan ya haura ya duba. Ya ce, “Ba kome a can.” Sau bakwai Iliya ya ce, “Koma.”
Et il dit à son serviteur: Monte maintenant, [et] regarde vers la mer. Il monta donc, et regarda, et dit: Il n'y a rien. Et [Elie lui] dit: Retournes-y par sept fois.
44 Sau na bakwai, bawan ya ce, “Wani girgije ƙarami kamar hannun mutum yana tasowa daga teku.” Sai Iliya ya ce, “Je ka faɗa wa Ahab, ‘Shirya keken yaƙinka, ka gangara kafin ruwan sama yă tare ka.’”
A la septième fois, il dit: Voilà une petite nuée comme la paume de la main d'un homme, laquelle monte de la mer. Alors [Elie lui] dit: Monte, et dis à Achab: Attelle [ton chariot], et descends, de peur que la pluie ne te surprenne.
45 Ana cikin haka, sarari ya ƙara duhunta da girgije, iska ta taso, sai ruwan sama kamar da bakin kwarya ya sauko, Ahab kuwa ya hau zuwa Yezireyel.
Et il arriva que les cieux s'obscurcirent de tous côtés de nuées, [accompagnées] de vent, et il y eut une grande pluie; et Achab monta sur son chariot, et vint à Jizréhel.
46 Ikon Ubangiji ya sauko a kan Iliya, ya sha ɗamara, ya ruga a guje a gaban Ahab har zuwa Yezireyel.
Et la main de l'Eternel fut sur Elie, qui s'étant retroussé sur les reins, courut devant Achab, jusqu'à l'entrée de Jizréhel.

< 1 Sarakuna 18 >