< 1 Sarakuna 16 >

1 Sai maganar Ubangiji ta zo wa Yehu ɗan Hanani game da Ba’asha,
Alors la parole de l'Eternel fut adressée à Jéhu, fils de Hanani, contre Bahasa, pour lui dire:
2 “Na ɗaga ka daga ƙura na mai da kai shugaban mutanena Isra’ila, amma ka yi tafiya a hanyoyin Yerobowam, ka kuma sa mutanena Isra’ila suka yi zunubi, ka tsokane ni na yi fushi ta wurin zunubansu.
Parce que je t'ai élevé de la poudre, et que je t'ai établi Conducteur de mon peuple d'Israël, et que malgré cela tu as suivi le train de Jéroboam, et as fait pécher mon peuple d'Israël, pour m'irriter par leurs péchés.
3 Saboda haka ina gab da cinye Ba’asha da gidansa, zan kuma mai da gidanka kamar na Yerobowam ɗan Nebat.
Voici, je m'en vais entièrement exterminer Bahasa, et sa maison, et je mettrai ta maison au même état que j'ai mis la maison de Jéroboam fils de Nébat.
4 Karnuka za su cinye waɗanda suke na Ba’asha da suka mutu a birni, tsuntsaye kuma za su cinye waɗanda suka mutu a jeji.”
Celui [de la race] de Bahasa qui mourra dans la ville, les chiens le mangeront; et celui des siens qui mourra aux champs, les oiseaux des cieux le mangeront.
5 Game da sauran ayyukan mulkin Ba’asha, abin da ya yi, da kuma nasarorinsa, an rubuta su cikin littafin tarihin sarakunan Isra’ila.
Le reste des faits de Bahasa, ce qu'il a fait, et sa valeur, n'est-il pas écrit au Livre des Chroniques des Rois d'Israël.
6 Ba’asha ya huta tare da kakanninsa, aka kuma binne shi a Tirza. Sai Ela ɗansa ya gāje shi a matsayin sarki.
Ainsi Bahasa s'endormit avec ses pères, et fut enseveli à Tirtsa, et Ela son fils régna en sa place.
7 Ban da haka, maganar Ubangiji ta zo ta wurin annabi Yehu ɗan Hanani wa Ba’asha da gidansa, saboda dukan muguntar da ya aikata a gaban Ubangiji, ya tsokane shi yă yi fushi ta wurin abubuwan da ya yi, da kuma zama kamar gidan Yerobowam, da kuma domin ya hallaka gidan Yerobowam.
La parole de l'Eternel fut aussi [adressée] par le moyen de Jéhu, fils de Hanani le Prophète, contre Bahasa, et contre sa maison, à cause de tout le mal qu'il avait fait devant l'Eternel, en l'irritant par l'œuvre de ses mains, [pour lui dire] qu'il en serait comme de la maison de Jéroboam; même parce qu'il l'avait frappée.
8 A shekara ta ashirin da shida ta Asa sarkin Yahuda, Ela ɗan Ba’asha ya zama sarkin Isra’ila, ya kuma yi mulki a Tirza shekaru biyu.
L'an vingt et sixième d'Asa Roi de Juda, Ela fils de Bahasa commença à régner sur Israël, et il [régna] deux ans à Tirtsa.
9 Zimri, ɗaya daga cikin shugabanni, wanda ya shugabanci rabin kekunan yaƙin Ela, ya yi maƙarƙashiya a kansa. Ela yana a Tirza a lokacin, ya bugu a gidan Arza, sarkin fada a Tirza.
Et Zimri son serviteur, capitaine de la moitié des chariots, fit une conspiration contre Ela, lorsqu'il était à Tirtsa buvant et s'enivrant dans la maison d'Artsa son maître d'hôtel, à Tirtsa.
10 Zimri ya shiga, ya buge shi ya kashe a shekara ta ashirin da bakwai na Asa sarkin Yahuda. Sa’an nan ya gāje shi a matsayin sarki.
Zimri donc vint, et le frappa, et le tua l'an vingt et septième d'Asa Roi de Juda, et régna en sa place.
11 Nan da nan sai ya fara mulki ya kuwa zauna a kujerar sarauta, ya kashe dukan iyalin Ba’asha. Bai bar namiji guda ɗaya ba, ko dangi, ko aboki.
Et comme il entrait en son règne, sitôt qu'il fut assis sur son trône, il frappa toute la maison de Bahasa; il n'en laissa rien depuis l'homme jusqu'à un chien; [il ne lui laissa] ni parent, ni ami.
12 Ta haka Zimri ya hallaka dukan iyalin Ba’asha, bisa ga maganar da Ubangiji ya yi game da Ba’asha ta wurin annabi Yehu.
Ainsi Zimri extermina toute la maison de Bahasa, selon la parole que l'Eternel avait proférée contre Bahasa, par le moyen de Jéhu le Prophète;
13 Wannan ya faru saboda dukan zunuban Ba’asha da waɗanda ɗansa Ela ya yi, da ya sa Isra’ila suka yi, har suka tsokane Ubangiji, Allah na Isra’ila, yă yi fushi ta wurin gumakansu marasa amfani.
A cause de tous les péchés de Bahasa, et des péchés d'Ela son fils, par lesquels ils avaient péché, et avaient fait pécher Israël, irritant l'Eternel le Dieu d'Israël par leurs vanités.
14 Game da sauran ayyukan mulkin Ela, da dukan abin da ya yi, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Isra’ila.
Le reste des faits d'Ela, et même tout ce qu'il a fait, n'est-il pas écrit au Livre des Chroniques des Rois d'Israël?
15 A shekara ta ashirin da bakwai na Asa sarkin Yahuda, Zimri ya yi mulki a Tirza kwana bakwai. Mayaƙa suka yi sansani kusa da Gibbeton, wani garin Filistiyawa.
La vingt et septième année d'Asa Roi de Juda, Zimri régna sept jours à Tirtsa; or le peuple était campé contre Guibbethon qui était aux Philistins.
16 Sa’ad da Isra’ilawa a cikin sansani suka ji cewa Zimri ya yi maƙarƙashiya a kan sarki, ya kuma kashe shi, sai suka yi shela, suka naɗa Omri, shugaban mayaƙa ya zama sarki a bisa Isra’ila, a wannan rana a cikin sansani.
Et le peuple qui était-là campé, entendit qu'on disait: Zimri a fait une conspiration, et il a même tué le Roi; c'est pourquoi en ce même jour tout Israël établit dans le camp pour Roi Homri, capitaine de l'armée d'Israël.
17 Sai Omri da dukan Isra’ilawa suka janye daga Gibbeton, suka yi wa Tirza kwanto.
Et Homri et tout Israël montèrent de devant Guibbethon, et assiégèrent Tirtsa.
18 Da Zimri ya ga cewa an kame birnin, sai ya je ya shiga hasumiya fadan sarki ya sa wa fadan wuta wutar kuwa ta ƙone shi ya mutu.
Mais dès que Zimri eut vu que la ville était prise, il entra au palais de la maison Royale, et brûla sur soi la maison Royale, et il mourut;
19 Wannan ya faru saboda zunuban da ya yi, ya yi mugunta a gaban Ubangiji ya kuma yi tafiya a hanyoyin Yerobowam da kuma cikin zunubin da Yerobowam ya yi da ya sa Isra’ila suka yi.
A cause des péchés par lesquels il avait péché, faisant ce qui déplaît à l'Eternel, en suivant le train de Jéroboam, et son péché, qu'il avait fait pour faire pécher Israël.
20 Game da sauran ayyukan mulkin Zimri, da tawayen da ya yi, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Isra’ila.
Le reste des faits de Zimri, et la conspiration qu'il fit, toutes ces choses ne sont-elles pas écrites au Livre des Chroniques des Rois d'Israël?
21 Sai mutanen Isra’ila suka rabu kashi biyu; rabi guda sun goyi bayan Tibni ɗan Ginat yă zama sarki, ɗayan rabin kuma sun goyi bayan Omri.
Alors le peuple d'Israël se divisa en deux partis; la moitié du peuple suivait Tibni fils de Guinath, pour le faire Roi; et l'autre moitié suivait Homri.
22 Amma mabiyan Omri suka nuna sun fi na Tibni ɗan Ginat ƙarfi. Sai Tibni ya mutu, Omri kuwa ya zama sarki.
Mais le peuple qui suivait Homri, fut plus fort que le peuple qui suivait Tibni fils de Guinath, et Tibni mourut, et Homri régna.
23 A shekara ta talatin da ɗaya na Asa sarkin Yahuda, Omri ya zama sarkin Isra’ila, ya kuma yi mulki shekara goma sha biyu, shekaru shida a Tirza.
La trente et unième année d'Asa Roi de Juda, Homri commença à régner sur Israël, [et il régna] douze ans; il régna six ans à Tirtsa.
24 Ya saya tudun Samariya daga Shemer, a bakin talentin biyu na azurfa, ya kuma gina birni a kan tudun, ya kira shi Samariya, bayan Shemer, sunan mai tudun a dā.
Puis il acheta de Sémer la montagne de Samarie, deux talents d'argent; et il bâtit [une ville] sur cette montagne, et il nomma la ville qu'il bâtit, du nom de Sémer, Seigneur de la montagne de Samarie.
25 Amma Omri ya yi mugunta a gaban Ubangiji, ya kuma yi zunubi fiye da dukan waɗanda suka kasance kafin shi.
Et Homri fit ce qui déplaît à l'Eternel; il fit même pis que tous ceux qui avaient été avant lui.
26 Ya yi tafiya a dukan hanyoyin Yerobowam ɗan Nebat da kuma cikin zunubinsa wanda ya sa Isra’ila suka yi, har suka tsokane Ubangiji, Allah na Isra’ila yă yi fushi ta wurin gumakansu marasa amfani.
Car il suivit tout le train de Jéroboam fils de Nébat, et son péché, par lequel il avait fait pécher Israël, afin qu'ils irritassent l'Eternel le Dieu d'Israël par leurs vanités.
27 Game da sauran ayyukan mulkin Omri, abin da ya yi, da kuma abubuwan da ya yi, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Isra’ila.
Le reste des faits de Homri, tout ce qu'il a fait, et les exploits qu'il fit, ne sont-ils pas écrits aux Livre des Chroniques des Rois d'Israël?
28 Omri ya huta tare da kakanninsa, aka kuma binne shi a Samariya. Sai Ahab ya gāje shi a matsayin sarki.
Ainsi Homri s'endormit avec ses pères, et fut enseveli à Samarie, et Achab son fils régna en sa place.
29 A shekara ta talatin da takwas ta Asa sarkin Yahuda, Ahab ɗan Omri ya zama sarkin Isra’ila, ya kuma yi mulki a Samariya a kan Isra’ila, shekara ashirin da biyu.
Achab fils de Homri commença à régner sur Israël la trente-huitième année d'Asa Roi de Juda; et Achab fils de Homri régna sur Israël à Samarie vingt et deux ans.
30 Ahab ɗan Omri ya yi mugunta sosai a gaban Ubangiji fiye da wani daga cikin waɗanda suka riga shi.
Et Achab fils de Homri fit ce qui déplaît à l'Eternel, plus que tous ceux qui avaient été avant lui.
31 Bai zama masa wani abu mai wuya ba, yă yi zunuban Yerobowam ɗan Nebat, har ma ya auri Yezebel’yar Etba’al sarkin Sidoniyawa, ya kuma fara bauta wa Ba’al, ya yi masa sujada.
Et il arriva que, comme si ce lui eût été peu de chose de marcher dans les péchés de Jéroboam fils de Nébat, il prit pour femme Izebel, fille d'Eth-bahal, Roi des Sidoniens, puis il alla, et servit Bahal, et se prosterna devant lui.
32 Ya kafa bagade domin Ba’al a haikalin Ba’al da ya gina a Samariya.
Et il dressa un autel à Bahal, en la maison de Bahal, qu'il bâtit à Samarie.
33 Ahab ya gina ginshiƙin Ashera, ya kuma aikata abubuwa masu yawa don yă tsokane Ubangiji, Allah na Isra’ila yă yi fushi fiye da dukan sarakunan Isra’ila da suka riga shi.
Et Achab fit un bocage; de sorte qu'Achab fit encore pis que tous les Rois d'Israël qui avaient été avant lui, pour irriter l'Eternel le Dieu d'Israël.
34 A lokaci Ahab ne, Hiyel mutumin Betel ya sāke gina Yeriko. Ya kafa tushensa a bakin ran ɗan farinsa Abiram, ya kuma kafa ƙofofinsa a bakin ran autansa Segub, bisa ga maganar Ubangiji da ya yi ta wurin Yoshuwa ɗan Nun.
En son temps Hiel de Bethel bâtit Jérico, laquelle il fonda sur Abiram son premier-né, et posa ses portes sur Ségub son puîné, selon la parole que l'Eternel avait proférée par le moyen de Josué, fils de Nun.

< 1 Sarakuna 16 >