< 1 Sarakuna 16 >

1 Sai maganar Ubangiji ta zo wa Yehu ɗan Hanani game da Ba’asha,
خداوند به ییهو نبی فرمود که این پیغام را به بعشا بدهد:
2 “Na ɗaga ka daga ƙura na mai da kai shugaban mutanena Isra’ila, amma ka yi tafiya a hanyoyin Yerobowam, ka kuma sa mutanena Isra’ila suka yi zunubi, ka tsokane ni na yi fushi ta wurin zunubansu.
«تو را از روی خاک بلند کردم و به سلطنت قوم خود اسرائیل رساندم؛ اما تو مانند یربعام گناه ورزیدی و قوم مرا به گناه کشانیدی و آنها نیز با گناهانشان مرا خشمگین نمودند.
3 Saboda haka ina gab da cinye Ba’asha da gidansa, zan kuma mai da gidanka kamar na Yerobowam ɗan Nebat.
پس تو و خاندان تو را مثل خاندان یربعام پسر نِباط نابود می‌کنم.
4 Karnuka za su cinye waɗanda suke na Ba’asha da suka mutu a birni, tsuntsaye kuma za su cinye waɗanda suka mutu a jeji.”
از خانهٔ تو آنکه در شهر بمیرد، سگها او را می‌خورند و آنکه در صحرا بمیرد، لاشخورها او را می‌خورند!»
5 Game da sauran ayyukan mulkin Ba’asha, abin da ya yi, da kuma nasarorinsa, an rubuta su cikin littafin tarihin sarakunan Isra’ila.
این پیغام برای بعشا و خاندانش فرستاده شد، زیرا او مانند یربعام با کارهای زشت و شرم‌آور خود خداوند را خشمگین کرده بود و نیز خاندان یربعام را از بین برده بود. وقتی بعشا مرد او را در ترصه دفن کردند و پسرش ایله به جای او پادشاه شد. بقیهٔ رویدادهای سلطنت بعشا، یعنی فتوحات و کارهای او در کتاب «تاریخ پادشاهان اسرائیل» نوشته شده است.
6 Ba’asha ya huta tare da kakanninsa, aka kuma binne shi a Tirza. Sai Ela ɗansa ya gāje shi a matsayin sarki.
7 Ban da haka, maganar Ubangiji ta zo ta wurin annabi Yehu ɗan Hanani wa Ba’asha da gidansa, saboda dukan muguntar da ya aikata a gaban Ubangiji, ya tsokane shi yă yi fushi ta wurin abubuwan da ya yi, da kuma zama kamar gidan Yerobowam, da kuma domin ya hallaka gidan Yerobowam.
8 A shekara ta ashirin da shida ta Asa sarkin Yahuda, Ela ɗan Ba’asha ya zama sarkin Isra’ila, ya kuma yi mulki a Tirza shekaru biyu.
در بیست و ششمین سال سلطنت آسا پادشاه یهودا، ایله پسر بعشا بر تخت سلطنت اسرائیل نشست و دو سال در ترصه سلطنت کرد.
9 Zimri, ɗaya daga cikin shugabanni, wanda ya shugabanci rabin kekunan yaƙin Ela, ya yi maƙarƙashiya a kansa. Ela yana a Tirza a lokacin, ya bugu a gidan Arza, sarkin fada a Tirza.
زمری که فرماندهی نیمی از ارابه‌های سلطنتی را به عهده داشت، علیه او توطئه چید. یک روز که ایله پادشاه در ترصه، در خانهٔ ارصا، وزیر دربار خود، بر اثر نوشیدن شراب مست شده بود،
10 Zimri ya shiga, ya buge shi ya kashe a shekara ta ashirin da bakwai na Asa sarkin Yahuda. Sa’an nan ya gāje shi a matsayin sarki.
زمری وارد خانه شد و به ایله حمله کرد و او را کشت. این واقعه در بیست و هفتمین سال سلطنت آسا پادشاه یهودا رخ داد. از آن تاریخ زمری خود را پادشاه اسرائیل اعلام کرد.
11 Nan da nan sai ya fara mulki ya kuwa zauna a kujerar sarauta, ya kashe dukan iyalin Ba’asha. Bai bar namiji guda ɗaya ba, ko dangi, ko aboki.
وقتی زمری بر تخت سلطنت نشست، اعضای خاندان بعشا را قتل عام کرد و حتی یک مرد از خویشاوندان و دوستان بعشا را زنده نگذاشت.
12 Ta haka Zimri ya hallaka dukan iyalin Ba’asha, bisa ga maganar da Ubangiji ya yi game da Ba’asha ta wurin annabi Yehu.
نابودی فرزندان بعشا که خداوند توسط ییهو نبی قبلاً خبر داده بود،
13 Wannan ya faru saboda dukan zunuban Ba’asha da waɗanda ɗansa Ela ya yi, da ya sa Isra’ila suka yi, har suka tsokane Ubangiji, Allah na Isra’ila, yă yi fushi ta wurin gumakansu marasa amfani.
به این سبب بود که بعشا و پسرش ایله گناه ورزیده، بنی‌اسرائیل را به بت‌پرستی کشاندند و به این ترتیب خشم خداوند را برانگیختند.
14 Game da sauran ayyukan mulkin Ela, da dukan abin da ya yi, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Isra’ila.
بقیهٔ رویدادهای سلطنت ایله در کتاب «تاریخ پادشاهان اسرائیل» نوشته شده است.
15 A shekara ta ashirin da bakwai na Asa sarkin Yahuda, Zimri ya yi mulki a Tirza kwana bakwai. Mayaƙa suka yi sansani kusa da Gibbeton, wani garin Filistiyawa.
زمری در بیست و هفتمین سال سلطنت آسا پادشاه یهودا، پادشاه اسرائیل شد و فقط هفت روز در ترصه سلطنت کرد. لشکر اسرائیل علیه شهر فلسطینی جِبِتون اردو زده بود.
16 Sa’ad da Isra’ilawa a cikin sansani suka ji cewa Zimri ya yi maƙarƙashiya a kan sarki, ya kuma kashe shi, sai suka yi shela, suka naɗa Omri, shugaban mayaƙa ya zama sarki a bisa Isra’ila, a wannan rana a cikin sansani.
وقتی سربازان اسرائیل که آمادهٔ حمله به جبتون بودند، شنیدند که زمری، پادشاه را کشته است، عمری را که سردار سپاه بود همان جا پادشاه خود ساختند.
17 Sai Omri da dukan Isra’ilawa suka janye daga Gibbeton, suka yi wa Tirza kwanto.
عمری بی‌درنگ با نیروهای خود به ترصه برگشت و آن را محاصره کرد.
18 Da Zimri ya ga cewa an kame birnin, sai ya je ya shiga hasumiya fadan sarki ya sa wa fadan wuta wutar kuwa ta ƙone shi ya mutu.
زمری وقتی دید که شهر محاصره شده، به داخل کاخ سلطنتی رفت و آن را آتش زد. او خود نیز در میان شعله‌های آتش سوخت.
19 Wannan ya faru saboda zunuban da ya yi, ya yi mugunta a gaban Ubangiji ya kuma yi tafiya a hanyoyin Yerobowam da kuma cikin zunubin da Yerobowam ya yi da ya sa Isra’ila suka yi.
او مانند یربعام نسبت به خداوند گناه ورزید و اسرائیل را به گناه کشاند.
20 Game da sauran ayyukan mulkin Zimri, da tawayen da ya yi, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Isra’ila.
بقیه وقایع زندگی زمری و شرح شورش او در کتاب «تاریخ پادشاهان اسرائیل» نوشته شده است.
21 Sai mutanen Isra’ila suka rabu kashi biyu; rabi guda sun goyi bayan Tibni ɗan Ginat yă zama sarki, ɗayan rabin kuma sun goyi bayan Omri.
در آن روزها بین مردم اسرائیل دو دستگی افتاد. نیمی از مردم طرفدار عمری بودند و نیمی دیگر از تبنی پسر جینت پشتیبانی می‌کردند.
22 Amma mabiyan Omri suka nuna sun fi na Tibni ɗan Ginat ƙarfi. Sai Tibni ya mutu, Omri kuwa ya zama sarki.
ولی سرانجام طرفداران عمری پیروز شدند. تبنی کشته شد و عمری به سلطنت رسید.
23 A shekara ta talatin da ɗaya na Asa sarkin Yahuda, Omri ya zama sarkin Isra’ila, ya kuma yi mulki shekara goma sha biyu, shekaru shida a Tirza.
در سی و یکمین سال سلطنت آسا پادشاه یهودا، عمری پادشاه اسرائیل شد و دوازده سال سلطنت کرد. از این دوازده سال، شش سال را در ترصه سلطنت کرد.
24 Ya saya tudun Samariya daga Shemer, a bakin talentin biyu na azurfa, ya kuma gina birni a kan tudun, ya kira shi Samariya, bayan Shemer, sunan mai tudun a dā.
او تپهٔ سامره را از شخصی به نام سامر به هفتاد کیلو نقره خرید و شهری روی آن ساخت و نام آن را سامره گذاشت.
25 Amma Omri ya yi mugunta a gaban Ubangiji, ya kuma yi zunubi fiye da dukan waɗanda suka kasance kafin shi.
ولی عمری بیش از پادشاهان قبل نسبت به خداوند گناه ورزید.
26 Ya yi tafiya a dukan hanyoyin Yerobowam ɗan Nebat da kuma cikin zunubinsa wanda ya sa Isra’ila suka yi, har suka tsokane Ubangiji, Allah na Isra’ila yă yi fushi ta wurin gumakansu marasa amfani.
او مانند یرُبعام پسر نِباط به پرستیدن بت پرداخت و قوم اسرائیل را به گمراهی کشاند و به این وسیله خشم خداوند، خدای اسرائیل را برانگیخت.
27 Game da sauran ayyukan mulkin Omri, abin da ya yi, da kuma abubuwan da ya yi, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Isra’ila.
بقیه رویدادهای سلطنت و فتوحات عمری در کتاب «تاریخ پادشاهان اسرائیل» نوشته شده است.
28 Omri ya huta tare da kakanninsa, aka kuma binne shi a Samariya. Sai Ahab ya gāje shi a matsayin sarki.
وقتی عمری مرد او را در سامره دفن کردند و پسرش اَخاب به جای او پادشاه شد.
29 A shekara ta talatin da takwas ta Asa sarkin Yahuda, Ahab ɗan Omri ya zama sarkin Isra’ila, ya kuma yi mulki a Samariya a kan Isra’ila, shekara ashirin da biyu.
در سی و هشتمین سال سلطنت آسا پادشاه یهودا، اَخاب پسر عُمری پادشاه اسرائیل شد و بیست و دو سال در سامره سلطنت کرد.
30 Ahab ɗan Omri ya yi mugunta sosai a gaban Ubangiji fiye da wani daga cikin waɗanda suka riga shi.
اَخاب بیش از پادشاهان قبل نسبت به خداوند گناه ورزید.
31 Bai zama masa wani abu mai wuya ba, yă yi zunuban Yerobowam ɗan Nebat, har ma ya auri Yezebel’yar Etba’al sarkin Sidoniyawa, ya kuma fara bauta wa Ba’al, ya yi masa sujada.
او نه فقط مثل یربعام پسر نِباط مرتکب گناه شد، بلکه با ایزابل دختر اتبعل، پادشاه صیدون نیز ازدواج کرد و بت بعل صیدونی‌ها را پرستید و در برابر آن سجده کرد.
32 Ya kafa bagade domin Ba’al a haikalin Ba’al da ya gina a Samariya.
او در سامره یک بتخانه و یک مذبح برای بعل ساخت،
33 Ahab ya gina ginshiƙin Ashera, ya kuma aikata abubuwa masu yawa don yă tsokane Ubangiji, Allah na Isra’ila yă yi fushi fiye da dukan sarakunan Isra’ila da suka riga shi.
بعد از آن بت اَشیره را ساخت و با این اعمال خود بیش از هر پادشاهی که قبل از او در اسرائیل سلطنت کرده بود، خداوند، خدای اسرائیل را خشمگین نمود.
34 A lokaci Ahab ne, Hiyel mutumin Betel ya sāke gina Yeriko. Ya kafa tushensa a bakin ran ɗan farinsa Abiram, ya kuma kafa ƙofofinsa a bakin ran autansa Segub, bisa ga maganar Ubangiji da ya yi ta wurin Yoshuwa ɗan Nun.
در دورهٔ سلطنت او مردی از بیت‌ئیل به نام حی‌ئیل، شهر اریحا را دوباره بنا کرد. اما وقتی پایه‌های آن را می‌نهاد، پسر بزرگش ابیرام مرد و وقتی آن را تمام کرد و دروازه‌هایش را کار گذاشت، پسر کوچکش سجوب مرد. این به سبب لعنت خداوند بر اریحا بود که توسط یوشع پسر نون اعلام شده بود.

< 1 Sarakuna 16 >