< 1 Sarakuna 17 >
1 To, Iliya mutumin Tishbe, daga Tishbe a Gileyad, ya ce wa Ahab, “Muddin Ubangiji, Allah na Isra’ila wanda nake bauta wa yana a raye, ba za a yi raɓa ko ruwan sama a’yan shekaru masu zuwa ba, sai ko na faɗa haka.”
Un Elija no Tizbes, no Gileādas iedzīvotājiem, sacīja uz Ahabu: tik tiešām kā Tas Kungs, Israēla Dievs, dzīvo, kā priekšā es stāvu, šinīs gados nebūs nedz rasas nedz lietus, kā vien, kad es to sacīšu.
2 Sai maganar Ubangiji ta zo wa Iliya, ta ce,
Un Tā Kunga vārds uz to notika tā:
3 “Ka bar nan, ka nufi wajajen gabas, ka ɓuya a Rafin Kerit, gabas da Urdun.
Ej no šejienes un griezies pret rītiem un paslēpies pie Krites upes, kas tek pret Jardāni.
4 Za ka sha daga rafin, zan kuma umarci hankaki su ciyar da kai a can.”
Un tur tu vari dzert no tās upes, un Es kraukļiem esmu pavēlējis, ka tiem tevi tur būs uzturēt.
5 Saboda haka sai Iliya ya yi abin da Ubangiji ya faɗa masa. Ya tafi Rafin Kerit, gabas da Urdun, ya zauna a can.
Un viņš nogāja un darīja pēc Tā Kunga vārda, un nogāja un palika pie Krites upes, kas tek pret Jardāni.
6 Hankaki suka riƙa kawo masa abinci da nama, safe da yamma, ya kuma sha daga rafin.
Un kraukļi viņam atnesa maizi un gaļu rītos un maizi un gaļu vakaros, un viņš dzēra no tās upes.
7 Ana nan sai rafin ya bushe saboda ba a yi ruwan sama a ƙasar ba.
Bet pēc kāda laika tā upe izsīka, jo lietus tai zemē nebija.
8 Sai maganar Ubangiji ta zo wa Iliya cewa,
Tad Tā Kunga vārds uz viņu notika tā:
9 “Je ka, nan take, zuwa Zarefat na Sidon, ka zauna a can. Na umarci wata gwauruwa a can tă ciyar da kai.”
Celies un ej uz Sareptu, kas pie Sidones pieder, un paliec turpat; redzi, Es tur esmu pavēlējis vienai atraitnei, tevi uzturēt.
10 Saboda haka sai ya tafi Zarefat. Sa’ad da ya isa ƙofar gari, sai ga wata gwauruwa tana tattara’yan itace. Sai ya kira ta, ya ce, “Ki kawo mini ɗan ruwa a tulu don in sha.”
Tad viņš cēlās un gāja uz Sareptu Un kad viņš nonāca pie pilsētas vārtiem, redzi, tad tur viena atraitne lasīja malku. Un viņš tai sauca un sacīja: atnes man traukā kādu ūdens malciņu, ko dzert.
11 Da ta kama hanya za tă tafi tă kawo, sai ya sāke kiranta ya ce, “Ina roƙonki, ki kuma kawo mini ɗan abinci.”
Un tā gāja to atnest. Un viņš tai sauca un sacīja: atnes man arī kumosu maizes savā rokā.
12 Sai ta ce masa, “Na rantse da Ubangiji Allahnka, ba ni da wani abinci, sai dai ɗan gari hannu guda a tulu, da kuma ɗan mai a kwalaba. Ina tattara’yan itacen nan ne don in kai gida in yi abinci wa kaina da ɗana, don mu ci, mu mutu.”
Bet tā sacīja: tik tiešām kā Tas Kungs, tavs Dievs, dzīvo, man nekā cepta nav, un tik vien ir sauja miltu tīnē un maķenīt eļļas krūzē, un redzi, es esmu salasījusi kādu pāri malkas gabaliņu, un nu es iešu un sev un savam dēlam ko pataisīšu, ka ēdam un mirstam.
13 Iliya ya ce mata, “Kada ki ji tsoro. Ki tafi gida, ki yi yadda kika ce. Amma da farko ki yi mini’yar wainar burodi daga abin da kike da shi ki kawo mini, sa’an nan ki yi wani abu wa kanki da kuma ɗanki.
Un Elija uz to sacīja: nebīsties, ej, pataisi to, kā tu sacījusi, bet man taisi no tiem papriekš mazu rausi un iznes man to ārā, un pēc tu arī varēsi taisīt sev un savam dēlam.
14 Gama abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila ya ce, ‘Tulun garin ba zai ƙare ba, kwalabar man kuma ba zai bushe ba sai ranar da Ubangiji ya bayar da ruwan sama a ƙasar.’”
Jo tā saka Tas Kungs, Israēla Dievs: milti tīnē neies galā un krūzē eļļas netrūks līdz tai dienai, kad Tas Kungs dos lietu virs zemes.
15 Sai ta tafi, ta yi yadda Iliya ya faɗa mata. Saboda haka aka kasance da abinci kowace rana wa Iliya da kuma don macen da iyalinta.
Un tā nogāja un darīja pēc Elijas vārda; tā viņa ēda un viņš un viņas nams labu laiku;
16 Gama tulun garin bai ƙare ba, kwalabar man kuma bai bushe ba, kamar yadda Ubangiji ya faɗa wa Iliya.
Milti tīnē negāja galā un krūzē eļļas netrūka pēc Tā Kunga vārda, ko viņš caur Eliju bija runājis.
17 Ana nan sai ɗan matan, wato, gwauruwan nan ya fara ciwo. Ciwon ya ƙara muni, daga ƙarshe sai ya daina numfashi.
Un pēc tam notikās, ka šīs sievas, tās nama mātes, dēls palika slims un viņa slimība palika ļoti grūta, kamēr viņam dvašas vairs nebija.
18 Sai ta ce wa Iliya, “Mutumin Allah, yaya haka? Ka zo ne domin ka nuna wa Allah zunubaina, ka kuma jawo mutuwar ɗana?”
Un tā sacīja uz Eliju: kas man ar tevi, tu Dieva vīrs? Tu pie manis esi atnācis, lai mani grēki top pieminēti un mans dēls mirst.
19 Iliya ya ce, “Ki miƙa mini ɗanki.” Sai ya ɗauke shi daga hannuwanta, ya kai shi ɗakin sama inda yake zama, ya kwantar da shi a gadonsa.
Un viņš uz to sacīja: dod man šurp savu dēlu. Un viņš to ņēma no viņas klēpja un to uznesa augšistabā, kur viņš mita, un to lika uz savu gultu.
20 Sa’an nan ya yi kuka ga Ubangiji ya ce, “Ya Ubangiji Allahna, don me ka kawo wannan masifa a kan gwauruwan nan? Kai ka ce in zauna tare da ita, ga shi yanzu ɗanta ya mutu.”
Un viņš piesauca To Kungu un sacīja: Kungs, mans Dievs! Vai tad Tu šai atraitnei, pie kuras es piemājoju, tik ļaunu esi darījis un nonāvējis viņas bērnu?
21 Sai ya kwanta, ya miƙe kansa a kan yaron sau uku, ya kuma yi kuka ga Ubangiji ya ce, “Ya Ubangiji Allahna, ka mai da ran yaron nan!”
Un viņš stiepās pār to bērnu trīs reizes un piesauca To Kungu un sacīja: Kungs, mans Dievs! Lai jel šā bērna dvēsele atkal nāk iekš viņa!
22 Ubangiji kuwa ya ji kukan Iliya, sai ran yaron ya dawo masa, ya kuma rayu.
Un Tas Kungs klausīja Elijas balsi, un tā bērna dvēsele atkal nāca iekš viņa, un tas atdzīvojās.
23 Iliya ya ɗauki yaron ya sauko da shi daga ɗakin sama zuwa cikin gida. Ya ba da shi ga mahaifiyarsa, ya ce, “Duba, ɗanki yana da rai!”
Un Elija ņēma to bērnu un to nonesa no augšistabas namā un to deva viņa mātei; un Elija uz to sacīja: redzi še, tavs dēls dzīvs.
24 Sai matar ta ce wa Iliya, “Yanzu na san cewa kai mutumin Allah ne, Ubangiji kuma yana magana ta wurinka.”
Tad tā sieva sacīja uz Eliju: nu es zinu, ka tu esi Dieva vīrs, un Tā Kunga vārds tavā mutē ir patiesība.