< 1 Sarakuna 15 >

1 A shekara ta goma sha takwas ta mulkin Yerobowam ɗan Nebat, Abiyam ya zama sarkin Yahuda,
Ainsi en la dix-huitième année du règne de Jéroboam, fils de Nabath, Abiam régna sur Juda.
2 ya kuma yi mulki a Urushalima shekara uku. Sunan mahaifiyarsa Ma’aka ne,’yar Abisalom.
Il régna trois ans dans Jérusalem; le nom de sa mère était Maacha, fille d’Abessalom.
3 Shi ma ya aikata dukan irin zunubai da tsohonsa ya yi. Zuciyarsa ba tă bi Ubangiji Allahnsa, kamar yadda zuciyar Dawuda kakansa ta yi ba.
Et il marcha dans tous les péchés que son père avait commis avant lui, et son cœur n’était point parfait avec le Seigneur son Dieu, comme le cœur de David son père.
4 Duk da haka, saboda Dawuda Ubangiji Allahnsa ya ba shi fitila a Urushalima ta wurin ta da wani da ya gāje shi, ta wurinsa kuma Urushalima ta yi ƙarfi.
Mais, à cause de David, le Seigneur son Dieu lui donna une lampe dans Jérusalem, en sorte qu’il suscita son fils après lui, et maintint Jérusalem,
5 Gama Dawuda ya yi abin da yake daidai a gaban Ubangiji, bai kuma fasa kiyaye wani daga umarnan Ubangiji ba dukan kwanakinsa, sai dai a batun Uriya mutumin Hitti.
Parce que David avait fait ce qui était droit aux yeux du Seigneur, et qu’il ne s’était point détourné de tout ce qu’il lui avait commandé, durant tous les jours de sa vie, excepté le fait touchant Urie, l’Héthéen.
6 Aka yi yaƙi tsakanin Rehobowam da Yerobowam a duk kwanakin Abiya.
Cependant il y eut guerre entre Roboam et Jéroboam, pendant tout le temps de la vie de Roboam.
7 Game da sauran ayyukan mulkin Abiyam kuwa, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Yahuda. Aka yi yaƙi tsakanin Abiyam da Yerobowam.
Mais le reste des actions d’Abiam, et tout ce qu’il fit, n’est-ce pas écrit dans le Livre des actions des jours des rois de Juda? Et il y eut une bataille entre Abiam et Jéroboam.
8 Sai Abiyam ya huta tare da kakanninsa, aka kuma binne shi a Birnin Dawuda. Asa kuwa ya gāje shi a matsayin sarki.
Et Abiam dormit avec ses pères, et on l’ensevelit dans la cité de David; et son fils Asa régna en sa place.
9 A shekara ta ashirin ta Yerobowam sarkin Isra’ila, Asa ya zama sarkin Yahuda,
Ainsi en la vingtième année de Jéroboam, roi d’Israël, Asa, roi de Juda, régna.
10 ya yi mulki a Urushalima shekara arba’in da ɗaya. Sunan mahaifiya mahaifiyarsa, Ma’aka ne’yar Abisalom.
Et il régna quarante-un ans dans Jérusalem. Le nom de sa mère était Maacha, fille d’Abessalom.
11 Asa ya yi abin da yake daidai a gaban Ubangiji, kamar yadda kakansa Dawuda ya yi.
Et Asa fit ce qui était droit en la présence du Seigneur, comme David son père;
12 Ya kori dukan maza karuwai na masujadai daga ƙasar, ya kuma yi waje da dukan gumakan da mahaifinsa ya yi.
Et il chassa les efféminés du pays, et le purifia de toutes les souillures des idoles que ses pères avaient fabriquées.
13 Ya tuɓe mahaifiya mahaifiyarsa Ma’aka daga matsayinta na mahaifiyar sarauniya, gama ta gina ƙazantaccen ginshiƙin Ashera. Asa ya yanke ginshiƙin, ya kuma ƙone shi a Kwarin Kidron.
De plus, il éloigna même sa mère Maacha, afin qu’elle ne fût pas préposée aux sacrifices de Priape, et à son bois sacré qu’elle avait consacré; et il renversa sa caverne, et il brisa le simulacre très obscène, et le brûla dans le torrent de Cédron.
14 Ko da yake bai cire masujadai da suke kan tuddai ba, zuciyar Asa ta kasance da aminci ɗungum ga Ubangiji dukan kwanakinsa.
Mais il ne détruisit pas les hauts lieux. Toutefois le cœur d’Asa fut parfait avec le Seigneur durant tous ses jours;
15 Ya kawo azurfa da zinariya da kayayyakin da shi da mahaifinsa suka keɓe a haikalin Ubangiji.
Il porta aussi ce qu’avait consacré son père, et qu’il avait voué dans la maison du Seigneur, de l’argent, de l’or, et des vases.
16 Aka yi yaƙi tsakanin Asa da Ba’asha sarkin Isra’ila dukan kwanakin mulkinsu.
Or il y eut guerre entre Asa et Baasa, roi d’Israël, durant tous leurs jours.
17 Ba’asha sarkin Isra’ila ya haura, ya yi yaƙi da Yahuda, ya kuma gina Rama don yă hana wani daga fita ko shiga yankin Asa, sarkin Yahuda.
Et Baasa, roi d’Israël, vint contre Juda et bâtit Rama, afin que personne ne pût sortir ou entrer du côté d’Asa, roi de Juda.
18 Sai Asa ya ɗauki dukan azurfa da kuma zinariyar da suka rage a ma’ajin haikalin Ubangiji da kuma nasa fadan, ya ba da su ga wani shugabansa, ya kuma aika da su zuwa ga Ben-Hadad ɗan Tabrimmon, ɗan Heziyon, sarkin Aram, wanda yake mulki a Damaskus.
C’est pourquoi Asa, prenant tout l’argent et l’or qui étaient demeurés dans les trésors de la maison du Seigneur et dans les trésors de la maison du roi, les mit entre les mains de ses serviteurs, et les envoya à Bénadad, fils de Tabremon, fils d’Hézion, roi de Syrie, qui habitait à Damas, disant:
19 Ya ce, “Bari yarjejjeniya ta kasance tsakanina da kai, kamar yadda ta kasance tsakanin mahaifina da mahaifinka. Duba, ina aika maka kyautai na azurfa da na zinariya. Yanzu fa sai ka janye yarjejjeniyarka da Ba’asha sarkin Isra’ila, don yă janye daga gare ni.”
Il y a alliance entre moi et vous, et entre mon père et votre père: c’est pourquoi je vous ai envoyé des présents, de l’argent et de l’or, et je vous prie de venir, et de rendre vaine l’alliance que vous avez avec Baasa, roi d’Israël, afin qu’il se retire loin de moi.
20 Ben-Hadad ya yarda da maganar Sarki Asa, ya kuma aika shugabannin sojojin mayaƙansa ya yi yaƙi da garuruwan Isra’ila. Ya kame Iyon, Dan, Abel-Bet-Ma’aka da dukan Kinneret, haɗe da Naftali.
Bénadad, écoutant le roi Asa, envoya les princes de son armée contre les villes d’Israël, et ils prirent d’assaut Ahion, Dan, Abel maison de Maacha, et Cennéroth tout entière, c’est-à-dire toute la terre de Nephthali.
21 Da Ba’asha ya ji haka, sai ya daina ginin Rama, ya janye zuwa Tirza.
Ce qu’ayant appris, Baasa cessa de bâtir Rama, et revint à Thersa.
22 Sai Sarki Asa ya ba da umarni ga dukan Yahuda, kuma babu wanda aka ware, kowa yă taimaka a kwashe duwatsu da katakan da Ba’asha yake amfani da su daga Rama. Da duwatsu da katakan ne Sarki Asa ya gina Geba a Benyamin da kuma Mizfa.
Or le roi Asa envoya un messager dans tout Juda, disant: Que personne ne soit exempté. Et on emporta les pierres de Rama et les bois avec lesquels Baasa avait bâti, et le roi Asa en construisit Gabaa en Benjamin, et Maspha.
23 Game da sauran ayyukan mulkin Asa, dukan nasarorinsa, dukan abin da ya yi, da kuma biranen da ya gina, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Yahuda. A tsufansa, sai ƙafafunsa suka kamu da cuta.
, Mais le reste de toutes les actions d’Asa, tous ses traits de courage, tout ce qu’il fit, et les villes qu’il bâtit, n’est-ce pas écrit dans le Livre des actions des jours des rois de Juda? Cependant dans le temps de sa vieillesse, il souffrit de ses pieds;
24 Sai Asa ya huta tare da kakanninsa, aka kuma binne shi tare da su a birnin kakansa Dawuda. Sai Yehoshafat ɗansa ya gāje shi a matsayin sarki.
Et il dormit avec ses pères, et il fut enseveli avec eux dans la cité de David son père. Et Josaphat, son fils, régna eu sa place.
25 Nadab ɗan Yerobowam ya zama sarkin Isra’ila a shekara ta biyu ta Asa sarkin Yahuda, ya kuma yi mulki a bisa Isra’ila shekara biyu.
Or Nadab, fils de Jéroboam, régna sur Israël la seconde année d’Asa, roi de Juda; et il régna deux ans sur Israël.
26 Ya yi mugunta a gaban Ubangiji, yana tafiya a hanyoyin mahaifinsa da kuma cikin zunubinsa, wanda ya sa Isra’ila suka yi.
Et il fit ce qui est mal en la présence du Seigneur, et il marcha dans les voies de son père et dans les péchés par lesquels il fit pécher Israël.
27 Ba’asha ɗan Ahiya na gidan Issakar ya yi maƙarƙashiya gāba da shi, ya buge shi a Gibbeton, a wani garin Filistiyawa, yayinda Nadab da dukan Isra’ila suke wa garin kwanto.
Mais Baasa, fils d’Ahias, de la maison d’Issachar, lui tendit des embûches et le tua près de Gebbethon, qui est une ville des Philistins; vu que Nadab et tout Israël assiégeaient Gebbethon.
28 Ba’asha ya kashe Nadab a shekara ta uku ta Asa sarkin Yahuda, ya kuma gāje shi a matsayin sarki.
Baasa tua donc Nadab, et il régna en sa place, la troisième année d’Asa, roi de Juda.
29 Nan da nan da ya fara mulki, sai ya kashe dukan iyalin Yerobowam. Bai bar wa Yerobowam wani da rai ba, amma ya hallaka su duka, bisa ga maganar Ubangiji da ya ba wa bawansa Ahiya, mutumin Shilo.
Et lorsque Baasa fut devenu roi, il tua toute la maison de Jéroboam: il n’en laissa pas même une seule âme de sa race, jusqu’à ce qu’il l’eût exterminée, selon la parole que le Seigneur avait dite par l’entremise de son serviteur Ahias, le Silonite,
30 Wannan abu ya faru saboda zunuban da Yerobowam ya yi, ya kuma sa Isra’ila ya yi, kuma saboda ya tsokane Ubangiji, Allah na Isra’ila, ya yi fushi.
À cause des péchés que Jéroboam avait commis et par lesquels il avait fait pécher Israël, et à cause du péché par lequel il avait irrité le Seigneur Dieu d’Israël.
31 Game da sauran ayyukan mulkin Nadab da kuma dukan abin da ya yi, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Isra’ila.
Mais le reste des actions de Nadab, et tout ce qu’il fit, n’est-ce pas écrit dans le Livre des actions des jours des rois d’Israël?
32 Aka yi yaƙi tsakanin Asa da Ba’asha sarkin Isra’ila dukan kwanakin mulkinsu.
Et il y eut guerre entre Asa et Baasa, roi d’Israël, durant tous leurs jours.
33 A shekara ta uku ta Asa sarkin Yahuda, Ba’asha ɗan Ahiya ya zama sarkin dukan Isra’ila a Tirza, ya kuma yi sarauta shekara ashirin da huɗu.
La troisième année d’Asa, roi de Juda, Baasa, fils d’Ahias, régna sur tout Israël à Thersa pendant vingt-quatre ans.
34 Ya aikata mugunta a gaban Ubangiji, yana tafiya a hanyoyin Yerobowam da kuma cikin zunubinsa, wanda ya sa Isra’ila suka yi.
Et il fit le mal devant le Seigneur, et il marcha dans la voie de Jéroboam et dans les péchés par lesquels il avait fait pécher Israël.

< 1 Sarakuna 15 >