< 1 Sarakuna 15 >

1 A shekara ta goma sha takwas ta mulkin Yerobowam ɗan Nebat, Abiyam ya zama sarkin Yahuda,
La dix-huitième année du roi Jéroboam, fils de Nébat, Abijam commença à régner sur Juda.
2 ya kuma yi mulki a Urushalima shekara uku. Sunan mahaifiyarsa Ma’aka ne,’yar Abisalom.
Il régna trois ans à Jérusalem. Sa mère s'appelait Maaca, et était fille d'Abishalom.
3 Shi ma ya aikata dukan irin zunubai da tsohonsa ya yi. Zuciyarsa ba tă bi Ubangiji Allahnsa, kamar yadda zuciyar Dawuda kakansa ta yi ba.
Il marcha dans tous les péchés que son père avait commis avant lui; et son cœur ne fut point intègre envers l'Éternel son Dieu, comme le cœur de David, son père.
4 Duk da haka, saboda Dawuda Ubangiji Allahnsa ya ba shi fitila a Urushalima ta wurin ta da wani da ya gāje shi, ta wurinsa kuma Urushalima ta yi ƙarfi.
Mais, pour l'amour de David, l'Éternel son Dieu lui donna une lampe dans Jérusalem, suscitant son fils après lui et laissant subsister Jérusalem;
5 Gama Dawuda ya yi abin da yake daidai a gaban Ubangiji, bai kuma fasa kiyaye wani daga umarnan Ubangiji ba dukan kwanakinsa, sai dai a batun Uriya mutumin Hitti.
Parce que David avait fait ce qui est droit devant l'Éternel, et que, pendant toute sa vie, il ne s'était point détourné de tout ce qu'il lui avait commandé, excepté dans l'affaire d'Urie, le Héthien.
6 Aka yi yaƙi tsakanin Rehobowam da Yerobowam a duk kwanakin Abiya.
Et il y avait eu guerre entre Roboam et Jéroboam, tout le temps de leur vie.
7 Game da sauran ayyukan mulkin Abiyam kuwa, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Yahuda. Aka yi yaƙi tsakanin Abiyam da Yerobowam.
Le reste des actions d'Abijam et tout ce qu'il fit, cela n'est-il pas écrit au livre des Chroniques des rois de Juda? Il y eut aussi guerre entre Abijam et Jéroboam.
8 Sai Abiyam ya huta tare da kakanninsa, aka kuma binne shi a Birnin Dawuda. Asa kuwa ya gāje shi a matsayin sarki.
Et Abijam s'endormit avec ses pères, et on l'ensevelit dans la cité de David; et Asa, son fils, régna à sa place.
9 A shekara ta ashirin ta Yerobowam sarkin Isra’ila, Asa ya zama sarkin Yahuda,
La vingtième année de Jéroboam, roi d'Israël, Asa commença à régner sur Juda;
10 ya yi mulki a Urushalima shekara arba’in da ɗaya. Sunan mahaifiya mahaifiyarsa, Ma’aka ne’yar Abisalom.
Et il régna quarante et un ans à Jérusalem. Sa mère s'appelait Maaca, et elle était fille d'Abishalom.
11 Asa ya yi abin da yake daidai a gaban Ubangiji, kamar yadda kakansa Dawuda ya yi.
Et Asa fit ce qui est droit aux yeux de l'Éternel, comme David, son père.
12 Ya kori dukan maza karuwai na masujadai daga ƙasar, ya kuma yi waje da dukan gumakan da mahaifinsa ya yi.
Il chassa du pays les prostitués, et il ôta toutes les idoles que ses pères avaient faites.
13 Ya tuɓe mahaifiya mahaifiyarsa Ma’aka daga matsayinta na mahaifiyar sarauniya, gama ta gina ƙazantaccen ginshiƙin Ashera. Asa ya yanke ginshiƙin, ya kuma ƙone shi a Kwarin Kidron.
Et même il destitua de son rang sa mère, Maaca, qui avait fait une idole pour Ashéra. Et Asa abattit son idole et la brûla au torrent de Cédron.
14 Ko da yake bai cire masujadai da suke kan tuddai ba, zuciyar Asa ta kasance da aminci ɗungum ga Ubangiji dukan kwanakinsa.
Les hauts lieux ne furent point ôtés; néanmoins, le cœur d'Asa fut intègre envers l'Éternel tout le long de ses jours,
15 Ya kawo azurfa da zinariya da kayayyakin da shi da mahaifinsa suka keɓe a haikalin Ubangiji.
Et il remit dans la maison de l'Éternel les choses qui avaient été consacrées par son père, avec ce qu'il lui avait aussi consacré, l'argent, l'or et les ustensiles.
16 Aka yi yaƙi tsakanin Asa da Ba’asha sarkin Isra’ila dukan kwanakin mulkinsu.
Or il y eut guerre entre Asa et Baesha, roi d'Israël, tout le temps de leur vie.
17 Ba’asha sarkin Isra’ila ya haura, ya yi yaƙi da Yahuda, ya kuma gina Rama don yă hana wani daga fita ko shiga yankin Asa, sarkin Yahuda.
Et Baesha, roi d'Israël, monta contre Juda, et il bâtit Rama, afin de ne laisser sortir ni entrer aucun homme pour Asa, roi de Juda.
18 Sai Asa ya ɗauki dukan azurfa da kuma zinariyar da suka rage a ma’ajin haikalin Ubangiji da kuma nasa fadan, ya ba da su ga wani shugabansa, ya kuma aika da su zuwa ga Ben-Hadad ɗan Tabrimmon, ɗan Heziyon, sarkin Aram, wanda yake mulki a Damaskus.
Alors Asa prit tout l'argent et l'or demeuré dans les trésors de l'Éternel et les trésors de la maison royale, et les remit à ses serviteurs; et le roi Asa les envoya vers Ben-Hadad, fils de Tabrimon, fils de Hezjon, roi de Syrie, qui habitait à Damas, pour lui dire:
19 Ya ce, “Bari yarjejjeniya ta kasance tsakanina da kai, kamar yadda ta kasance tsakanin mahaifina da mahaifinka. Duba, ina aika maka kyautai na azurfa da na zinariya. Yanzu fa sai ka janye yarjejjeniyarka da Ba’asha sarkin Isra’ila, don yă janye daga gare ni.”
Il y a alliance entre moi et toi, comme entre mon père et ton père; voici je t'envoie un présent en argent et en or; va, romps ton alliance avec Baesha, roi d'Israël, afin qu'il se retire de moi.
20 Ben-Hadad ya yarda da maganar Sarki Asa, ya kuma aika shugabannin sojojin mayaƙansa ya yi yaƙi da garuruwan Isra’ila. Ya kame Iyon, Dan, Abel-Bet-Ma’aka da dukan Kinneret, haɗe da Naftali.
Et Ben-Hadad écouta le roi Asa, et il envoya les capitaines de ses armées contre les villes d'Israël; et il frappa Ijjon, Dan, Abel-Beth-Maaca et tout Kinnéroth, avec tout le pays de Nephthali.
21 Da Ba’asha ya ji haka, sai ya daina ginin Rama, ya janye zuwa Tirza.
Et aussitôt que Baesha l'eut appris, il cessa de bâtir Rama; et il resta à Thirtsa.
22 Sai Sarki Asa ya ba da umarni ga dukan Yahuda, kuma babu wanda aka ware, kowa yă taimaka a kwashe duwatsu da katakan da Ba’asha yake amfani da su daga Rama. Da duwatsu da katakan ne Sarki Asa ya gina Geba a Benyamin da kuma Mizfa.
Alors le roi Asa fit publier par tout Juda, que tous, sans exempter personne, eussent à emporter les pierres et le bois de Rama, que Baesha faisait bâtir; et le roi Asa en bâtit Guéba de Benjamin, et Mitspa.
23 Game da sauran ayyukan mulkin Asa, dukan nasarorinsa, dukan abin da ya yi, da kuma biranen da ya gina, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Yahuda. A tsufansa, sai ƙafafunsa suka kamu da cuta.
Quant à tout le reste des actions d'Asa et tous ses exploits, et tout ce qu'il fit, et les villes qu'il bâtit, cela n'est-il pas écrit au livre des Chroniques des rois de Juda? Seulement, au temps de sa vieillesse, il fut malade des pieds.
24 Sai Asa ya huta tare da kakanninsa, aka kuma binne shi tare da su a birnin kakansa Dawuda. Sai Yehoshafat ɗansa ya gāje shi a matsayin sarki.
Et Asa s'endormit avec ses pères, et il fut enseveli avec eux dans la cité de David, son père; et Josaphat, son fils, régna à sa place.
25 Nadab ɗan Yerobowam ya zama sarkin Isra’ila a shekara ta biyu ta Asa sarkin Yahuda, ya kuma yi mulki a bisa Isra’ila shekara biyu.
Nadab, fils de Jéroboam, avait commencé à régner sur Israël la seconde année d'Asa, roi de Juda, et il régna deux ans sur Israël.
26 Ya yi mugunta a gaban Ubangiji, yana tafiya a hanyoyin mahaifinsa da kuma cikin zunubinsa, wanda ya sa Isra’ila suka yi.
Il fit ce qui est mal aux yeux de l'Éternel; et il marcha dans la voie de son père et dans le péché par lequel il avait fait pécher Israël.
27 Ba’asha ɗan Ahiya na gidan Issakar ya yi maƙarƙashiya gāba da shi, ya buge shi a Gibbeton, a wani garin Filistiyawa, yayinda Nadab da dukan Isra’ila suke wa garin kwanto.
Et Baesha, fils d'Achija, de la maison d'Issacar, conspira contre lui, et le frappa à Guibbéthon qui est aux Philistins, lorsque Nadab et tout Israël assiégeaient Guibbéthon.
28 Ba’asha ya kashe Nadab a shekara ta uku ta Asa sarkin Yahuda, ya kuma gāje shi a matsayin sarki.
Baesha le fit donc mourir, la troisième année d'Asa, roi de Juda; et il régna à sa place.
29 Nan da nan da ya fara mulki, sai ya kashe dukan iyalin Yerobowam. Bai bar wa Yerobowam wani da rai ba, amma ya hallaka su duka, bisa ga maganar Ubangiji da ya ba wa bawansa Ahiya, mutumin Shilo.
Et dès qu'il fut roi, il frappa toute la maison de Jéroboam; et il ne laissa à Jéroboam aucune âme vivante qu'il n'exterminât, selon la parole que l'Éternel avait prononcée par son serviteur Achija, de Silo,
30 Wannan abu ya faru saboda zunuban da Yerobowam ya yi, ya kuma sa Isra’ila ya yi, kuma saboda ya tsokane Ubangiji, Allah na Isra’ila, ya yi fushi.
A cause des péchés que Jéroboam avait commis et fait commettre à Israël, en provoquant l'Éternel, le Dieu d'Israël.
31 Game da sauran ayyukan mulkin Nadab da kuma dukan abin da ya yi, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Isra’ila.
Le reste des actions de Nadab, et tout ce qu'il fit, cela n'est-il pas écrit au livre des Chroniques des rois d'Israël?
32 Aka yi yaƙi tsakanin Asa da Ba’asha sarkin Isra’ila dukan kwanakin mulkinsu.
Or, il y eut guerre entre Asa et Baesha, roi d'Israël, tout le temps de leur vie.
33 A shekara ta uku ta Asa sarkin Yahuda, Ba’asha ɗan Ahiya ya zama sarkin dukan Isra’ila a Tirza, ya kuma yi sarauta shekara ashirin da huɗu.
La troisième année d'Asa, roi de Juda, Baesha, fils d'Achija, commença à régner sur tout Israël, à Thirtsa; il régna vingt-quatre ans.
34 Ya aikata mugunta a gaban Ubangiji, yana tafiya a hanyoyin Yerobowam da kuma cikin zunubinsa, wanda ya sa Isra’ila suka yi.
Il fit ce qui est mal aux yeux de l'Éternel; et il marcha dans la voie de Jéroboam et dans le péché par lequel il avait fait pécher Israël.

< 1 Sarakuna 15 >