< 1 Sarakuna 15 >
1 A shekara ta goma sha takwas ta mulkin Yerobowam ɗan Nebat, Abiyam ya zama sarkin Yahuda,
En la dix-huitième année du règne de Jéroboam, fils de Nabat, Abiam, fils de Roboam, devint roi de Juda.
2 ya kuma yi mulki a Urushalima shekara uku. Sunan mahaifiyarsa Ma’aka ne,’yar Abisalom.
Et il régna trois ans à Jérusalem; sa mère, fille d'Absalon, se nommait Maacha.
3 Shi ma ya aikata dukan irin zunubai da tsohonsa ya yi. Zuciyarsa ba tă bi Ubangiji Allahnsa, kamar yadda zuciyar Dawuda kakansa ta yi ba.
Et il marcha dans les péchés que son père avait faits devant lui, et son cœur ne fut point parfait avec le Seigneur son Dieu, comme l'était le cœur de son père David.
4 Duk da haka, saboda Dawuda Ubangiji Allahnsa ya ba shi fitila a Urushalima ta wurin ta da wani da ya gāje shi, ta wurinsa kuma Urushalima ta yi ƙarfi.
Mais, à cause de David, le Seigneur lui donna un rejeton, afin de maintenir ses enfants après lui, et d'affermir Jérusalem;
5 Gama Dawuda ya yi abin da yake daidai a gaban Ubangiji, bai kuma fasa kiyaye wani daga umarnan Ubangiji ba dukan kwanakinsa, sai dai a batun Uriya mutumin Hitti.
Parce que David avait fait ce qui est droit devant le Seigneur, et que, pendant toute sa vie, il ne s'était jamais écarté des commandements.
6 Aka yi yaƙi tsakanin Rehobowam da Yerobowam a duk kwanakin Abiya.
7 Game da sauran ayyukan mulkin Abiyam kuwa, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Yahuda. Aka yi yaƙi tsakanin Abiyam da Yerobowam.
Quant au reste de l'histoire d'Abiam, n'est-il pas écrit au livre des Faits et gestes des rois de Juda? Et la guerre ne cessa pas entre Abiam et Jéroboam.
8 Sai Abiyam ya huta tare da kakanninsa, aka kuma binne shi a Birnin Dawuda. Asa kuwa ya gāje shi a matsayin sarki.
Et Abiam s'endormit avec ses pères, en la vingt-quatrième année du règne de Jéroboam; il fut enseveli auprès de ses pères en la ville de David; et son fils Asa régna à sa place.
9 A shekara ta ashirin ta Yerobowam sarkin Isra’ila, Asa ya zama sarkin Yahuda,
Dans la vingt-quatrième année du règne de Jéroboam, roi d'Israël, Asa devint roi de Juda.
10 ya yi mulki a Urushalima shekara arba’in da ɗaya. Sunan mahaifiya mahaifiyarsa, Ma’aka ne’yar Abisalom.
Il régna quarante et un ans à Jérusalem; sa mère, fille d'Absalon, se nommait Ana.
11 Asa ya yi abin da yake daidai a gaban Ubangiji, kamar yadda kakansa Dawuda ya yi.
Et Asa fit ce qui était droit devant le Seigneur, comme son père David.
12 Ya kori dukan maza karuwai na masujadai daga ƙasar, ya kuma yi waje da dukan gumakan da mahaifinsa ya yi.
Et il détruisit, dans la terre promise, les initiations, et il abolit les infâmes pratiques qu'avaient adoptées ses pères.
13 Ya tuɓe mahaifiya mahaifiyarsa Ma’aka daga matsayinta na mahaifiyar sarauniya, gama ta gina ƙazantaccen ginshiƙin Ashera. Asa ya yanke ginshiƙin, ya kuma ƙone shi a Kwarin Kidron.
Il expulsa Ana, sa mère, pour qu'elle ne fût plus rien, parce qu'elle réunissait une association d'initiés dans son bois sacré, et il abattit ses refuges, et il les livra aux flammes dans la vallée de Cédron.
14 Ko da yake bai cire masujadai da suke kan tuddai ba, zuciyar Asa ta kasance da aminci ɗungum ga Ubangiji dukan kwanakinsa.
Mais il ne détruisit pas les hauts lieux; néanmoins, le cœur d'Asa fut parfait avec Dieu tout le temps qu'il vécut.
15 Ya kawo azurfa da zinariya da kayayyakin da shi da mahaifinsa suka keɓe a haikalin Ubangiji.
Et il transporta les colonnes de son père; il transporta dans le temple du Seigneur ses colonnes d'or et d'argent, et ses vases.
16 Aka yi yaƙi tsakanin Asa da Ba’asha sarkin Isra’ila dukan kwanakin mulkinsu.
Et la guerre ne cessa point entre Asa et Baasa, roi d'Israël, tout le temps de leur vie.
17 Ba’asha sarkin Isra’ila ya haura, ya yi yaƙi da Yahuda, ya kuma gina Rama don yă hana wani daga fita ko shiga yankin Asa, sarkin Yahuda.
Baasa, roi d'Israël, marcha contre Juda, et il se mit à bâtir Rhama, pour qu'il n'y eût personne qui pût sortir ni rentrer, en faveur du roi Asa.
18 Sai Asa ya ɗauki dukan azurfa da kuma zinariyar da suka rage a ma’ajin haikalin Ubangiji da kuma nasa fadan, ya ba da su ga wani shugabansa, ya kuma aika da su zuwa ga Ben-Hadad ɗan Tabrimmon, ɗan Heziyon, sarkin Aram, wanda yake mulki a Damaskus.
Asa, alors, prit tout l'argent et tout l'or qui se trouva dans les trésors du temple et du palais; il les confia à ses serviteurs, et il les envoya chez le fils d'Ader, fils de Tabremon, fils d'Esion, roi de Syrie, qui résidait à Damas, disant:
19 Ya ce, “Bari yarjejjeniya ta kasance tsakanina da kai, kamar yadda ta kasance tsakanin mahaifina da mahaifinka. Duba, ina aika maka kyautai na azurfa da na zinariya. Yanzu fa sai ka janye yarjejjeniyarka da Ba’asha sarkin Isra’ila, don yă janye daga gare ni.”
Fais alliance entre moi et toi, entre la maison de mon père et la maison de ton père; voilà que je t'ai envoyé des présents: de l'argent et de l'or; viens, romps ton alliance avec Baasa, roi d'Israël, et il s'éloignera de moi.
20 Ben-Hadad ya yarda da maganar Sarki Asa, ya kuma aika shugabannin sojojin mayaƙansa ya yi yaƙi da garuruwan Isra’ila. Ya kame Iyon, Dan, Abel-Bet-Ma’aka da dukan Kinneret, haɗe da Naftali.
Et Ben-Ader écouta le roi Asa; il fit partir les chefs de ses armées contre les villes d'Israël; ils dévastèrent Ahion, Dan, Abel de la maison de Maacha, et tout Cennereth jusqu'aux confins de Nephthali.
21 Da Ba’asha ya ji haka, sai ya daina ginin Rama, ya janye zuwa Tirza.
Quand Baasa l'apprit, il abandonna les constructions de Rhama, et il retourna à Thersa.
22 Sai Sarki Asa ya ba da umarni ga dukan Yahuda, kuma babu wanda aka ware, kowa yă taimaka a kwashe duwatsu da katakan da Ba’asha yake amfani da su daga Rama. Da duwatsu da katakan ne Sarki Asa ya gina Geba a Benyamin da kuma Mizfa.
Et le roi Asa, dans Enacim, donna ses ordres à tout Juda, ils enlevèrent les pierres de Rhama, et les bois que Baasa avait employés pour la bâtir. Ensuite, le roi s'en servit pour fortifier toutes les collines de Benjamin, et pour y établir la tour du guet.
23 Game da sauran ayyukan mulkin Asa, dukan nasarorinsa, dukan abin da ya yi, da kuma biranen da ya gina, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Yahuda. A tsufansa, sai ƙafafunsa suka kamu da cuta.
Quant au reste de l'histoire d'Asa, à toutes les actions qu'il fit en sa puissance, à toutes les villes qu'il bâtit, ne sont-ils pas inscrits au livre des Faits et gestes des rois de Juda? Toutefois, dans sa vieillesse, il, perdit l'usage de ses pieds.
24 Sai Asa ya huta tare da kakanninsa, aka kuma binne shi tare da su a birnin kakansa Dawuda. Sai Yehoshafat ɗansa ya gāje shi a matsayin sarki.
Et Asa s'endormit avec ses pères; il fut enseveli auprès d'eux en la ville de David, son aïeul. Et Josaphat, son fils, régna à sa place.
25 Nadab ɗan Yerobowam ya zama sarkin Isra’ila a shekara ta biyu ta Asa sarkin Yahuda, ya kuma yi mulki a bisa Isra’ila shekara biyu.
Nabat, fils de Jéroboam, devint roi d'Israël dans la seconde année du règne d'Asa en Juda, et Nabat régna deux ans.
26 Ya yi mugunta a gaban Ubangiji, yana tafiya a hanyoyin mahaifinsa da kuma cikin zunubinsa, wanda ya sa Isra’ila suka yi.
Et il fit le mai devant le Seigneur; il marcha dans la voie de son père, et dans les péchés où il avait fait tomber Israël.
27 Ba’asha ɗan Ahiya na gidan Issakar ya yi maƙarƙashiya gāba da shi, ya buge shi a Gibbeton, a wani garin Filistiyawa, yayinda Nadab da dukan Isra’ila suke wa garin kwanto.
Et Baasa, fils d'Achias, l'assiégea à la tète de la maison de Bélaan, fils d'Achias; il l'entoura de palissades à Gabathon, ville des Philistins, que Nabat et tout Israël avaient investie.
28 Ba’asha ya kashe Nadab a shekara ta uku ta Asa sarkin Yahuda, ya kuma gāje shi a matsayin sarki.
Et Baasa le tua, la troisième année du règne d'Asa en Juda, et il régna à sa place.
29 Nan da nan da ya fara mulki, sai ya kashe dukan iyalin Yerobowam. Bai bar wa Yerobowam wani da rai ba, amma ya hallaka su duka, bisa ga maganar Ubangiji da ya ba wa bawansa Ahiya, mutumin Shilo.
Dès qu'il fut proclamé, il extermina toute la maison de Jéroboam; nul de ceux des siens, qui avait souffle de vie, ne fut épargné, jusqu'à ce que tout eût péri, selon la parole que le Seigneur avait dite par la voix de son serviteur Achias le Silonite,
30 Wannan abu ya faru saboda zunuban da Yerobowam ya yi, ya kuma sa Isra’ila ya yi, kuma saboda ya tsokane Ubangiji, Allah na Isra’ila, ya yi fushi.
Concernant les péchés de Jéroboam, et le péché où il avait fait tomber Israël pour irriter le Seigneur Dieu d'Israël.
31 Game da sauran ayyukan mulkin Nadab da kuma dukan abin da ya yi, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Isra’ila.
Quant au reste de l'histoire de Nabat, n'est-il pas écrit au livre des Faits et gestes des rois d'Israël?
32 Aka yi yaƙi tsakanin Asa da Ba’asha sarkin Isra’ila dukan kwanakin mulkinsu.
En la troisième année du règne d'Asa en Juda, Baasa, fils d'Achias, fut proclamé roi d'Israël, et il régna vingt-quatre ans à Thersa.
33 A shekara ta uku ta Asa sarkin Yahuda, Ba’asha ɗan Ahiya ya zama sarkin dukan Isra’ila a Tirza, ya kuma yi sarauta shekara ashirin da huɗu.
En la troisième année du règne d'Asa en Juda, Baasa, fils d'Achias, fut proclamé roi d'Israël, et il régna vingt-quatre ans à Thersa.
34 Ya aikata mugunta a gaban Ubangiji, yana tafiya a hanyoyin Yerobowam da kuma cikin zunubinsa, wanda ya sa Isra’ila suka yi.
Et il fit le mal devant le Seigneur; il marcha dans la voie de Jéroboam, fils de Nabat, et dans les péchés où il avait fait tomber Israël.