< 1 Sarakuna 18 >

1 Bayan dogon lokaci, a cikin shekara ta uku, maganar Ubangiji ta zo wa Iliya, ta ce, “Tafi, ka gabatar da kanka ga Ahab, zan kuwa aika da ruwan sama a ƙasar.”
And the days are many, and the word of YHWH has been to Elijah in the third year, saying, “Go, appear to Ahab, and I give rain on the face of the ground”;
2 Saboda haka Iliya ya tafi ya gabatar da kansa ga Ahab. Yanzu dai yunwa ta tsananta a Samariya,
and Elijah goes to appear to Ahab. And the famine is severe in Samaria,
3 Ahab kuma ya aika a kawo Obadiya, sarkin fadansa (Obadiya dai cikakken mai gaskata da Ubangiji ne.
and Ahab calls to Obadiah, who [is] over the house—and Obadiah has been fearing YHWH greatly,
4 Yayinda Yezebel tana kisan annabawan Ubangiji, Obadiya ya ɗauki annabawa ɗari ya ɓoye a kogwanni biyu, hamsin a kowanne, ya kuma tanada musu abinci da kuma ruwa.)
and it comes to pass, in Jezebel’s cutting off the prophets of YHWH, that Obadiah takes one hundred prophets, and hides them, fifty men in a cave, and has sustained them with bread and water—
5 Ahab ya ce wa Obadiya, “Ka ratsa ƙasar zuwa dukan maɓulɓulai da fadamu. Mai yiwuwa ka sami ciyawa mu ba dawakai da alfadarai don su rayu, don kada mu kashe dabbobinmu.”
and Ahab says to Obadiah, “Go through the land, to all fountains of waters, and to all the brooks, perhaps we find hay, and keep alive horse and mule, and do not cut off any of the livestock.”
6 Saboda haka suka raba ƙasar da za su ratsa, Ahab zai tafi gefe ɗaya, Obadiya kuma yă bi gefe ɗaya.
And they apportion the land to themselves, to pass over into it; Ahab has gone in one way by himself, and Obadiah has gone in another way by himself;
7 Yayinda Obadiya yana tafiya, sai Iliya ya sadu da shi. Obadiya ya gane shi, ya rusuna har ƙasa, ya ce, “Kai ne, shugabana, Iliya?”
and Obadiah [is] in the way, and behold, Elijah [is there] to meet him; and he discerns him, and falls on his face and says, “Are you he—my lord Elijah?”
8 Iliya ya amsa, ya ce, “I, je ka faɗa wa maigidanka cewa, ‘Iliya yana a nan.’”
And he says to him, “I [am]; go, say to your lord, Behold, Elijah.”
9 Obadiya ya yi tambaya, “Me na yi da ba daidai ba, da kake miƙa bawanka ga Ahab don yă kashe?
And he says, “What have I sinned, that you are giving your servant into the hand of Ahab—to put me to death?
10 Na rantse da Ubangiji Allahnka, babu al’umma ko masarauta da mai girma sarki bai aika a nemo ka ba. In suka ce ba ka can, sai yă sa mulkin ko al’ummar su rantse, cewa ai, ba su same ka ba.
Your God YHWH lives, if there is a nation and kingdom to where my lord has not sent to seek [for] you; and they said, He is not, then he caused the kingdom and the nation to swear, that it does not find you;
11 Amma yanzu kana faɗa mini in tafi wurin mai girma in ce, ‘Iliya yana a nan.’
and now, you are saying, Go, say to your lord, Behold, Elijah;
12 Ban san inda Ruhun Ubangiji zai kai ka sa’ad da na bar ka ba. In na tafi na faɗa wa Ahab bai kuma same ka a nan ba, zai sa a kashe ni. Tuna fa, ni bawanka, na yi wa Ubangiji sujada tun ina saurayi.
and it has been, I go from you, and the Spirit of YHWH lifts you up to where I do not know, and I have come to declare to Ahab, and he does not find you, and he has slain me; and your servant is fearing YHWH from my youth.
13 Ranka yă daɗe, ashe, ba a faɗa maka abin da na yi lokacin da Yezebel ta karkashe annabawan Ubangiji ba? Yadda na ɓoye annabawa ɗari, na sa su hamsin-hamsin a kogwanni biyu, na yi ta ba su abinci da ruwa.
Has it not been declared to my lord that which I have done in Jezebel’s slaying the prophets of YHWH, that I hide one hundred men of the prophets of YHWH, fifty by fifty in a cave, and sustained them with bread and water?
14 Yanzu fa, kana ce in tafi wurin mai girma sarki, in ce, ‘Iliya yana a nan.’ Ai, zai kashe ni!”
And now you are saying, Go, say to my lord, Behold, Elijah—and he has slain me!”
15 Iliya ya ce, “Na rantse da Ubangiji Maɗaukaki, wanda nake bauta wa, tabbatacce zan gabatar da kaina ga Ahab a yau.”
And Elijah says, “YHWH of Hosts lives, before whom I have stood, surely I appear to him today.”
16 Saboda haka sai Obadiya ya tafi wurin Ahab ya faɗa masa, Ahab kuwa ya tafi wurin Iliya.
Obadiah goes to meet Ahab, and declares [it] to him, and Ahab goes to meet Elijah.
17 Sa’ad da Ahab ya ga Iliya, sai ya ce masa, “Kai ne wannan, kai mai tā-da-na-zaune-tsaye a Isra’ila?”
[And it] comes to pass at Ahab’s seeing Elijah that Ahab says to him, “Are you he—the troubler of Israel?”
18 Iliya ya amsa, ya ce, “Ban tā-da-na-zaune-tsaye a Isra’ila ba. Amma kai da iyalin mahaifinka, ku kuka tā-da-na-zaune-tsaye. Ka ƙyale umarnai Ubangiji, ka bi Ba’al.
And he says, “I have not troubled Israel, but you and the house of your father, in your forsaking the commands of YHWH, and you go after the Ba‘alim;
19 Yanzu ka tara mutane daga dukan Isra’ila su sadu da ni a kan Dutsen Karmel. Ka kuma kawo annabawa ɗari huɗu da hamsin na Ba’al, da kuma annabawa ɗari huɗu na Ashera, waɗanda suke ci a teburin Yezebel.”
and now, send, gather all Israel to me, to the Mount of Carmel, and the four hundred and fifty prophets of Ba‘al, and the four hundred prophets of Asherah who are eating at the table of Jezebel.”
20 Sai Ahab ya aika a duk fāɗin Isra’ila, ya kuma tattara annabawan a kan Dutsen Karmel.
And Ahab sends among all the sons of Israel, and gathers the prophets to the Mount of Carmel;
21 Iliya ya je gaban mutane ya ce, “Har yaushe za ku yi ta yawo tsakanin ra’ayoyi biyu? In Ubangiji ne Allah, ku bi shi; amma in Ba’al Allah ne, ku bi shi.” Mutane dai ba su ce uffam ba.
and Elijah comes near to all the people and says, “Until when are you leaping on the two branches? If YHWH [is] God, go after Him; and if Ba‘al, go after him”; and the people have not answered him a word.
22 Sai Iliya ya ce musu, “Ni ne kaɗai annabin Ubangiji da ya rage, amma Ba’al yana da annabawa ɗari huɗu da hamsin.
And Elijah says to the people, “I have been left, by myself, a prophet of YHWH; and the prophets of Ba‘al [are] four hundred and fifty men;
23 Ku samo mana bijimai biyu. Bari su zaɓa ɗaya wa kansu, bari kuma su yanka shi kucu-kucu su sa a itace, sai dai, kada su sa wuta a kansa. Ni kuwa zan shirya ɗaya bijimin in sa a kan itace, ni ma, ba zan sa wuta a kansa ba.
and let them give two bullocks to us, and they choose one bullock for themselves, and cut it in pieces, and place [it] on the wood, and place no fire; and I prepare the other bullock, and have put [it] on the wood, and I do not place fire—
24 Sa’an nan ku kira bisa sunan allahnku, ni kuwa zan kira bisa sunan Ubangiji. Duk allahn da ya amsa ta wurin wuta, shi ne Allah.” Sai dukan jama’a suka ce, “Abin nan da faɗa yana da kyau.”
and you have called in the name of your god, and I call in the Name of YHWH, and it has been, the god who answers by fire—He [is] the God.” And all the people answer and say, “The word [is] good.”
25 Iliya ya ce wa annabawan Ba’al, “Ku ku fara zaɓi bijimi ɗaya, ku shirya, da yake kuna da yawa. Ku kira a bisa sunan allahnku, amma kada ku ƙuna wuta.”
And Elijah says to the prophets of Ba‘al, “Choose one bullock for yourselves, and prepare [it] first, for you [are] the multitude, and call in the name of your god, and place no fire.”
26 Sai suka ɗauki bijimin da aka ba su suka shirya shi. Sa’an nan suka kira bisa sunan Ba’al daga safe har tsakar rana. Suna ihu, “Ya Ba’al, ka amsa mana!” Amma babu wata amsa, babu wani da ya amsa. Suka yi ta rawa kewaye da bagaden da suka yi.
And they take the bullock that [one] gave to them, and prepare [it], and call in the name of Ba‘al from the morning even until the noon, saying, “O Ba‘al, answer us!” And there is no voice, and there is none answering; and they leap on the altar that one had made.
27 Da tsakar rana, Iliya ya fara yin musu ba’a. Ya ce, “Ku yi ihu da ƙarfi, tabbatacce shi allah ne! Mai yiwuwa yana cikin zurfin tunani, ko dai aiki ya yi masa yawa, ko ya yi tafiya. Mai yiwuwa yana barci ne, dole a tashe shi.”
And it comes to pass, at noon, that Elijah mocks at them and says, “Call with a loud voice, for he [is] a god, for he is meditating, or pursuing, or on a journey; it may be he is asleep, and awakes.”
28 Sai suka yi ta ihu da ƙarfi suna tsattsaga kansu da takuba da māsu, yadda al’adarsu take, sai da jininsu ya yi ta zuba.
And they call with a loud voice, and cut themselves, according to their ordinance, with swords and with spears, until a flowing of blood [is] on them;
29 Tsakar rana ta wuce, suka ci gaba da ƙoƙari, suna annabci har lokacin miƙa hadayar yamma ya yi. Amma babu wani da ya tanƙa, babu wani da ya amsa, babu wanda ya kula.
and it comes to pass, at the passing by of the noon, that they feign themselves prophets until the going up of the present, and there is no voice, and there is none answering, and there is none attending.
30 Sa’an nan Iliya ya ce wa dukan mutane, “Ku zo nan wurina.” Suka zo wurinsa, ya kuma shirya bagaden Ubangiji, da ya riga ya zama kufai.
And Elijah says to all the people, “Come near to me”; and all the people come near to him, and he repairs the altar of YHWH that is broken down;
31 Iliya ya ɗauki duwatsu goma sha biyu, ɗaya don kowace kabila zuriyar Yaƙub, wanda maganar Ubangiji ta zo masa, cewa, “Sunanka zai zama Isra’ila.”
and Elijah takes twelve stones, according to the number of the tribes of the sons of Jacob, to whom the word of YHWH was, saying, “Israel is your name”;
32 Da waɗannan duwatsun ya gina bagade cikin sunan Ubangiji, ya kuma haƙa wuriya kewaye da shi, isashe da zai ci garwa biyu na irin ƙwayar gyada.
and he builds an altar with the stones, in the Name of YHWH, and makes a trench, as about the space of two measures of seed, around the altar.
33 Ya shirya itace, ya yayyanka bijimin kucu-kucu, ya shimfiɗa shi a itacen. Sa’an nan ya ce musu, “Ku cika manyan tuluna da ruwa, ku zuba a kan hadayar da kuma a kan itacen.” Suka zuba.
And he arranges the wood, and cuts the bullock in pieces, and places [it] on the wood, and says, “Fill four pitchers of water, and pour [them] on the burnt-offering, and on the wood”;
34 Ya ce, “Ku sāke yin haka,” sai suka sāke yin haka. Ya umarta, “Ku yi haka sau na uku,” suka kuma yi haka sau na uku.
and he says, “Do [it] a second time”; and they do [it] a second time; and he says, “Do [it] a third time”; and they do [it] a third time;
35 Ruwan ya gangara kewaye da bagaden har ma ya cika wuriyar.
and the water goes around the altar, and he has also filled the trench with water.
36 A lokacin hadaya, sai annabi Iliya ya zo gaba ya yi addu’a, ya ce, “Ya Ubangiji Allah na Ibrahim, na Isra’ila da kuma na Yaƙub, bari a sani a yau cewa kai Allah ne a cikin Isra’ila, a kuma san cewa ni bawanka ne, na kuma yi dukan waɗannan abubuwa bisa umarninka.
And it comes to pass, at the going up of the [evening] present, that Elijah the prophet comes near and says, “YHWH, God of Abraham, Isaac, and Israel, let it be known today that You [are] God in Israel, and that I, Your servant, have done the whole of these things by Your word;
37 Ka amsa mini, ya Ubangiji, ka amsa mini, saboda waɗannan mutane su san cewa kai, ya Ubangiji, kai ne Allah, su kuma san cewa kana sāke juye zukatansu zuwa gare ka.”
answer me, O YHWH, answer me, and this people [then] knows that You [are] YHWH God; and You have turned their heart backward.”
38 Sai wutar Ubangiji ya fāɗo, ya cinye hadayar, itacen, duwatsun da kuma ƙasar, ya lashe ruwan da yake cikin wuriyar.
And a fire falls [from] YHWH, and consumes the burnt-offering, and the wood, and the stones, and the dust, and it has licked up the water that [is] in the trench.
39 Sa’ad da mutane suka ga wannan, sai suka rusuna, suka sunkuyar da kai suka ce, “Ubangiji, shi ne Allah! Ubangiji, shi ne Allah!”
And all the people see, and fall on their faces, and say, “YHWH, He [is] the God! YHWH, He [is] the God!”
40 Sa’an nan Iliya ya umarce su, ya ce, “Ku kama annabawan Ba’al, kada ku bar waninsu yă tsere!” Suka kama su, Iliya kuwa ya sa aka gangara da su zuwa Kwarin Kishon, aka yayyanka su a can.
And Elijah says to them, “Catch the prophets of Ba‘al; do not let a man escape from them”; and they catch them, and Elijah brings them down to the Brook of Kishon, and slaughters them there.
41 Sai Iliya ya ce wa Ahab, “Ka haura gida, ka ci, ka sha, gama ina jin motsin ruwan sama mai yawa.”
And Elijah says to Ahab, “Go up, eat and drink, because of the sound of the noise of the shower.”
42 Sai Ahab ya ruga don yă ci, yă sha, amma Iliya ya hau kan ƙwanƙolin Karmel, ya rusuna ƙasa, ya sa fuska a tsakanin gwiwarsa.
And Ahab goes up to eat, and to drink, and Elijah has gone up to the top of Carmel, and he stretches himself out on the earth, and he places his face between his knees,
43 Ya ce wa bawansa, “Tafi ka dubi wajen teku.” Sai bawan ya haura ya duba. Ya ce, “Ba kome a can.” Sau bakwai Iliya ya ce, “Koma.”
and says to his young man, “Now go up, look attentively [toward] the way of the sea”; and he goes up and looks attentively, and says, “There is nothing”; and he says, “Turn back,” seven times.
44 Sau na bakwai, bawan ya ce, “Wani girgije ƙarami kamar hannun mutum yana tasowa daga teku.” Sai Iliya ya ce, “Je ka faɗa wa Ahab, ‘Shirya keken yaƙinka, ka gangara kafin ruwan sama yă tare ka.’”
And it comes to pass, at the seventh, that he says, “Behold, a little thickness as the palm of a man is coming up out of the sea.” And he says, “Go up, say to Ahab, Bind and go down, and the shower does not restrain you.”
45 Ana cikin haka, sarari ya ƙara duhunta da girgije, iska ta taso, sai ruwan sama kamar da bakin kwarya ya sauko, Ahab kuwa ya hau zuwa Yezireyel.
And it comes to pass, in the meantime, that the heavens have become black—thick clouds and wind—and the shower is great; and Ahab rides, and goes to Jezreel,
46 Ikon Ubangiji ya sauko a kan Iliya, ya sha ɗamara, ya ruga a guje a gaban Ahab har zuwa Yezireyel.
and the hand of YHWH has been on Elijah, and he girds up his loins, and runs before Ahab, until your entering Jezreel.

< 1 Sarakuna 18 >