< 1 Sarakuna 18 >
1 Bayan dogon lokaci, a cikin shekara ta uku, maganar Ubangiji ta zo wa Iliya, ta ce, “Tafi, ka gabatar da kanka ga Ahab, zan kuwa aika da ruwan sama a ƙasar.”
and to be day many and word LORD to be to(wards) Elijah in/on/with year [the] third to/for to say to go: went to see: see to(wards) Ahab and to give: give rain upon face: surface [the] land: country
2 Saboda haka Iliya ya tafi ya gabatar da kansa ga Ahab. Yanzu dai yunwa ta tsananta a Samariya,
and to go: went Elijah to/for to see: see to(wards) Ahab and [the] famine strong in/on/with Samaria
3 Ahab kuma ya aika a kawo Obadiya, sarkin fadansa (Obadiya dai cikakken mai gaskata da Ubangiji ne.
and to call: call to Ahab to(wards) Obadiah which upon [the] house: household and Obadiah to be afraid [obj] LORD much
4 Yayinda Yezebel tana kisan annabawan Ubangiji, Obadiya ya ɗauki annabawa ɗari ya ɓoye a kogwanni biyu, hamsin a kowanne, ya kuma tanada musu abinci da kuma ruwa.)
and to be in/on/with to cut: eliminate Jezebel [obj] prophet LORD and to take: take Obadiah hundred prophet and to hide them fifty man in/on/with cave and to sustain them food: bread and water
5 Ahab ya ce wa Obadiya, “Ka ratsa ƙasar zuwa dukan maɓulɓulai da fadamu. Mai yiwuwa ka sami ciyawa mu ba dawakai da alfadarai don su rayu, don kada mu kashe dabbobinmu.”
and to say Ahab to(wards) Obadiah to go: went in/on/with land: country/planet to(wards) all spring [the] water and to(wards) all [the] torrent: valley perhaps to find grass and to live horse and mule and not to cut: lack from [the] animal
6 Saboda haka suka raba ƙasar da za su ratsa, Ahab zai tafi gefe ɗaya, Obadiya kuma yă bi gefe ɗaya.
and to divide to/for them [obj] [the] land: country/planet to/for to pass in/on/with her Ahab to go: went in/on/with way: direction one to/for alone him and Obadiah to go: went in/on/with way: direction one to/for alone him
7 Yayinda Obadiya yana tafiya, sai Iliya ya sadu da shi. Obadiya ya gane shi, ya rusuna har ƙasa, ya ce, “Kai ne, shugabana, Iliya?”
and to be Obadiah in/on/with way: journey and behold Elijah to/for to encounter: meet him and to recognize him and to fall: fall upon face his and to say you(m. s.) this lord my Elijah
8 Iliya ya amsa, ya ce, “I, je ka faɗa wa maigidanka cewa, ‘Iliya yana a nan.’”
and to say to/for him I to go: went to say to/for lord your behold Elijah
9 Obadiya ya yi tambaya, “Me na yi da ba daidai ba, da kake miƙa bawanka ga Ahab don yă kashe?
and to say what? to sin for you(m. s.) to give: give [obj] servant/slave your in/on/with hand: power Ahab to/for to die me
10 Na rantse da Ubangiji Allahnka, babu al’umma ko masarauta da mai girma sarki bai aika a nemo ka ba. In suka ce ba ka can, sai yă sa mulkin ko al’ummar su rantse, cewa ai, ba su same ka ba.
alive LORD God your if: surely no there nation and kingdom which not to send: depart lord my there to/for to seek you and to say nothing and to swear [obj] [the] kingdom and [obj] [the] nation for not to find you
11 Amma yanzu kana faɗa mini in tafi wurin mai girma in ce, ‘Iliya yana a nan.’
and now you(m. s.) to say to go: went to say to/for lord your behold Elijah
12 Ban san inda Ruhun Ubangiji zai kai ka sa’ad da na bar ka ba. In na tafi na faɗa wa Ahab bai kuma same ka a nan ba, zai sa a kashe ni. Tuna fa, ni bawanka, na yi wa Ubangiji sujada tun ina saurayi.
and to be I to go: went from with you and spirit LORD to lift: bear you upon which not to know and to come (in): come to/for to tell to/for Ahab and not to find you and to kill me and servant/slave your afraid [obj] LORD from youth my
13 Ranka yă daɗe, ashe, ba a faɗa maka abin da na yi lokacin da Yezebel ta karkashe annabawan Ubangiji ba? Yadda na ɓoye annabawa ɗari, na sa su hamsin-hamsin a kogwanni biyu, na yi ta ba su abinci da ruwa.
not to tell to/for lord my [obj] which to make: do in/on/with to kill Jezebel [obj] prophet LORD and to hide from prophet LORD hundred man fifty fifty man in/on/with cave and to sustain them food: bread and water
14 Yanzu fa, kana ce in tafi wurin mai girma sarki, in ce, ‘Iliya yana a nan.’ Ai, zai kashe ni!”
and now you(m. s.) to say to go: went to say to/for lord your behold Elijah and to kill me
15 Iliya ya ce, “Na rantse da Ubangiji Maɗaukaki, wanda nake bauta wa, tabbatacce zan gabatar da kaina ga Ahab a yau.”
and to say Elijah alive LORD Hosts which to stand: stand to/for face: before his for [the] day to see: see to(wards) him
16 Saboda haka sai Obadiya ya tafi wurin Ahab ya faɗa masa, Ahab kuwa ya tafi wurin Iliya.
and to go: went Obadiah to/for to encounter: meet Ahab and to tell to/for him and to go: went Ahab to/for to encounter: meet Elijah
17 Sa’ad da Ahab ya ga Iliya, sai ya ce masa, “Kai ne wannan, kai mai tā-da-na-zaune-tsaye a Isra’ila?”
and to be like/as to see: see Ahab [obj] Elijah and to say Ahab to(wards) him you(m. s.) this to trouble Israel
18 Iliya ya amsa, ya ce, “Ban tā-da-na-zaune-tsaye a Isra’ila ba. Amma kai da iyalin mahaifinka, ku kuka tā-da-na-zaune-tsaye. Ka ƙyale umarnai Ubangiji, ka bi Ba’al.
and to say not to trouble [obj] Israel that if: except if: except you(m. s.) and house: household father your in/on/with to leave: forsake you [obj] commandment LORD and to go: follow after [the] Baal
19 Yanzu ka tara mutane daga dukan Isra’ila su sadu da ni a kan Dutsen Karmel. Ka kuma kawo annabawa ɗari huɗu da hamsin na Ba’al, da kuma annabawa ɗari huɗu na Ashera, waɗanda suke ci a teburin Yezebel.”
and now to send: depart to gather to(wards) me [obj] all Israel to(wards) mountain: mount [the] (Mount) Carmel and [obj] prophet [the] Baal four hundred and fifty and prophet [the] Asherah four hundred to eat table Jezebel
20 Sai Ahab ya aika a duk fāɗin Isra’ila, ya kuma tattara annabawan a kan Dutsen Karmel.
and to send: depart Ahab in/on/with all son: descendant/people Israel and to gather [obj] [the] prophet to(wards) mountain: mount [the] (Mount) Carmel
21 Iliya ya je gaban mutane ya ce, “Har yaushe za ku yi ta yawo tsakanin ra’ayoyi biyu? In Ubangiji ne Allah, ku bi shi; amma in Ba’al Allah ne, ku bi shi.” Mutane dai ba su ce uffam ba.
and to approach: approach Elijah to(wards) all [the] people and to say till how you(m. p.) to limp upon two [the] division if LORD [the] God to go: follow after him and if [the] Baal to go: follow after him and not to answer [the] people [obj] him word
22 Sai Iliya ya ce musu, “Ni ne kaɗai annabin Ubangiji da ya rage, amma Ba’al yana da annabawa ɗari huɗu da hamsin.
and to say Elijah to(wards) [the] people I to remain prophet to/for LORD to/for alone me and prophet [the] Baal four hundred and fifty man
23 Ku samo mana bijimai biyu. Bari su zaɓa ɗaya wa kansu, bari kuma su yanka shi kucu-kucu su sa a itace, sai dai, kada su sa wuta a kansa. Ni kuwa zan shirya ɗaya bijimin in sa a kan itace, ni ma, ba zan sa wuta a kansa ba.
and to give: give to/for us two bullock and to choose to/for them [the] bullock [the] one and to cut him and to set: put upon [the] tree: wood and fire not to set: put and I to make [obj] [the] bullock [the] one and to give: put upon [the] tree: wood and fire not to set: put
24 Sa’an nan ku kira bisa sunan allahnku, ni kuwa zan kira bisa sunan Ubangiji. Duk allahn da ya amsa ta wurin wuta, shi ne Allah.” Sai dukan jama’a suka ce, “Abin nan da faɗa yana da kyau.”
and to call: call to in/on/with name God your and I to call: call to in/on/with name LORD and to be [the] God which to answer in/on/with fire he/she/it [the] God and to answer all [the] people and to say pleasant [the] word: speaking
25 Iliya ya ce wa annabawan Ba’al, “Ku ku fara zaɓi bijimi ɗaya, ku shirya, da yake kuna da yawa. Ku kira a bisa sunan allahnku, amma kada ku ƙuna wuta.”
and to say Elijah to/for prophet [the] Baal to choose to/for you [the] bullock [the] one and to make first for you(m. p.) [the] many and to call: call to in/on/with name God your and fire not to set: put
26 Sai suka ɗauki bijimin da aka ba su suka shirya shi. Sa’an nan suka kira bisa sunan Ba’al daga safe har tsakar rana. Suna ihu, “Ya Ba’al, ka amsa mana!” Amma babu wata amsa, babu wani da ya amsa. Suka yi ta rawa kewaye da bagaden da suka yi.
and to take: take [obj] [the] bullock which to give: give to/for them and to make and to call: call to in/on/with name [the] Baal from [the] morning and till [the] midday to/for to say [the] Baal to answer us and nothing voice and nothing to answer and to limp upon [the] altar which to make
27 Da tsakar rana, Iliya ya fara yin musu ba’a. Ya ce, “Ku yi ihu da ƙarfi, tabbatacce shi allah ne! Mai yiwuwa yana cikin zurfin tunani, ko dai aiki ya yi masa yawa, ko ya yi tafiya. Mai yiwuwa yana barci ne, dole a tashe shi.”
and to be in/on/with midday and to mock in/on/with them Elijah and to say to call: call out in/on/with voice great: large for God he/she/it for complaint and for pursuing to/for him and for way: journey to/for him perhaps sleeping he/she/it and to awake
28 Sai suka yi ta ihu da ƙarfi suna tsattsaga kansu da takuba da māsu, yadda al’adarsu take, sai da jininsu ya yi ta zuba.
and to call: call out in/on/with voice great: large and to cut like/as justice: custom their in/on/with sword and in/on/with spear till to pour: pour blood upon them
29 Tsakar rana ta wuce, suka ci gaba da ƙoƙari, suna annabci har lokacin miƙa hadayar yamma ya yi. Amma babu wani da ya tanƙa, babu wani da ya amsa, babu wanda ya kula.
and to be like/as to pass [the] midday and to prophesy till to/for to ascend: offer up [the] offering and nothing voice and nothing to answer and nothing attentiveness
30 Sa’an nan Iliya ya ce wa dukan mutane, “Ku zo nan wurina.” Suka zo wurinsa, ya kuma shirya bagaden Ubangiji, da ya riga ya zama kufai.
and to say Elijah to/for all [the] people to approach: approach to(wards) me and to approach: approach all [the] people to(wards) him and to heal [obj] altar LORD [the] to overthrow
31 Iliya ya ɗauki duwatsu goma sha biyu, ɗaya don kowace kabila zuriyar Yaƙub, wanda maganar Ubangiji ta zo masa, cewa, “Sunanka zai zama Isra’ila.”
and to take: take Elijah two ten stone like/as number tribe son: descendant/people Jacob which to be word LORD to(wards) him to/for to say Israel to be name your
32 Da waɗannan duwatsun ya gina bagade cikin sunan Ubangiji, ya kuma haƙa wuriya kewaye da shi, isashe da zai ci garwa biyu na irin ƙwayar gyada.
and to build [obj] [the] stone altar in/on/with name LORD and to make conduit like/as house: container seah seed around to/for altar
33 Ya shirya itace, ya yayyanka bijimin kucu-kucu, ya shimfiɗa shi a itacen. Sa’an nan ya ce musu, “Ku cika manyan tuluna da ruwa, ku zuba a kan hadayar da kuma a kan itacen.” Suka zuba.
and to arrange [obj] [the] tree: wood and to cut [obj] [the] bullock and to set: put upon [the] tree: wood and to say to fill four jar water and to pour: pour upon [the] burnt offering and upon [the] tree: wood
34 Ya ce, “Ku sāke yin haka,” sai suka sāke yin haka. Ya umarta, “Ku yi haka sau na uku,” suka kuma yi haka sau na uku.
and to say to repeat and to repeat and to say to do three and to do three
35 Ruwan ya gangara kewaye da bagaden har ma ya cika wuriyar.
and to go: walk [the] water around to/for altar and also [obj] [the] conduit to fill water
36 A lokacin hadaya, sai annabi Iliya ya zo gaba ya yi addu’a, ya ce, “Ya Ubangiji Allah na Ibrahim, na Isra’ila da kuma na Yaƙub, bari a sani a yau cewa kai Allah ne a cikin Isra’ila, a kuma san cewa ni bawanka ne, na kuma yi dukan waɗannan abubuwa bisa umarninka.
and to be in/on/with to ascend: offer up [the] offering and to approach: approach Elijah [the] prophet and to say LORD God Abraham Isaac and Israel [the] day: today to know for you(m. s.) God in/on/with Israel and I servant/slave your (and in/on/with word your *Q(K)*) to make: do [obj] all [the] word [the] these
37 Ka amsa mini, ya Ubangiji, ka amsa mini, saboda waɗannan mutane su san cewa kai, ya Ubangiji, kai ne Allah, su kuma san cewa kana sāke juye zukatansu zuwa gare ka.”
to answer me LORD to answer me and to know [the] people [the] this for you(m. s.) LORD [the] God and you(m. s.) to turn: turn [obj] heart their backwards
38 Sai wutar Ubangiji ya fāɗo, ya cinye hadayar, itacen, duwatsun da kuma ƙasar, ya lashe ruwan da yake cikin wuriyar.
and to fall: fall fire LORD and to eat [obj] [the] burnt offering and [obj] [the] tree: wood and [obj] [the] stone and [obj] [the] dust and [obj] [the] water which in/on/with conduit to lick
39 Sa’ad da mutane suka ga wannan, sai suka rusuna, suka sunkuyar da kai suka ce, “Ubangiji, shi ne Allah! Ubangiji, shi ne Allah!”
and to see: see all [the] people and to fall: fall upon face their and to say LORD he/she/it [the] God LORD he/she/it [the] God
40 Sa’an nan Iliya ya umarce su, ya ce, “Ku kama annabawan Ba’al, kada ku bar waninsu yă tsere!” Suka kama su, Iliya kuwa ya sa aka gangara da su zuwa Kwarin Kishon, aka yayyanka su a can.
and to say Elijah to/for them to capture [obj] prophet [the] Baal man: anyone not to escape from them and to capture them and to go down them Elijah to(wards) torrent: valley Kishon and to slaughter them there
41 Sai Iliya ya ce wa Ahab, “Ka haura gida, ka ci, ka sha, gama ina jin motsin ruwan sama mai yawa.”
and to say Elijah to/for Ahab to ascend: rise to eat and to drink for voice: sound crowd [the] rain
42 Sai Ahab ya ruga don yă ci, yă sha, amma Iliya ya hau kan ƙwanƙolin Karmel, ya rusuna ƙasa, ya sa fuska a tsakanin gwiwarsa.
and to ascend: rise Ahab to/for to eat and to/for to drink and Elijah to ascend: rise to(wards) head: top [the] (Mount) Carmel and to bend (down) land: soil [to] and to set: put face his between (knee his *Q(K)*)
43 Ya ce wa bawansa, “Tafi ka dubi wajen teku.” Sai bawan ya haura ya duba. Ya ce, “Ba kome a can.” Sau bakwai Iliya ya ce, “Koma.”
and to say to(wards) youth his to ascend: rise please to look way: direction sea and to ascend: rise and to look and to say nothing anything and to say to return: again seven beat
44 Sau na bakwai, bawan ya ce, “Wani girgije ƙarami kamar hannun mutum yana tasowa daga teku.” Sai Iliya ya ce, “Je ka faɗa wa Ahab, ‘Shirya keken yaƙinka, ka gangara kafin ruwan sama yă tare ka.’”
and to be in/on/with seventh and to say behold cloud small like/as palm man to ascend: rise from sea and to say to ascend: rise to say to(wards) Ahab to bind and to go down and not to restrain you [the] rain
45 Ana cikin haka, sarari ya ƙara duhunta da girgije, iska ta taso, sai ruwan sama kamar da bakin kwarya ya sauko, Ahab kuwa ya hau zuwa Yezireyel.
and to be till thus and till thus and [the] heaven be dark cloud and spirit: breath and to be rain great: large and to ride Ahab and to go: went Jezreel [to]
46 Ikon Ubangiji ya sauko a kan Iliya, ya sha ɗamara, ya ruga a guje a gaban Ahab har zuwa Yezireyel.
and hand: power LORD to be to(wards) Elijah and to gird loin his and to run: run to/for face: before Ahab till to come (in): towards you Jezreel [to]