< 1 Sarakuna 15 >
1 A shekara ta goma sha takwas ta mulkin Yerobowam ɗan Nebat, Abiyam ya zama sarkin Yahuda,
Now in the eighteenth year of king Jerobo'am the son of Nebat became Abiyam king over Judah.
2 ya kuma yi mulki a Urushalima shekara uku. Sunan mahaifiyarsa Ma’aka ne,’yar Abisalom.
Three years he reigned in Jerusalem. And his mother's name was Ma'achah, the daughter of Abishalom.
3 Shi ma ya aikata dukan irin zunubai da tsohonsa ya yi. Zuciyarsa ba tă bi Ubangiji Allahnsa, kamar yadda zuciyar Dawuda kakansa ta yi ba.
And he walked in all the sins of his father, which he had done before him; and his heart was not entire with the Lord his God, like the heart of David his father.
4 Duk da haka, saboda Dawuda Ubangiji Allahnsa ya ba shi fitila a Urushalima ta wurin ta da wani da ya gāje shi, ta wurinsa kuma Urushalima ta yi ƙarfi.
Nevertheless for the sake of David did the Lord his God give him a rule in Jerusalem, to set up his son after him, and to allow Jerusalem to exist.
5 Gama Dawuda ya yi abin da yake daidai a gaban Ubangiji, bai kuma fasa kiyaye wani daga umarnan Ubangiji ba dukan kwanakinsa, sai dai a batun Uriya mutumin Hitti.
Because David did what is right in the eyes of the Lord, and turned not aside from all that he had commanded him all the days of his life, save only in the matter of Uriyah the Hittite.
6 Aka yi yaƙi tsakanin Rehobowam da Yerobowam a duk kwanakin Abiya.
And there had been war between Rehobo'am and Jerobo'am all the days of his life.
7 Game da sauran ayyukan mulkin Abiyam kuwa, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Yahuda. Aka yi yaƙi tsakanin Abiyam da Yerobowam.
And the rest of the acts of Abiyam, and all that he did, behold, they are written in the book of the chronicles of the kings of Judah. And there was [also] war between Abiyam and Jerobo'am.
8 Sai Abiyam ya huta tare da kakanninsa, aka kuma binne shi a Birnin Dawuda. Asa kuwa ya gāje shi a matsayin sarki.
And Abiyam slept with his fathers; and they buried him in the city of David: and Assa his son became king in his stead.
9 A shekara ta ashirin ta Yerobowam sarkin Isra’ila, Asa ya zama sarkin Yahuda,
And in the twentieth year of Jerobo'am the king of Israel became Assa king over Judah.
10 ya yi mulki a Urushalima shekara arba’in da ɗaya. Sunan mahaifiya mahaifiyarsa, Ma’aka ne’yar Abisalom.
And forty and one years did he reign in Jerusalem. And the name of his mother was Ma'achah, the daughter of Abishalom.
11 Asa ya yi abin da yake daidai a gaban Ubangiji, kamar yadda kakansa Dawuda ya yi.
And Assa did what is right in the eyes of the Lord, like David his father.
12 Ya kori dukan maza karuwai na masujadai daga ƙasar, ya kuma yi waje da dukan gumakan da mahaifinsa ya yi.
And he put away the sodomites out of the land, and removed all the idols which his fathers had made.
13 Ya tuɓe mahaifiya mahaifiyarsa Ma’aka daga matsayinta na mahaifiyar sarauniya, gama ta gina ƙazantaccen ginshiƙin Ashera. Asa ya yanke ginshiƙin, ya kuma ƙone shi a Kwarin Kidron.
And also Ma'achah his mother, even her he removed from being queen; because she had made a scandalous image for the grove; and Assa cut down her scandalous image, and burnt it by the brook Kidron.
14 Ko da yake bai cire masujadai da suke kan tuddai ba, zuciyar Asa ta kasance da aminci ɗungum ga Ubangiji dukan kwanakinsa.
But the high-places were not removed; nevertheless Assa's heart was entire with the Lord all his days.
15 Ya kawo azurfa da zinariya da kayayyakin da shi da mahaifinsa suka keɓe a haikalin Ubangiji.
And he brought the things which his father had sanctified, and his own sanctified things, into the house of the Lord, silver, and gold, and vessels.
16 Aka yi yaƙi tsakanin Asa da Ba’asha sarkin Isra’ila dukan kwanakin mulkinsu.
And there was war between Assa and Ba'sha the king of Israel all their days.
17 Ba’asha sarkin Isra’ila ya haura, ya yi yaƙi da Yahuda, ya kuma gina Rama don yă hana wani daga fita ko shiga yankin Asa, sarkin Yahuda.
And Ba'sha the king of Israel went up against Judah, and built Ramah, in order not to suffer any one to go out or come in to Assa the king of Judah.
18 Sai Asa ya ɗauki dukan azurfa da kuma zinariyar da suka rage a ma’ajin haikalin Ubangiji da kuma nasa fadan, ya ba da su ga wani shugabansa, ya kuma aika da su zuwa ga Ben-Hadad ɗan Tabrimmon, ɗan Heziyon, sarkin Aram, wanda yake mulki a Damaskus.
Then did Assa take all the silver and the gold that were left in the treasures of the house of the Lord, and the treasures of the king's house, and gave them into the hand of his servants; and king Assa sent them to Ben-hadad, the son of Tabrimmon, the son of Chesyon, the king of Syria, who dwelt in Damascus, saying,
19 Ya ce, “Bari yarjejjeniya ta kasance tsakanina da kai, kamar yadda ta kasance tsakanin mahaifina da mahaifinka. Duba, ina aika maka kyautai na azurfa da na zinariya. Yanzu fa sai ka janye yarjejjeniyarka da Ba’asha sarkin Isra’ila, don yă janye daga gare ni.”
A covenant is between me and thee, [as] between my father and thy father: behold, I have sent unto thee a present of silver and gold; go and do break thy covenant with Ba'sha the king of Israel, that he may withdraw from me.
20 Ben-Hadad ya yarda da maganar Sarki Asa, ya kuma aika shugabannin sojojin mayaƙansa ya yi yaƙi da garuruwan Isra’ila. Ya kame Iyon, Dan, Abel-Bet-Ma’aka da dukan Kinneret, haɗe da Naftali.
And Ben-hadad hearkened unto king Assa, and sent the captains of the armies which he had against the cities of Israel, and smote 'Iyon, and Dan, and Abel-beth-ma'achah, and the whole of Kinneroth, with all the land of Naphtali.
21 Da Ba’asha ya ji haka, sai ya daina ginin Rama, ya janye zuwa Tirza.
And it came to pass, when Ba'sha heard this, that he left off the building of Ramah, and remained in Tirzah.
22 Sai Sarki Asa ya ba da umarni ga dukan Yahuda, kuma babu wanda aka ware, kowa yă taimaka a kwashe duwatsu da katakan da Ba’asha yake amfani da su daga Rama. Da duwatsu da katakan ne Sarki Asa ya gina Geba a Benyamin da kuma Mizfa.
Then king Assa called together by proclamation all Judah, none being exempted: and they took away the stones of Ramah, and its timber, wherewith Ba'sha had built; and king Assa built with them Geba' of Benjamin, and Mizpah.
23 Game da sauran ayyukan mulkin Asa, dukan nasarorinsa, dukan abin da ya yi, da kuma biranen da ya gina, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Yahuda. A tsufansa, sai ƙafafunsa suka kamu da cuta.
And the rest of all the acts of Assa, and all his mighty deeds, and all that he did, and the cities which he built, behold, they are written in the book of the chronicles of the kings of Judah. Nevertheless in the time of his old age he became diseased in his feet.
24 Sai Asa ya huta tare da kakanninsa, aka kuma binne shi tare da su a birnin kakansa Dawuda. Sai Yehoshafat ɗansa ya gāje shi a matsayin sarki.
And Assa slept with his fathers, and was buried with his fathers in the city of David his father: and Jehoshaphat his son became king in his stead.
25 Nadab ɗan Yerobowam ya zama sarkin Isra’ila a shekara ta biyu ta Asa sarkin Yahuda, ya kuma yi mulki a bisa Isra’ila shekara biyu.
And Nadab the son of Jerobo'am became king over Israel in the second year of Assa the king of Judah; and he reigned over Israel two years.
26 Ya yi mugunta a gaban Ubangiji, yana tafiya a hanyoyin mahaifinsa da kuma cikin zunubinsa, wanda ya sa Isra’ila suka yi.
And he did what is evil in the eyes of the Lord, and he walked in the way of his father, and in his sin wherewith he had induced Israel to sin.
27 Ba’asha ɗan Ahiya na gidan Issakar ya yi maƙarƙashiya gāba da shi, ya buge shi a Gibbeton, a wani garin Filistiyawa, yayinda Nadab da dukan Isra’ila suke wa garin kwanto.
And Ba'sha the son of Achiyah, of the house of Issachar, conspired against him; and Ba'sha smote him at Gibbethon, which belonged to the Philistines: while Nadab and all Israel were besieging Gibbethon.
28 Ba’asha ya kashe Nadab a shekara ta uku ta Asa sarkin Yahuda, ya kuma gāje shi a matsayin sarki.
And Ba'sha slew him in the third year of Assa the king of Judah, and became king in his stead.
29 Nan da nan da ya fara mulki, sai ya kashe dukan iyalin Yerobowam. Bai bar wa Yerobowam wani da rai ba, amma ya hallaka su duka, bisa ga maganar Ubangiji da ya ba wa bawansa Ahiya, mutumin Shilo.
And it came to pass, when he reigned, that he smote all the house of Jerobo'am; he left not any that breathed unto Jerobo'am, until he had destroyed him, according to the word of the Lord, which he had spoken by his servant Achiyah the Shilonite;
30 Wannan abu ya faru saboda zunuban da Yerobowam ya yi, ya kuma sa Isra’ila ya yi, kuma saboda ya tsokane Ubangiji, Allah na Isra’ila, ya yi fushi.
Because of the sins of Jerobo'am which he had sinned, and through which he had induced Israel to sin, by his provoking wherewith he provoked the Lord the God of Israel to anger.
31 Game da sauran ayyukan mulkin Nadab da kuma dukan abin da ya yi, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Isra’ila.
And the rest of the acts of Nadab, and all that he did, behold, they are written in the book of the chronicles of the kings of Israel.
32 Aka yi yaƙi tsakanin Asa da Ba’asha sarkin Isra’ila dukan kwanakin mulkinsu.
And there was war between Assa and Ba'sha the king of Israel all their days.
33 A shekara ta uku ta Asa sarkin Yahuda, Ba’asha ɗan Ahiya ya zama sarkin dukan Isra’ila a Tirza, ya kuma yi sarauta shekara ashirin da huɗu.
In the third year of Assa the king of Judah became Ba'sha the son of Achiyah king over all Israel, in Thirzah, [for] twenty and four years.
34 Ya aikata mugunta a gaban Ubangiji, yana tafiya a hanyoyin Yerobowam da kuma cikin zunubinsa, wanda ya sa Isra’ila suka yi.
And he did what is evil in the eyes of the Lord, and walked in the way of Jerobo'am, and in his sin wherewith he had induced Israel to sin.