< 1 Sarakuna 15 >
1 A shekara ta goma sha takwas ta mulkin Yerobowam ɗan Nebat, Abiyam ya zama sarkin Yahuda,
Ngomnyaka wetshumi lesificaminwembili wenkosi uJerobhowamu indodana kaNebati uAbhiyamu wasesiba yinkosi phezu kukaJuda.
2 ya kuma yi mulki a Urushalima shekara uku. Sunan mahaifiyarsa Ma’aka ne,’yar Abisalom.
Wabusa iminyaka emithathu eJerusalema. Lebizo likanina lalinguMahaka indodakazi kaAbishalomu.
3 Shi ma ya aikata dukan irin zunubai da tsohonsa ya yi. Zuciyarsa ba tă bi Ubangiji Allahnsa, kamar yadda zuciyar Dawuda kakansa ta yi ba.
Wasehamba ezonweni zonke zikayise ayezenze phambi kwakhe, lenhliziyo yakhe yayingaphelelanga kuJehova uNkulunkulu wakhe, njengenhliziyo kaDavida uyise.
4 Duk da haka, saboda Dawuda Ubangiji Allahnsa ya ba shi fitila a Urushalima ta wurin ta da wani da ya gāje shi, ta wurinsa kuma Urushalima ta yi ƙarfi.
Kodwa ngenxa kaDavida iNkosi uNkulunkulu wakhe yamnika isibane eJerusalema, ngokubeka indodana yakhe emva kwakhe, langokuqinisa iJerusalema.
5 Gama Dawuda ya yi abin da yake daidai a gaban Ubangiji, bai kuma fasa kiyaye wani daga umarnan Ubangiji ba dukan kwanakinsa, sai dai a batun Uriya mutumin Hitti.
Ngoba uDavida wenza okulungileyo emehlweni eNkosi, kaphambukanga kukho konke eyamlaya khona insuku zonke zempilo yakhe, ngaphandle kwedabeni lukaUriya umHethi.
6 Aka yi yaƙi tsakanin Rehobowam da Yerobowam a duk kwanakin Abiya.
Kwakukhona-ke impi phakathi kukaRehobhowamu loJerobhowamu zonke izinsuku zempilo yakhe.
7 Game da sauran ayyukan mulkin Abiyam kuwa, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Yahuda. Aka yi yaƙi tsakanin Abiyam da Yerobowam.
Ezinye-ke zezindaba zikaAbhiyamu, lakho konke akwenzayo, kakubhalwanga yini egwalweni lwemilando yamakhosi akoJuda? Njalo kwaba lempi phakathi kukaAbhiyamu loJerobhowamu.
8 Sai Abiyam ya huta tare da kakanninsa, aka kuma binne shi a Birnin Dawuda. Asa kuwa ya gāje shi a matsayin sarki.
UAbhiyamu waselala laboyise, bamngcwabela emzini kaDavida. UAsa indodana yakhe wasesiba yinkosi esikhundleni sakhe.
9 A shekara ta ashirin ta Yerobowam sarkin Isra’ila, Asa ya zama sarkin Yahuda,
Ngomnyaka wamatshumi amabili kaJerobhowamu inkosi yakoIsrayeli uAsa wasesiba yinkosi yakoJuda.
10 ya yi mulki a Urushalima shekara arba’in da ɗaya. Sunan mahaifiya mahaifiyarsa, Ma’aka ne’yar Abisalom.
Wasebusa iminyaka engamatshumi amane lanye eJerusalema. Lebizo likanina lalinguMahaka indodakazi kaAbishalomu.
11 Asa ya yi abin da yake daidai a gaban Ubangiji, kamar yadda kakansa Dawuda ya yi.
UAsa wasesenza okulungileyo emehlweni eNkosi njengoDavida uyise.
12 Ya kori dukan maza karuwai na masujadai daga ƙasar, ya kuma yi waje da dukan gumakan da mahaifinsa ya yi.
Wasusa izinkotshana elizweni, wasusa zonke izithombe oyise ababezenzile.
13 Ya tuɓe mahaifiya mahaifiyarsa Ma’aka daga matsayinta na mahaifiyar sarauniya, gama ta gina ƙazantaccen ginshiƙin Ashera. Asa ya yanke ginshiƙin, ya kuma ƙone shi a Kwarin Kidron.
Laye-ke uMahaka unina wamsusa ekubeni yindlovukazi, ngoba wayenze into enengekayo ibe yiAshera; uAsa waseyigamula into yakhe enengekayo, wayitshisela esifuleni iKidroni.
14 Ko da yake bai cire masujadai da suke kan tuddai ba, zuciyar Asa ta kasance da aminci ɗungum ga Ubangiji dukan kwanakinsa.
Kanti indawo eziphakemeyo kazisuswanga; lanxa kunjalo inhliziyo kaAsa yayiphelele kuJehova insuku zakhe zonke.
15 Ya kawo azurfa da zinariya da kayayyakin da shi da mahaifinsa suka keɓe a haikalin Ubangiji.
Wasengenisa izinto ezehlukanisiweyo zikayise kanye lezakhe izinto ezehlukanisiweyo endlini yeNkosi, isiliva legolide lezitsha.
16 Aka yi yaƙi tsakanin Asa da Ba’asha sarkin Isra’ila dukan kwanakin mulkinsu.
Kwakukhona-ke impi phakathi kukaAsa loBahasha inkosi yakoIsrayeli zonke izinsuku zabo.
17 Ba’asha sarkin Isra’ila ya haura, ya yi yaƙi da Yahuda, ya kuma gina Rama don yă hana wani daga fita ko shiga yankin Asa, sarkin Yahuda.
UBahasha inkosi yakoIsrayeli wasesenyuka wamelana loJuda, wakha iRama, ukuze angavumeli muntu ukuphuma lokungena kuAsa inkosi yakoJuda.
18 Sai Asa ya ɗauki dukan azurfa da kuma zinariyar da suka rage a ma’ajin haikalin Ubangiji da kuma nasa fadan, ya ba da su ga wani shugabansa, ya kuma aika da su zuwa ga Ben-Hadad ɗan Tabrimmon, ɗan Heziyon, sarkin Aram, wanda yake mulki a Damaskus.
UAsa wasethatha sonke isiliva legolide okwakusele emagugwini endlu kaJehova lamagugu endlu yenkosi, wakunikela esandleni senceku zakhe; inkosi uAsa yakuthumela kuBenihadadi indodana kaTabirimoni indodana kaHeziyoni, inkosi yeSiriya, owayehlala eDamaseko, esithi:
19 Ya ce, “Bari yarjejjeniya ta kasance tsakanina da kai, kamar yadda ta kasance tsakanin mahaifina da mahaifinka. Duba, ina aika maka kyautai na azurfa da na zinariya. Yanzu fa sai ka janye yarjejjeniyarka da Ba’asha sarkin Isra’ila, don yă janye daga gare ni.”
Kulesivumelwano phakathi kwami lawe, phakathi kukababa loyihlo; khangela, ngikuthumezela isipho, isiliva legolide. Hamba, yephula isivumelwano sakho loBahasha inkosi yakoIsrayeli, ukuze enyuke asuke kimi.
20 Ben-Hadad ya yarda da maganar Sarki Asa, ya kuma aika shugabannin sojojin mayaƙansa ya yi yaƙi da garuruwan Isra’ila. Ya kame Iyon, Dan, Abel-Bet-Ma’aka da dukan Kinneret, haɗe da Naftali.
UBenihadadi waseyilalela inkosi uAsa, wathuma induna zamabutho ayelawo emelene lemizi yakoIsrayeli, watshaya iIjoni leDani leAbeli-Beti-Mahaka layo yonke iKinerothi lelizwe lonke lakoNafithali.
21 Da Ba’asha ya ji haka, sai ya daina ginin Rama, ya janye zuwa Tirza.
Kwasekusithi uBahasha ekuzwa wayekela ukwakha iRama, wahlala eTiriza.
22 Sai Sarki Asa ya ba da umarni ga dukan Yahuda, kuma babu wanda aka ware, kowa yă taimaka a kwashe duwatsu da katakan da Ba’asha yake amfani da su daga Rama. Da duwatsu da katakan ne Sarki Asa ya gina Geba a Benyamin da kuma Mizfa.
Inkosi uAsa yasisenza isimemezelo kuyo yonke iJuda; kakho owayetshiywe ngaphandle; ukuze basuse amatshe eRama lezigodo zayo, uBahasha ayesakha ngakho. Inkosi uAsa wasesakha ngakho iGeba yakoBhenjamini leMizipa.
23 Game da sauran ayyukan mulkin Asa, dukan nasarorinsa, dukan abin da ya yi, da kuma biranen da ya gina, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Yahuda. A tsufansa, sai ƙafafunsa suka kamu da cuta.
Ezinye-ke zazo zonke indaba zikaAsa, lawo wonke amandla akhe, lakho konke akwenzayo, lemizi ayakhayo, kakubhalwanga yini egwalweni lwemilando yamakhosi akoJuda? Kodwa esikhathini sobudala bakhe wayelomkhuhlane ezinyaweni.
24 Sai Asa ya huta tare da kakanninsa, aka kuma binne shi tare da su a birnin kakansa Dawuda. Sai Yehoshafat ɗansa ya gāje shi a matsayin sarki.
UAsa waselala laboyise, wangcwatshelwa kuboyise emzini kaDavida uyise. UJehoshafathi indodana yakhe wasesiba yinkosi esikhundleni sakhe.
25 Nadab ɗan Yerobowam ya zama sarkin Isra’ila a shekara ta biyu ta Asa sarkin Yahuda, ya kuma yi mulki a bisa Isra’ila shekara biyu.
UNadabi indodana kaJerobhowamu wasesiba yinkosi phezu kukaIsrayeli ngomnyaka wesibili kaAsa inkosi yakoJuda; wabusa phezu kukaIsrayeli iminyaka emibili.
26 Ya yi mugunta a gaban Ubangiji, yana tafiya a hanyoyin mahaifinsa da kuma cikin zunubinsa, wanda ya sa Isra’ila suka yi.
Wasesenza okubi emehlweni eNkosi, wahamba ngendlela kayise, lesonweni sakhe, enza uIsrayeli one ngaso.
27 Ba’asha ɗan Ahiya na gidan Issakar ya yi maƙarƙashiya gāba da shi, ya buge shi a Gibbeton, a wani garin Filistiyawa, yayinda Nadab da dukan Isra’ila suke wa garin kwanto.
UBahasha indodana kaAhiya, owendlu kaIsakari, wasemenzela ugobe; uBahasha wamtshaya eGibethoni engeyamaFilisti, lapho uNadabi loIsrayeli wonke bevimbezele iGibethoni.
28 Ba’asha ya kashe Nadab a shekara ta uku ta Asa sarkin Yahuda, ya kuma gāje shi a matsayin sarki.
UBahasha wambulala-ke ngomnyaka wesithathu kaAsa inkosi yakoJuda, wasesiba yinkosi esikhundleni sakhe.
29 Nan da nan da ya fara mulki, sai ya kashe dukan iyalin Yerobowam. Bai bar wa Yerobowam wani da rai ba, amma ya hallaka su duka, bisa ga maganar Ubangiji da ya ba wa bawansa Ahiya, mutumin Shilo.
Kwasekusithi ekubuseni kwakhe watshaya yonke indlu kaJerobhowamu, katshiyanga loyedwa ophefumulayo kuJerobhowamu, waze wamqeda, njengelizwi leNkosi eyalikhuluma ngesandla senceku yayo uAhiya umShilo.
30 Wannan abu ya faru saboda zunuban da Yerobowam ya yi, ya kuma sa Isra’ila ya yi, kuma saboda ya tsokane Ubangiji, Allah na Isra’ila, ya yi fushi.
Ngenxa yezono zikaJerobhowamu azonayo, lowenza uIsrayeli azone, ngentukuthelo yakhe athukuthelisa ngayo iNkosi, uNkulunkulu kaIsrayeli.
31 Game da sauran ayyukan mulkin Nadab da kuma dukan abin da ya yi, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Isra’ila.
Ezinye-ke zezindaba zikaNadabi, lakho konke akwenzayo, kakubhalwanga yini egwalweni lwemilando yamakhosi akoIsrayeli?
32 Aka yi yaƙi tsakanin Asa da Ba’asha sarkin Isra’ila dukan kwanakin mulkinsu.
Njalo kwakulempi phakathi kukaAsa loBahasha inkosi yakoIsrayeli insuku zabo zonke.
33 A shekara ta uku ta Asa sarkin Yahuda, Ba’asha ɗan Ahiya ya zama sarkin dukan Isra’ila a Tirza, ya kuma yi sarauta shekara ashirin da huɗu.
Ngomnyaka wesithathu kaAsa inkosi yakoJuda uBahasha indodana kaAhiya waba yinkosi phezu kukaIsrayeli wonke eTiriza; iminyaka engamatshumi amabili lane.
34 Ya aikata mugunta a gaban Ubangiji, yana tafiya a hanyoyin Yerobowam da kuma cikin zunubinsa, wanda ya sa Isra’ila suka yi.
Wasesenza okubi emehlweni eNkosi, wahamba ngendlela kaJerobhowamu, lesonweni sakhe, enza uIsrayeli one ngaso.