< 1 Sarakuna 17 >

1 To, Iliya mutumin Tishbe, daga Tishbe a Gileyad, ya ce wa Ahab, “Muddin Ubangiji, Allah na Isra’ila wanda nake bauta wa yana a raye, ba za a yi raɓa ko ruwan sama a’yan shekaru masu zuwa ba, sai ko na faɗa haka.”
Et Elie, le Thesbite, un des habitants de Galaad, dit à Achab: Il vit, le Seigneur Dieu d’Israël, en la présence duquel je suis! il n’y aura pendant ces années-ci ni rosée ni pluie que selon les paroles de ma bouche.
2 Sai maganar Ubangiji ta zo wa Iliya, ta ce,
Et la parole du Seigneur fut adressée à Elie, disant:
3 “Ka bar nan, ka nufi wajajen gabas, ka ɓuya a Rafin Kerit, gabas da Urdun.
Retire-toi d’ici; va contre l’orient, et cache-toi près du torrent de Carith, qui est contre le Jourdain;
4 Za ka sha daga rafin, zan kuma umarci hankaki su ciyar da kai a can.”
Et là tu boiras au torrent; et j’ai ordonné aux corbeaux qu’ils te nourrissent là.
5 Saboda haka sai Iliya ya yi abin da Ubangiji ya faɗa masa. Ya tafi Rafin Kerit, gabas da Urdun, ya zauna a can.
Elie s’en alla donc, et fit selon la parole du Seigneur, et lorsqu’il s’en fut allé, il s’assit près du torrent de Carith, qui est contre le Jourdain.
6 Hankaki suka riƙa kawo masa abinci da nama, safe da yamma, ya kuma sha daga rafin.
Et les corbeaux lui apportaient du pain et de la chair le matin, également du pain et de la chair le soir, et il buvait au torrent.
7 Ana nan sai rafin ya bushe saboda ba a yi ruwan sama a ƙasar ba.
Mais après quelques jours le torrent se sécha; car il n’avait pas plu sur la terre.
8 Sai maganar Ubangiji ta zo wa Iliya cewa,
La parole du Seigneur lui fut donc adressée, disant:
9 “Je ka, nan take, zuwa Zarefat na Sidon, ka zauna a can. Na umarci wata gwauruwa a can tă ciyar da kai.”
Lève-toi, et va à Sarephta, ville des Sidoniens, et tu demeureras là; car j’ai ordonné là à une femme veuve qu’elle te nourrisse.
10 Saboda haka sai ya tafi Zarefat. Sa’ad da ya isa ƙofar gari, sai ga wata gwauruwa tana tattara’yan itace. Sai ya kira ta, ya ce, “Ki kawo mini ɗan ruwa a tulu don in sha.”
Il se leva et s’en alla à Sarephta. Et lorsqu’il fut venu à la porte de la ville, il aperçut une femme veuve qui ramassait du bois; et il l’appela, et lui dit: Donne-moi un peu d’eau dans le vase, afin que je boive.
11 Da ta kama hanya za tă tafi tă kawo, sai ya sāke kiranta ya ce, “Ina roƙonki, ki kuma kawo mini ɗan abinci.”
Et lorsque celle-ci allait pour en apporter, il cria derrière elle, disant: Apporte-moi aussi, je te prie, un peu de pain en ta main.
12 Sai ta ce masa, “Na rantse da Ubangiji Allahnka, ba ni da wani abinci, sai dai ɗan gari hannu guda a tulu, da kuma ɗan mai a kwalaba. Ina tattara’yan itacen nan ne don in kai gida in yi abinci wa kaina da ɗana, don mu ci, mu mutu.”
Elle lui répondit: Le Seigneur ton Dieu vit! je n’ai point de pain, mais seulement dans la cruche autant de farine qu’une main peut en contenir, et un peu d’huile dans le flacon. Voilà que je ramasse deux morceaux de bois, pour que j’entre et que je fasse du pain pour moi et pour mon fils, afin que nous mangions, et que nous mourions.
13 Iliya ya ce mata, “Kada ki ji tsoro. Ki tafi gida, ki yi yadda kika ce. Amma da farko ki yi mini’yar wainar burodi daga abin da kike da shi ki kawo mini, sa’an nan ki yi wani abu wa kanki da kuma ɗanki.
Élie lui dit: Ne crains point; mais va, et fais comme tu as dit; cependant fais pour moi auparavant, avec ce peu de farine même, un petit pain cuit sous la cendre, et apporte-le-moi; mais pour toi et pour ton fils, tu en feras ensuite.
14 Gama abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila ya ce, ‘Tulun garin ba zai ƙare ba, kwalabar man kuma ba zai bushe ba sai ranar da Ubangiji ya bayar da ruwan sama a ƙasar.’”
Car voici ce que dit le Seigneur Dieu d’Israël: La cruche de la farine ne manquera point, et le flacon de l’huile ne diminuera point, jusqu’au jour où le Seigneur doit donner de la pluie sur la face de la terre.
15 Sai ta tafi, ta yi yadda Iliya ya faɗa mata. Saboda haka aka kasance da abinci kowace rana wa Iliya da kuma don macen da iyalinta.
Cette femme s’en alla donc, et fit selon la parole d’Elie; et il mangea lui-même, et elle et sa maison; et depuis ce jour-là
16 Gama tulun garin bai ƙare ba, kwalabar man kuma bai bushe ba, kamar yadda Ubangiji ya faɗa wa Iliya.
La cruche de farine ne manqua point, et l’huile du flacon ne diminua point, selon la parole que le Seigneur avait dite par l’entremise d’Elie.
17 Ana nan sai ɗan matan, wato, gwauruwan nan ya fara ciwo. Ciwon ya ƙara muni, daga ƙarshe sai ya daina numfashi.
Or il arriva ensuite que le fils de cette femme, mère de famille, fut malade; et sa maladie fut très violente, en sorte qu’il ne restait pas en lui un souffle.
18 Sai ta ce wa Iliya, “Mutumin Allah, yaya haka? Ka zo ne domin ka nuna wa Allah zunubaina, ka kuma jawo mutuwar ɗana?”
Cette femme dit donc à Elie: Qu’importe à moi et à toi, homme de Dieu? Es-tu entré chez moi pour renouveler la mémoire de mes péchés et pour faire mourir mon fils?
19 Iliya ya ce, “Ki miƙa mini ɗanki.” Sai ya ɗauke shi daga hannuwanta, ya kai shi ɗakin sama inda yake zama, ya kwantar da shi a gadonsa.
Et Elie lui répondit: Donne-moi ton fils. Et il le prit de dessus son sein, le porta dans la chambre où lui-même demeurait, et il le mit sur son lit.
20 Sa’an nan ya yi kuka ga Ubangiji ya ce, “Ya Ubangiji Allahna, don me ka kawo wannan masifa a kan gwauruwan nan? Kai ka ce in zauna tare da ita, ga shi yanzu ɗanta ya mutu.”
Puis il cria au Seigneur et dit: Seigneur mon Dieu, même la veuve chez laquelle moi-même en tout cas je suis nourri, vous l’avez affligée au point de faire mourir son fils?
21 Sai ya kwanta, ya miƙe kansa a kan yaron sau uku, ya kuma yi kuka ga Ubangiji ya ce, “Ya Ubangiji Allahna, ka mai da ran yaron nan!”
Et il s’étendit et se rapetissa sur l’enfant jusqu’à sa mesure, par trois fois, puis il cria au Seigneur et dit: Seigneur mon Dieu, je vous conjure, que l’âme de cet enfant retourne en son corps.
22 Ubangiji kuwa ya ji kukan Iliya, sai ran yaron ya dawo masa, ya kuma rayu.
Et le Seigneur exauça la voix d’Elie, et l’âme de l’enfant retourna en lui, et il revécut.
23 Iliya ya ɗauki yaron ya sauko da shi daga ɗakin sama zuwa cikin gida. Ya ba da shi ga mahaifiyarsa, ya ce, “Duba, ɗanki yana da rai!”
Alors Elie prit l’enfant, le mena de sa chambre au bas de la maison, le remit à sa mère, et lui dit: Vois, ton fils vit.
24 Sai matar ta ce wa Iliya, “Yanzu na san cewa kai mutumin Allah ne, Ubangiji kuma yana magana ta wurinka.”
Et la femme répondit à Elie: Maintenant je reconnais en cela que tu es un homme de Dieu, et que la parole du Seigneur en ta bouche est véritable.

< 1 Sarakuna 17 >