< 1 Sarakuna 17 >

1 To, Iliya mutumin Tishbe, daga Tishbe a Gileyad, ya ce wa Ahab, “Muddin Ubangiji, Allah na Isra’ila wanda nake bauta wa yana a raye, ba za a yi raɓa ko ruwan sama a’yan shekaru masu zuwa ba, sai ko na faɗa haka.”
Og Thisbiteren Elias, en af dem, som boede i Gilead, sagde til Akab: Saa vist som Herren, Israels Gud, lever, for hvis Ansigt jeg staar, skal der hverken komme Dug eller Regn i disse Aar, uden efter mit Ord.
2 Sai maganar Ubangiji ta zo wa Iliya, ta ce,
Og Herrens Ord skete til ham og sagde:
3 “Ka bar nan, ka nufi wajajen gabas, ka ɓuya a Rafin Kerit, gabas da Urdun.
Gak herfra og vend dig imod Østen og skjul dig ved Bækken Krith, som er lige over for Jordanen.
4 Za ka sha daga rafin, zan kuma umarci hankaki su ciyar da kai a can.”
Og det skal ske, at du skal drikke af Bækken, og jeg har budet Ravnene, at de skulle forsørge dig der.
5 Saboda haka sai Iliya ya yi abin da Ubangiji ya faɗa masa. Ya tafi Rafin Kerit, gabas da Urdun, ya zauna a can.
Og han gik og gjorde efter Herrens Ord og gik og blev ved Bækken Krith, som er lige over for Jordanen.
6 Hankaki suka riƙa kawo masa abinci da nama, safe da yamma, ya kuma sha daga rafin.
Og Ravnene bragte ham Brød og Kød om Morgenen og Brød og Kød om Aftenen, og han drak af Bækken.
7 Ana nan sai rafin ya bushe saboda ba a yi ruwan sama a ƙasar ba.
Og det skete efter en Tids Forløb, da blev Bækken tør, thi der var ikke Regn i Landet.
8 Sai maganar Ubangiji ta zo wa Iliya cewa,
Da skete Herrens Ord til ham og sagde:
9 “Je ka, nan take, zuwa Zarefat na Sidon, ka zauna a can. Na umarci wata gwauruwa a can tă ciyar da kai.”
Staa op og gak til Sarepta, som er ved Sidon, og bliv der; se, jeg har budet der en Enke, at hun skal forsørge dig.
10 Saboda haka sai ya tafi Zarefat. Sa’ad da ya isa ƙofar gari, sai ga wata gwauruwa tana tattara’yan itace. Sai ya kira ta, ya ce, “Ki kawo mini ɗan ruwa a tulu don in sha.”
Og han stod op og gik til Sarepta og kom til Stadsporten, og se, der var en Enke, som sankede Ved; og han kaldte ad hende og sagde: Kære, hent mig lidt Vand i Karret, at jeg kan drikke.
11 Da ta kama hanya za tă tafi tă kawo, sai ya sāke kiranta ya ce, “Ina roƙonki, ki kuma kawo mini ɗan abinci.”
Da gik hun at hente, og han kaldte ad hende og sagde: Kære, tag mig et Stykke Brød med i din Haand.
12 Sai ta ce masa, “Na rantse da Ubangiji Allahnka, ba ni da wani abinci, sai dai ɗan gari hannu guda a tulu, da kuma ɗan mai a kwalaba. Ina tattara’yan itacen nan ne don in kai gida in yi abinci wa kaina da ɗana, don mu ci, mu mutu.”
Men hun sagde: Saa vist som Herren din Gud lever, jeg har ikke en Kage, kun en Haandfuld Mel i en Krukke og lidet Olie i et Krus; og se, jeg sanker et Par Stykker Brænde og gaar ind og vil lave det til mig og til min Søn, at vi maa æde det og dø.
13 Iliya ya ce mata, “Kada ki ji tsoro. Ki tafi gida, ki yi yadda kika ce. Amma da farko ki yi mini’yar wainar burodi daga abin da kike da shi ki kawo mini, sa’an nan ki yi wani abu wa kanki da kuma ɗanki.
Og Elias sagde til hende: Frygt ikke, gak ind, gør det efter dine Ord; dog lav mig først en liden Kage deraf og bring mig den ud, siden skal du lave dig og din Søn noget.
14 Gama abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila ya ce, ‘Tulun garin ba zai ƙare ba, kwalabar man kuma ba zai bushe ba sai ranar da Ubangiji ya bayar da ruwan sama a ƙasar.’”
Thi saa siger Herren, Israels Gud: Melet i Krukken skal ikke fortæres, og Oliekruset skal ikke blive tomt indtil den Dag, at Herren skal give Regn over Jorderige.
15 Sai ta tafi, ta yi yadda Iliya ya faɗa mata. Saboda haka aka kasance da abinci kowace rana wa Iliya da kuma don macen da iyalinta.
Og hun gik og gjorde efter Elias's Ord; og hun aad, ja, han og hun og hendes Hus i en god Tid.
16 Gama tulun garin bai ƙare ba, kwalabar man kuma bai bushe ba, kamar yadda Ubangiji ya faɗa wa Iliya.
Melet i Krukken blev ikke fortæret, og Oliekruset blev ikke tomt, efter Herrens Ord, som han talte ved Elias.
17 Ana nan sai ɗan matan, wato, gwauruwan nan ya fara ciwo. Ciwon ya ƙara muni, daga ƙarshe sai ya daina numfashi.
Og det skete efter disse Handeler, at samme Kvindes, Husets Ejerindes, Søn blev syg, og hans Sygdom var saare svar, indtil der ikke mere var Aande i ham.
18 Sai ta ce wa Iliya, “Mutumin Allah, yaya haka? Ka zo ne domin ka nuna wa Allah zunubaina, ka kuma jawo mutuwar ɗana?”
Og hun sagde til Elias: Hvad har jeg at gøre med dig, du Guds Mand? du er kommen til mig at lade min Misgerning kommes i Hu og at dræbe min Søn.
19 Iliya ya ce, “Ki miƙa mini ɗanki.” Sai ya ɗauke shi daga hannuwanta, ya kai shi ɗakin sama inda yake zama, ya kwantar da shi a gadonsa.
Og han sagde til hende: Giv mig hid din Søn; og han tog ham af hendes Skød og bar ham op paa Salen, hvor han boede, og han lagde ham paa sin Seng,
20 Sa’an nan ya yi kuka ga Ubangiji ya ce, “Ya Ubangiji Allahna, don me ka kawo wannan masifa a kan gwauruwan nan? Kai ka ce in zauna tare da ita, ga shi yanzu ɗanta ya mutu.”
og han raabte til Herren og sagde: Herre, min Gud! har du virkelig bragt Ulykke over denne Enke, som jeg opholder mig hos, saa at du dræber hendes Søn?
21 Sai ya kwanta, ya miƙe kansa a kan yaron sau uku, ya kuma yi kuka ga Ubangiji ya ce, “Ya Ubangiji Allahna, ka mai da ran yaron nan!”
Saa udstrakte han sig over Barnet tre Gange og raabte til Herren og sagde: Herre, min Gud! Kære, lad dette Barns Sjæl komme inden i det igen!
22 Ubangiji kuwa ya ji kukan Iliya, sai ran yaron ya dawo masa, ya kuma rayu.
Og Herren hørte Elias's Røst, og Barnets Sjæl kom inden i det igen, og det blev levende.
23 Iliya ya ɗauki yaron ya sauko da shi daga ɗakin sama zuwa cikin gida. Ya ba da shi ga mahaifiyarsa, ya ce, “Duba, ɗanki yana da rai!”
Og Elias tog Barnet og førte det ned fra Salen i Huset og gav hans Moder det, og Elias sagde: Se, din Søn lever.
24 Sai matar ta ce wa Iliya, “Yanzu na san cewa kai mutumin Allah ne, Ubangiji kuma yana magana ta wurinka.”
Og Kvinden sagde til Elias: Nu ved jeg dette, at du er en Guds Mand, og at Herrens Ord i din Mund er Sandhed.

< 1 Sarakuna 17 >