< 1 Sarakuna 15 >

1 A shekara ta goma sha takwas ta mulkin Yerobowam ɗan Nebat, Abiyam ya zama sarkin Yahuda,
Now no décimo oitavo ano do rei Jeroboão, filho de Nebat, Abijam começou a reinar sobre Judá.
2 ya kuma yi mulki a Urushalima shekara uku. Sunan mahaifiyarsa Ma’aka ne,’yar Abisalom.
Ele reinou três anos em Jerusalém. O nome de sua mãe era Maacah, filha de Abishalom.
3 Shi ma ya aikata dukan irin zunubai da tsohonsa ya yi. Zuciyarsa ba tă bi Ubangiji Allahnsa, kamar yadda zuciyar Dawuda kakansa ta yi ba.
Ele caminhou em todos os pecados de seu pai, o que havia feito antes dele; e seu coração não era perfeito com Javé, seu Deus, como o coração de Davi, seu pai.
4 Duk da haka, saboda Dawuda Ubangiji Allahnsa ya ba shi fitila a Urushalima ta wurin ta da wani da ya gāje shi, ta wurinsa kuma Urushalima ta yi ƙarfi.
Entretanto, por amor a Davi, Javé, seu Deus, deu-lhe uma lâmpada em Jerusalém, para fundar seu filho depois dele e estabelecer Jerusalém;
5 Gama Dawuda ya yi abin da yake daidai a gaban Ubangiji, bai kuma fasa kiyaye wani daga umarnan Ubangiji ba dukan kwanakinsa, sai dai a batun Uriya mutumin Hitti.
porque Davi fez o que era certo aos olhos de Javé, e não se afastou de nada do que lhe ordenou todos os dias de sua vida, exceto somente no caso de Urias, o hitita.
6 Aka yi yaƙi tsakanin Rehobowam da Yerobowam a duk kwanakin Abiya.
Agora havia guerra entre Rehoboam e Jeroboão todos os dias de sua vida.
7 Game da sauran ayyukan mulkin Abiyam kuwa, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Yahuda. Aka yi yaƙi tsakanin Abiyam da Yerobowam.
O resto dos atos de Abijam, e tudo o que ele fez, não estão escritos no livro das crônicas dos reis de Judá? Houve uma guerra entre Abijam e Jeroboão.
8 Sai Abiyam ya huta tare da kakanninsa, aka kuma binne shi a Birnin Dawuda. Asa kuwa ya gāje shi a matsayin sarki.
Abijam dormiu com seus pais, e eles o enterraram na cidade de David; e Asa seu filho reinou em seu lugar.
9 A shekara ta ashirin ta Yerobowam sarkin Isra’ila, Asa ya zama sarkin Yahuda,
No vigésimo ano de Jeroboão, rei de Israel, Asa começou a reinar sobre Judá.
10 ya yi mulki a Urushalima shekara arba’in da ɗaya. Sunan mahaifiya mahaifiyarsa, Ma’aka ne’yar Abisalom.
Ele reinou quarenta e um anos em Jerusalém. O nome de sua mãe era Maaca, filha de Abishalom.
11 Asa ya yi abin da yake daidai a gaban Ubangiji, kamar yadda kakansa Dawuda ya yi.
Asa fez o que era certo aos olhos de Iavé, como fez Davi, seu pai.
12 Ya kori dukan maza karuwai na masujadai daga ƙasar, ya kuma yi waje da dukan gumakan da mahaifinsa ya yi.
Ele expulsou os sodomitas da terra e removeu todos os ídolos que seus pais haviam feito.
13 Ya tuɓe mahaifiya mahaifiyarsa Ma’aka daga matsayinta na mahaifiyar sarauniya, gama ta gina ƙazantaccen ginshiƙin Ashera. Asa ya yanke ginshiƙin, ya kuma ƙone shi a Kwarin Kidron.
Ele também removeu Maacah sua mãe de ser rainha, porque ela tinha feito uma imagem abominável para uma Asherah. Asa cortou sua imagem e a queimou no riacho Kidron.
14 Ko da yake bai cire masujadai da suke kan tuddai ba, zuciyar Asa ta kasance da aminci ɗungum ga Ubangiji dukan kwanakinsa.
Mas os lugares altos não foram tirados. No entanto, o coração de Asa foi perfeito com Yahweh durante todos os seus dias.
15 Ya kawo azurfa da zinariya da kayayyakin da shi da mahaifinsa suka keɓe a haikalin Ubangiji.
Ele trouxe para a casa de Yahweh as coisas que seu pai havia dedicado, e as coisas que ele mesmo havia dedicado: prata, ouro e utensílios.
16 Aka yi yaƙi tsakanin Asa da Ba’asha sarkin Isra’ila dukan kwanakin mulkinsu.
Houve guerra entre Asa e Baasha, rei de Israel, durante todos os seus dias.
17 Ba’asha sarkin Isra’ila ya haura, ya yi yaƙi da Yahuda, ya kuma gina Rama don yă hana wani daga fita ko shiga yankin Asa, sarkin Yahuda.
Baasa, rei de Israel, subiu contra Judá, e construiu Ramá, para não permitir que ninguém saísse ou entrasse para Asa, rei de Judá.
18 Sai Asa ya ɗauki dukan azurfa da kuma zinariyar da suka rage a ma’ajin haikalin Ubangiji da kuma nasa fadan, ya ba da su ga wani shugabansa, ya kuma aika da su zuwa ga Ben-Hadad ɗan Tabrimmon, ɗan Heziyon, sarkin Aram, wanda yake mulki a Damaskus.
Então Asa pegou toda a prata e o ouro que ficou nos tesouros da casa de Iavé, e os tesouros da casa do rei, e os entregou na mão de seus servos. Então o rei Asa os enviou a Ben Hadad, filho de Tabrimmon, filho de Hezion, rei da Síria, que vivia em Damasco, dizendo:
19 Ya ce, “Bari yarjejjeniya ta kasance tsakanina da kai, kamar yadda ta kasance tsakanin mahaifina da mahaifinka. Duba, ina aika maka kyautai na azurfa da na zinariya. Yanzu fa sai ka janye yarjejjeniyarka da Ba’asha sarkin Isra’ila, don yă janye daga gare ni.”
“Que haja um tratado entre mim e você, assim entre meu pai e seu pai”. Eis que enviei a você um presente de prata e ouro. Ide, rompei vosso tratado com Baasa, rei de Israel, para que ele se afaste de mim”.
20 Ben-Hadad ya yarda da maganar Sarki Asa, ya kuma aika shugabannin sojojin mayaƙansa ya yi yaƙi da garuruwan Isra’ila. Ya kame Iyon, Dan, Abel-Bet-Ma’aka da dukan Kinneret, haɗe da Naftali.
Ben Hadad ouviu o rei Asa, e enviou os capitães de seus exércitos contra as cidades de Israel, e atingiu Ijon, e Dan, e Abel Beth Maacah, e todo o Chinneroth, com todas as terras de Naftali.
21 Da Ba’asha ya ji haka, sai ya daina ginin Rama, ya janye zuwa Tirza.
Quando Baasha soube disso, ele parou de construir Ramah, e viveu em Tirzah.
22 Sai Sarki Asa ya ba da umarni ga dukan Yahuda, kuma babu wanda aka ware, kowa yă taimaka a kwashe duwatsu da katakan da Ba’asha yake amfani da su daga Rama. Da duwatsu da katakan ne Sarki Asa ya gina Geba a Benyamin da kuma Mizfa.
Então o rei Asa fez uma proclamação a todo Judá. Ninguém estava isento. Eles carregaram as pedras de Ramah, e sua madeira, com a qual Baasha tinha construído; e o rei Asa usou-a para construir Geba de Benjamin, e Mizpah.
23 Game da sauran ayyukan mulkin Asa, dukan nasarorinsa, dukan abin da ya yi, da kuma biranen da ya gina, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Yahuda. A tsufansa, sai ƙafafunsa suka kamu da cuta.
Agora o resto de todos os atos de Asa, e todas as suas forças, e tudo o que ele fez, e as cidades que ele construiu, não estão escritos no livro das crônicas dos reis de Judá? Mas na época de sua velhice ele estava doente em seus pés.
24 Sai Asa ya huta tare da kakanninsa, aka kuma binne shi tare da su a birnin kakansa Dawuda. Sai Yehoshafat ɗansa ya gāje shi a matsayin sarki.
Asa dormiu com seus pais, e foi enterrado com seus pais na cidade de seu pai David; e Jehoshaphat seu filho reinou em seu lugar.
25 Nadab ɗan Yerobowam ya zama sarkin Isra’ila a shekara ta biyu ta Asa sarkin Yahuda, ya kuma yi mulki a bisa Isra’ila shekara biyu.
Nadab, filho de Jeroboão, começou a reinar sobre Israel no segundo ano de Asa, rei de Judá; e reinou sobre Israel dois anos.
26 Ya yi mugunta a gaban Ubangiji, yana tafiya a hanyoyin mahaifinsa da kuma cikin zunubinsa, wanda ya sa Isra’ila suka yi.
Ele fez o que era mau aos olhos de Iavé, e caminhou no caminho de seu pai, e em seu pecado com o qual ele fez Israel pecar.
27 Ba’asha ɗan Ahiya na gidan Issakar ya yi maƙarƙashiya gāba da shi, ya buge shi a Gibbeton, a wani garin Filistiyawa, yayinda Nadab da dukan Isra’ila suke wa garin kwanto.
Baasa, filho de Ahijah, da casa de Issachar, conspirou contra ele; e Baasa golpeou-o em Gibeton, que pertencia aos filisteus; pois Nadabe e todo Israel estavam sitiando Gibeton.
28 Ba’asha ya kashe Nadab a shekara ta uku ta Asa sarkin Yahuda, ya kuma gāje shi a matsayin sarki.
Even no terceiro ano de Asa, rei de Judá, Baasa o matou e reinou em seu lugar.
29 Nan da nan da ya fara mulki, sai ya kashe dukan iyalin Yerobowam. Bai bar wa Yerobowam wani da rai ba, amma ya hallaka su duka, bisa ga maganar Ubangiji da ya ba wa bawansa Ahiya, mutumin Shilo.
Assim que ele foi rei, ele atingiu toda a casa de Jeroboão. Ele não deixou para Jeroboão ninguém que respirasse, até que o tivesse destruído, segundo o ditado de Javé, que ele falou por seu servo Ahijah, o silonita;
30 Wannan abu ya faru saboda zunuban da Yerobowam ya yi, ya kuma sa Isra’ila ya yi, kuma saboda ya tsokane Ubangiji, Allah na Isra’ila, ya yi fushi.
pelos pecados de Jeroboão que ele pecou, e com os quais ele fez Israel pecar, por causa de sua provocação com a qual ele provocou Javé, o Deus de Israel, à ira.
31 Game da sauran ayyukan mulkin Nadab da kuma dukan abin da ya yi, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Isra’ila.
Agora o resto dos atos de Nadab, e tudo o que ele fez, não estão escritos no livro das crônicas dos reis de Israel?
32 Aka yi yaƙi tsakanin Asa da Ba’asha sarkin Isra’ila dukan kwanakin mulkinsu.
Houve guerra entre Asa e Baasa, rei de Israel, durante todos os seus dias.
33 A shekara ta uku ta Asa sarkin Yahuda, Ba’asha ɗan Ahiya ya zama sarkin dukan Isra’ila a Tirza, ya kuma yi sarauta shekara ashirin da huɗu.
No terceiro ano de Asa, rei de Judá, Baasa, filho de Ahijah, começou a reinar sobre todo Israel em Tirzah durante vinte e quatro anos.
34 Ya aikata mugunta a gaban Ubangiji, yana tafiya a hanyoyin Yerobowam da kuma cikin zunubinsa, wanda ya sa Isra’ila suka yi.
Ele fez o que era mau aos olhos de Javé, e caminhou no caminho de Jeroboão, e em seu pecado com o qual ele fez Israel pecar.

< 1 Sarakuna 15 >