< 1 Sarakuna 15 >

1 A shekara ta goma sha takwas ta mulkin Yerobowam ɗan Nebat, Abiyam ya zama sarkin Yahuda,
C’Est dans la dix-huitième année du règne de Jéroboam, fils de Nebat, qu’Abiam devint roi de Juda.
2 ya kuma yi mulki a Urushalima shekara uku. Sunan mahaifiyarsa Ma’aka ne,’yar Abisalom.
Il régna trois ans à Jérusalem. Sa mère se nommait Maakha, fille d’Abichalom.
3 Shi ma ya aikata dukan irin zunubai da tsohonsa ya yi. Zuciyarsa ba tă bi Ubangiji Allahnsa, kamar yadda zuciyar Dawuda kakansa ta yi ba.
Il se rendit coupable de tous les péchés que son père avait commis avant lui, et son cœur n’appartint pas sans partage à l’Eternel, son Dieu, comme le cœur de son aïeul David.
4 Duk da haka, saboda Dawuda Ubangiji Allahnsa ya ba shi fitila a Urushalima ta wurin ta da wani da ya gāje shi, ta wurinsa kuma Urushalima ta yi ƙarfi.
Car, c’est en faveur de David que l’Eternel, son Dieu, lui avait accordé un domaine en Jérusalem, voulant conserver son descendant après lui et assurer la durée de Jérusalem;
5 Gama Dawuda ya yi abin da yake daidai a gaban Ubangiji, bai kuma fasa kiyaye wani daga umarnan Ubangiji ba dukan kwanakinsa, sai dai a batun Uriya mutumin Hitti.
parce que David avait fait ce qui est droit aux yeux de l’Eternel et n’avait contrevenu, toute sa vie, à aucune de ses prescriptions, à part l’affaire d’Urie, le Héthéen.
6 Aka yi yaƙi tsakanin Rehobowam da Yerobowam a duk kwanakin Abiya.
Il y eut guerre entre Roboam et Jéroboam tout le temps de sa vie.
7 Game da sauran ayyukan mulkin Abiyam kuwa, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Yahuda. Aka yi yaƙi tsakanin Abiyam da Yerobowam.
Pour le surplus des faits et gestes d’Abiam, ils sont mentionnés dans le livre des annales des rois de Juda, ainsi que la guerre entre Abiam et Jéroboam.
8 Sai Abiyam ya huta tare da kakanninsa, aka kuma binne shi a Birnin Dawuda. Asa kuwa ya gāje shi a matsayin sarki.
Abiam reposa avec ses pères, et fut enseveli dans la Cité de David. Asa, son fils, lui succéda.
9 A shekara ta ashirin ta Yerobowam sarkin Isra’ila, Asa ya zama sarkin Yahuda,
C’Est dans la vingtième année du règne de Jéroboam sur Israël qu’Asa devint roi de Juda.
10 ya yi mulki a Urushalima shekara arba’in da ɗaya. Sunan mahaifiya mahaifiyarsa, Ma’aka ne’yar Abisalom.
Il régna quarante et un ans à Jérusalem. Le nom de sa mère était Maakha, fille d’Abichalom.
11 Asa ya yi abin da yake daidai a gaban Ubangiji, kamar yadda kakansa Dawuda ya yi.
Asa fit ce qui est agréable au Seigneur, à l’exemple de son aïeul David.
12 Ya kori dukan maza karuwai na masujadai daga ƙasar, ya kuma yi waje da dukan gumakan da mahaifinsa ya yi.
Il fit disparaître du pays ceux qui se prostituaient, et il en éloigna toutes les impures idoles faites par ses pères.
13 Ya tuɓe mahaifiya mahaifiyarsa Ma’aka daga matsayinta na mahaifiyar sarauniya, gama ta gina ƙazantaccen ginshiƙin Ashera. Asa ya yanke ginshiƙin, ya kuma ƙone shi a Kwarin Kidron.
Il destitua même de la régence sa mère Maakha, qui avait consacré une image à Achéra; par l’ordre d’Asa, cette image fut abattue et brûlée dans la vallée de Cédron.
14 Ko da yake bai cire masujadai da suke kan tuddai ba, zuciyar Asa ta kasance da aminci ɗungum ga Ubangiji dukan kwanakinsa.
Toutefois, les hauts-lieux ne disparurent point; mais le cœur d’Asa resta fidèle à l’Eternel, son Dieu, toute sa vie.
15 Ya kawo azurfa da zinariya da kayayyakin da shi da mahaifinsa suka keɓe a haikalin Ubangiji.
Il fit porter dans la maison du Seigneur ce que son père et lui-même avaient consacré en fait d’argent, d’or et de vases précieux.
16 Aka yi yaƙi tsakanin Asa da Ba’asha sarkin Isra’ila dukan kwanakin mulkinsu.
Il y eut guerre entre lui et Baasa, roi d’Israël, toute leur vie.
17 Ba’asha sarkin Isra’ila ya haura, ya yi yaƙi da Yahuda, ya kuma gina Rama don yă hana wani daga fita ko shiga yankin Asa, sarkin Yahuda.
Baasa, roi d’Israël, étant venu attaquer Juda, fortifia Rama pour ne pas laisser l’entrée libre à Asa, roi de Juda.
18 Sai Asa ya ɗauki dukan azurfa da kuma zinariyar da suka rage a ma’ajin haikalin Ubangiji da kuma nasa fadan, ya ba da su ga wani shugabansa, ya kuma aika da su zuwa ga Ben-Hadad ɗan Tabrimmon, ɗan Heziyon, sarkin Aram, wanda yake mulki a Damaskus.
Alors Asa prit tout l’argent et l’or qui restaient dans les trésors du temple, joints aux trésors de la maison du roi, les remit à ses serviteurs et les envoya à Ben-Hadad, fils de Tabrimmôn, fils de Hezyôn, roi de Syrie, résidant à Damas, avec ces paroles:
19 Ya ce, “Bari yarjejjeniya ta kasance tsakanina da kai, kamar yadda ta kasance tsakanin mahaifina da mahaifinka. Duba, ina aika maka kyautai na azurfa da na zinariya. Yanzu fa sai ka janye yarjejjeniyarka da Ba’asha sarkin Isra’ila, don yă janye daga gare ni.”
"Toi et moi soyons alliés, comme mon père fut allié du tien. Je t’envoie un cadeau d’argent et d’or, afin que tu rompes ton alliance avec Baasa, roi d’Israël, et qu’il se retire de chez moi."
20 Ben-Hadad ya yarda da maganar Sarki Asa, ya kuma aika shugabannin sojojin mayaƙansa ya yi yaƙi da garuruwan Isra’ila. Ya kame Iyon, Dan, Abel-Bet-Ma’aka da dukan Kinneret, haɗe da Naftali.
Ben-Hadad, accédant à la demande d’Asa, envoya ses généraux contre les villes d’Israël, et prit de vive force Iyyôn, Dan, Abel-Beth-Maakha, toute la région de Kinnerot avec tout le territoire de Nephtali.
21 Da Ba’asha ya ji haka, sai ya daina ginin Rama, ya janye zuwa Tirza.
Lorsque Baasa en fut informé, il renonça à fortifier Rama et s’établit à Tirça.
22 Sai Sarki Asa ya ba da umarni ga dukan Yahuda, kuma babu wanda aka ware, kowa yă taimaka a kwashe duwatsu da katakan da Ba’asha yake amfani da su daga Rama. Da duwatsu da katakan ne Sarki Asa ya gina Geba a Benyamin da kuma Mizfa.
Le roi Asa convoqua alors tous les gens de Juda, sans dispenser personne; et ils enlevèrent les pierres et le bois employés par Baasa aux travaux de Rama; Asa s’en servit pour fortifier Ghéba-en-Benjamin et Miçpa.
23 Game da sauran ayyukan mulkin Asa, dukan nasarorinsa, dukan abin da ya yi, da kuma biranen da ya gina, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Yahuda. A tsufansa, sai ƙafafunsa suka kamu da cuta.
Pour le surplus de l’histoire d’Asa, ses exploits et ses travaux, et les villes qu’il a bâties, tous ces faits sont consignés dans le livre des annales des rois de Juda; il est à noter seulement que, dans sa vieillesse, il eut les pieds malades.
24 Sai Asa ya huta tare da kakanninsa, aka kuma binne shi tare da su a birnin kakansa Dawuda. Sai Yehoshafat ɗansa ya gāje shi a matsayin sarki.
Asa s’endormit avec ses pères et fut inhumé auprès d’eux dans la Cité de David, son aïeul. Josaphat, son fils, régna à sa place.
25 Nadab ɗan Yerobowam ya zama sarkin Isra’ila a shekara ta biyu ta Asa sarkin Yahuda, ya kuma yi mulki a bisa Isra’ila shekara biyu.
Nadab, fils de Jéroboam, devint roi d’Israël la seconde année du règne d’Asa, roi de Juda, et régna deux ans sur Israël.
26 Ya yi mugunta a gaban Ubangiji, yana tafiya a hanyoyin mahaifinsa da kuma cikin zunubinsa, wanda ya sa Isra’ila suka yi.
Il fit ce qui déplaît à l’Eternel, imitant la conduite de son père et les péchés qu’il avait fait commettre à Israël.
27 Ba’asha ɗan Ahiya na gidan Issakar ya yi maƙarƙashiya gāba da shi, ya buge shi a Gibbeton, a wani garin Filistiyawa, yayinda Nadab da dukan Isra’ila suke wa garin kwanto.
Baasa, fils d’Ahiyya, de la maison d’Issachar, conspira contre lui et le fit périr à Ghibetôn, ville des Philistins, tandis que Nadab et tout Israël assiégeaient cette ville.
28 Ba’asha ya kashe Nadab a shekara ta uku ta Asa sarkin Yahuda, ya kuma gāje shi a matsayin sarki.
C’Est la troisième année du règne d’Asa, roi de Juda, que Baasa tua Nadab, à qui il succéda.
29 Nan da nan da ya fara mulki, sai ya kashe dukan iyalin Yerobowam. Bai bar wa Yerobowam wani da rai ba, amma ya hallaka su duka, bisa ga maganar Ubangiji da ya ba wa bawansa Ahiya, mutumin Shilo.
Devenu roi, il extermina toute la famille de Jéroboam, n’en épargnant pas une âme, jusqu’à ce qu’il l’eût anéantie, ainsi que le Seigneur l’avait annoncé par l’organe de son serviteur Ahiyya, de Silo,
30 Wannan abu ya faru saboda zunuban da Yerobowam ya yi, ya kuma sa Isra’ila ya yi, kuma saboda ya tsokane Ubangiji, Allah na Isra’ila, ya yi fushi.
à cause des péchés que Jéroboam avait commis et fait commettre à Israël, provoquant ainsi la colère du Seigneur, Dieu d’Israël.
31 Game da sauran ayyukan mulkin Nadab da kuma dukan abin da ya yi, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Isra’ila.
Quant au reste de l’histoire et des actes de Nadab, ils sont consignés dans le livre des annales des rois d’Israël.
32 Aka yi yaƙi tsakanin Asa da Ba’asha sarkin Isra’ila dukan kwanakin mulkinsu.
Il y eut guerre entre Asa et Baasa, toute leur vie.
33 A shekara ta uku ta Asa sarkin Yahuda, Ba’asha ɗan Ahiya ya zama sarkin dukan Isra’ila a Tirza, ya kuma yi sarauta shekara ashirin da huɗu.
C’Est dans la troisième année d’Asa, roi de Juda, que Baasa, fils d’Ahiyya, devint roi de tout Israël; il résida à Tirça et régna vingt-quatre ans.
34 Ya aikata mugunta a gaban Ubangiji, yana tafiya a hanyoyin Yerobowam da kuma cikin zunubinsa, wanda ya sa Isra’ila suka yi.
Il fit ce qui déplaît au Seigneur, imitant la conduite de Jéroboam et les péchés qu’il avait fait commettre à Israël.

< 1 Sarakuna 15 >