< 1 Sarakuna 17 >

1 To, Iliya mutumin Tishbe, daga Tishbe a Gileyad, ya ce wa Ahab, “Muddin Ubangiji, Allah na Isra’ila wanda nake bauta wa yana a raye, ba za a yi raɓa ko ruwan sama a’yan shekaru masu zuwa ba, sai ko na faɗa haka.”
Tisjbiten Elias fra Tisjbe i Gilead sagde til Akab: »Saa sandt HERREN, Israels Gud, lever, han, for hvis Aasyn jeg staar, i de kommende Aar skal der ikke falde Dug eller Regn uden paa mit udtrykkelige Bud!«
2 Sai maganar Ubangiji ta zo wa Iliya, ta ce,
Derpaa kom HERRENS Ord til ham saaledes:
3 “Ka bar nan, ka nufi wajajen gabas, ka ɓuya a Rafin Kerit, gabas da Urdun.
»Gaa bort herfra og begiv dig østerpaa og hold dig skjult ved Bækken Krit østen for Jordan;
4 Za ka sha daga rafin, zan kuma umarci hankaki su ciyar da kai a can.”
du skal drikke af Bækken, og Ravnene har jeg paalagt at sørge for Føde til dig der.«
5 Saboda haka sai Iliya ya yi abin da Ubangiji ya faɗa masa. Ya tafi Rafin Kerit, gabas da Urdun, ya zauna a can.
Da gik han og gjorde efter HERRENS Ord, han gik hen og tog Bolig ved Bækken Krit østen for Jordan;
6 Hankaki suka riƙa kawo masa abinci da nama, safe da yamma, ya kuma sha daga rafin.
og Ravnene bragte ham Brød om Morgenen og Kød om Aftenen, og han drak af Bækken.
7 Ana nan sai rafin ya bushe saboda ba a yi ruwan sama a ƙasar ba.
Men nogen Tid efter tørrede Bækken ud, eftersom der ingen Regn faldt i Landet.
8 Sai maganar Ubangiji ta zo wa Iliya cewa,
Da kom HERRENS Ord til ham saaledes:
9 “Je ka, nan take, zuwa Zarefat na Sidon, ka zauna a can. Na umarci wata gwauruwa a can tă ciyar da kai.”
»Begiv dig til Zarepta, som hører til Zidon, og tag Bolig der; se, jeg har paalagt en Enke der at sørge for Føde til dig.«
10 Saboda haka sai ya tafi Zarefat. Sa’ad da ya isa ƙofar gari, sai ga wata gwauruwa tana tattara’yan itace. Sai ya kira ta, ya ce, “Ki kawo mini ɗan ruwa a tulu don in sha.”
Saa begav han sig til Zarepta, og da han kom til Byens Port, fik han Øje paa en Enke, som var ved at sanke Brænde, og raabte til hende: »Hent mig lidt Vand i et Kar, for at jeg kan drikke!«
11 Da ta kama hanya za tă tafi tă kawo, sai ya sāke kiranta ya ce, “Ina roƙonki, ki kuma kawo mini ɗan abinci.”
Og da hun gik bort for at hente det, raabte han efter hende: »Tag ogsaa et Stykke Brød med til mig!«
12 Sai ta ce masa, “Na rantse da Ubangiji Allahnka, ba ni da wani abinci, sai dai ɗan gari hannu guda a tulu, da kuma ɗan mai a kwalaba. Ina tattara’yan itacen nan ne don in kai gida in yi abinci wa kaina da ɗana, don mu ci, mu mutu.”
Men hun svarede: »Saa sandt HERREN din Gud lever, jeg ejer ikke Brød, men kun en Haandfuld Mel i Krukken og lidt Olie i Dunken; jeg var netop ved at sanke et Par Stykker Brænde for at gaa hjem og tillave det til mig og min Søn; og naar vi har spist det, maa vi dø!«
13 Iliya ya ce mata, “Kada ki ji tsoro. Ki tafi gida, ki yi yadda kika ce. Amma da farko ki yi mini’yar wainar burodi daga abin da kike da shi ki kawo mini, sa’an nan ki yi wani abu wa kanki da kuma ɗanki.
Da sagde Elias til hende: »Frygt ikke! Gaa hjem og gør, som du siger; men lav først et lille Brød deraf til mig og bring mig det; siden kan du lave noget til dig selv og din Søn!
14 Gama abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila ya ce, ‘Tulun garin ba zai ƙare ba, kwalabar man kuma ba zai bushe ba sai ranar da Ubangiji ya bayar da ruwan sama a ƙasar.’”
Thi saa siger HERREN, Israels Gud: Melkrukken skal ikke blive tom, og Olien i Dunken skal ikke slippe op, før den Dag HERREN sender Regn over Jorden!«
15 Sai ta tafi, ta yi yadda Iliya ya faɗa mata. Saboda haka aka kasance da abinci kowace rana wa Iliya da kuma don macen da iyalinta.
Da gik hun og gjorde, som Elias sagde; og baade hun og han og hendes Søn havde noget at spise en Tid lang.
16 Gama tulun garin bai ƙare ba, kwalabar man kuma bai bushe ba, kamar yadda Ubangiji ya faɗa wa Iliya.
Melkrukken blev ikke tom, og Olien i Dunken slap ikke op, efter det Ord HERREN havde talet ved Elias.
17 Ana nan sai ɗan matan, wato, gwauruwan nan ya fara ciwo. Ciwon ya ƙara muni, daga ƙarshe sai ya daina numfashi.
Men nogen Tid efter blev Kvindens, Husets Ejerindes, Søn syg, og hans Sygdom tog heftigt til, saa der til sidst ikke mere var Liv i ham.
18 Sai ta ce wa Iliya, “Mutumin Allah, yaya haka? Ka zo ne domin ka nuna wa Allah zunubaina, ka kuma jawo mutuwar ɗana?”
Da sagde hun til Elias: »Hvad har jeg med dig at gøre, du Guds Mand! Er du kommet for at bringe min Synd i Erindring og volde min Søns Død?«
19 Iliya ya ce, “Ki miƙa mini ɗanki.” Sai ya ɗauke shi daga hannuwanta, ya kai shi ɗakin sama inda yake zama, ya kwantar da shi a gadonsa.
Men han svarede hende: »Lad mig faa din Søn!« Og han tog ham fra hendes Skød og bar ham op i Stuen paa Taget, hvor han boede, og lagde ham paa sin Seng.
20 Sa’an nan ya yi kuka ga Ubangiji ya ce, “Ya Ubangiji Allahna, don me ka kawo wannan masifa a kan gwauruwan nan? Kai ka ce in zauna tare da ita, ga shi yanzu ɗanta ya mutu.”
Saa raabte han til HERREN: »HERRE min Gud, vil du virkelig handle saa ilde mod den Enke; i hvis Hus jeg er Gæst, at du lader hendes Søn dø?«
21 Sai ya kwanta, ya miƙe kansa a kan yaron sau uku, ya kuma yi kuka ga Ubangiji ya ce, “Ya Ubangiji Allahna, ka mai da ran yaron nan!”
Derpaa strakte han sig tre Gange hen over Drengen og raabte til HERREN: »HERRE min Gud, lad dog Drengens Sjæl vende tilbage!«
22 Ubangiji kuwa ya ji kukan Iliya, sai ran yaron ya dawo masa, ya kuma rayu.
Og HERREN hørte Elias's Røst; Drengens Sjæl vendte tilbage, saa han blev levende.
23 Iliya ya ɗauki yaron ya sauko da shi daga ɗakin sama zuwa cikin gida. Ya ba da shi ga mahaifiyarsa, ya ce, “Duba, ɗanki yana da rai!”
Saa tog Elias Drengen og bragte ham fra Stuen paa Taget ned i Huset og gav hans Moder ham, idet han sagde: »Se, din Søn lever!«
24 Sai matar ta ce wa Iliya, “Yanzu na san cewa kai mutumin Allah ne, Ubangiji kuma yana magana ta wurinka.”
Da sagde Kvinden til Elias: »Nu ved jeg vist, at du er en Guds Mand, og at HERRENS Ord i din Mund er Sandhed.«

< 1 Sarakuna 17 >