< 1 Sarakuna 15 >

1 A shekara ta goma sha takwas ta mulkin Yerobowam ɗan Nebat, Abiyam ya zama sarkin Yahuda,
Now in the eighteenth year of the reign of Jeroboam the son of Nabat, Abiam reigned over Juda.
2 ya kuma yi mulki a Urushalima shekara uku. Sunan mahaifiyarsa Ma’aka ne,’yar Abisalom.
He reigned three years in Jerusalem: the name of his mother was Maacha the daughter of Abessalom.
3 Shi ma ya aikata dukan irin zunubai da tsohonsa ya yi. Zuciyarsa ba tă bi Ubangiji Allahnsa, kamar yadda zuciyar Dawuda kakansa ta yi ba.
And he walked in all the sins of his father, which he had done before him: and his heart was not perfect with the Lord his God, as was the heart of David his father.
4 Duk da haka, saboda Dawuda Ubangiji Allahnsa ya ba shi fitila a Urushalima ta wurin ta da wani da ya gāje shi, ta wurinsa kuma Urushalima ta yi ƙarfi.
But for David’s sake the Lord his God gave him a lamp in Jerusalem, to set up his son after him, and to establish Jerusalem:
5 Gama Dawuda ya yi abin da yake daidai a gaban Ubangiji, bai kuma fasa kiyaye wani daga umarnan Ubangiji ba dukan kwanakinsa, sai dai a batun Uriya mutumin Hitti.
Because David had done that which was right in the eyes of the Lord, and had not turned aside from any thing that he commanded him, all the days of his life, except the matter of Urias the Hethite.
6 Aka yi yaƙi tsakanin Rehobowam da Yerobowam a duk kwanakin Abiya.
But there was war between Roboam and Jeroboam all the time of his life.
7 Game da sauran ayyukan mulkin Abiyam kuwa, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Yahuda. Aka yi yaƙi tsakanin Abiyam da Yerobowam.
And the rest of the words of Abiam, and all that he did, are they not written in the book of the words of the days of the kings of Juda? And there was war between Abiam and Jeroboam.
8 Sai Abiyam ya huta tare da kakanninsa, aka kuma binne shi a Birnin Dawuda. Asa kuwa ya gāje shi a matsayin sarki.
And Abiam slept with his fathers, and they buried him in the city of David, and Asa his son reigned in his stead.
9 A shekara ta ashirin ta Yerobowam sarkin Isra’ila, Asa ya zama sarkin Yahuda,
So in the twentieth year of Jeroboam king of Israel, reigned Asa king of Juda,
10 ya yi mulki a Urushalima shekara arba’in da ɗaya. Sunan mahaifiya mahaifiyarsa, Ma’aka ne’yar Abisalom.
And he reigned one and forty years in Jerusalem. His mother’s name was Maacha, the daughter of Abessalom.
11 Asa ya yi abin da yake daidai a gaban Ubangiji, kamar yadda kakansa Dawuda ya yi.
And Asa did that which was right in the sight of the Lord, as did David his father:
12 Ya kori dukan maza karuwai na masujadai daga ƙasar, ya kuma yi waje da dukan gumakan da mahaifinsa ya yi.
And he took away the effeminate out of the land, and he removed all the filth of the idols, which his fathers had made.
13 Ya tuɓe mahaifiya mahaifiyarsa Ma’aka daga matsayinta na mahaifiyar sarauniya, gama ta gina ƙazantaccen ginshiƙin Ashera. Asa ya yanke ginshiƙin, ya kuma ƙone shi a Kwarin Kidron.
Moreover he also removed his mother Maacha, from being the princess in the sacrifices of Priapus, and in the grove which she had consecrated to him: and he destroyed her den, and broke in pieces the filthy idol, and burnt it by the torrent Cedron:
14 Ko da yake bai cire masujadai da suke kan tuddai ba, zuciyar Asa ta kasance da aminci ɗungum ga Ubangiji dukan kwanakinsa.
But the high places he did not take away. Nevertheless the heart of Asa was perfect with the Lord all his days:
15 Ya kawo azurfa da zinariya da kayayyakin da shi da mahaifinsa suka keɓe a haikalin Ubangiji.
And he brought in the things which his father had dedicated, and he had vowed, into the house of the Lord, silver and gold, and vessels.
16 Aka yi yaƙi tsakanin Asa da Ba’asha sarkin Isra’ila dukan kwanakin mulkinsu.
And there was war between Asa, and Baasa king of Israel all their days.
17 Ba’asha sarkin Isra’ila ya haura, ya yi yaƙi da Yahuda, ya kuma gina Rama don yă hana wani daga fita ko shiga yankin Asa, sarkin Yahuda.
And Baasa king of Israel went up against Juda, and built Rama, that no man might go out or come in, of the side of Asa king of Juda.
18 Sai Asa ya ɗauki dukan azurfa da kuma zinariyar da suka rage a ma’ajin haikalin Ubangiji da kuma nasa fadan, ya ba da su ga wani shugabansa, ya kuma aika da su zuwa ga Ben-Hadad ɗan Tabrimmon, ɗan Heziyon, sarkin Aram, wanda yake mulki a Damaskus.
Then Asa took all the silver and gold that remained in the treasures of the house of the Lord, and in the treasures of the king’s house, and delivered it into the hands of his servants: and sent them to Benadad son of Tabremon the son of Hezion, king of Syria, who dwelt in Damascus, saying:
19 Ya ce, “Bari yarjejjeniya ta kasance tsakanina da kai, kamar yadda ta kasance tsakanin mahaifina da mahaifinka. Duba, ina aika maka kyautai na azurfa da na zinariya. Yanzu fa sai ka janye yarjejjeniyarka da Ba’asha sarkin Isra’ila, don yă janye daga gare ni.”
There is a league between me and thee, and between my father and thy father: therefore I have sent thee presents of silver and gold: and I desire thee to come, and break thy league with Baasa king of Israel, that he may depart from me.
20 Ben-Hadad ya yarda da maganar Sarki Asa, ya kuma aika shugabannin sojojin mayaƙansa ya yi yaƙi da garuruwan Isra’ila. Ya kame Iyon, Dan, Abel-Bet-Ma’aka da dukan Kinneret, haɗe da Naftali.
Benadad hearkening to king Asa, sent the captains of his army against the cities of Israel, and they smote Ahion, and Dan, and Abeldomum Maacha, and all Cenneroth, that is all the land of Nephtali.
21 Da Ba’asha ya ji haka, sai ya daina ginin Rama, ya janye zuwa Tirza.
And when Baasa had heard this, he left off building Rama, and returned into Thersa.
22 Sai Sarki Asa ya ba da umarni ga dukan Yahuda, kuma babu wanda aka ware, kowa yă taimaka a kwashe duwatsu da katakan da Ba’asha yake amfani da su daga Rama. Da duwatsu da katakan ne Sarki Asa ya gina Geba a Benyamin da kuma Mizfa.
But king Asa sent word into all Juda, saying: Let no man be excused: and they took away the stones from Rama, and the timber thereof wherewith Baasa had been building, and with them Asa built Gabaa of Benjamin, and Maspha.
23 Game da sauran ayyukan mulkin Asa, dukan nasarorinsa, dukan abin da ya yi, da kuma biranen da ya gina, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Yahuda. A tsufansa, sai ƙafafunsa suka kamu da cuta.
But the rest of all the acts of Asa, and all his strength, and all that he did and the cities that he built, are they not written in the book of the words of the days of the kings of Juda? But in the time of his old age he was diseased in his feet.
24 Sai Asa ya huta tare da kakanninsa, aka kuma binne shi tare da su a birnin kakansa Dawuda. Sai Yehoshafat ɗansa ya gāje shi a matsayin sarki.
And he slept with his fathers, and was buried with them in the city of David his father. And Josaphat his son reigned in his place.
25 Nadab ɗan Yerobowam ya zama sarkin Isra’ila a shekara ta biyu ta Asa sarkin Yahuda, ya kuma yi mulki a bisa Isra’ila shekara biyu.
But Nadab the son of Jeroboam reigned over Israel the second year of Asa king of Juda: and he reigned over Israel two years.
26 Ya yi mugunta a gaban Ubangiji, yana tafiya a hanyoyin mahaifinsa da kuma cikin zunubinsa, wanda ya sa Isra’ila suka yi.
And he did evil in the sight of the Lord, and walked in the ways of his father, and in his sins, wherewith he made Israel to sin.
27 Ba’asha ɗan Ahiya na gidan Issakar ya yi maƙarƙashiya gāba da shi, ya buge shi a Gibbeton, a wani garin Filistiyawa, yayinda Nadab da dukan Isra’ila suke wa garin kwanto.
And Baasa the son of Ahias of the house of Issachar, conspired against him, and slew him in Gebbethon, which is a city of the Philistines: for Nadab and all Israel besieged Gebbethon.
28 Ba’asha ya kashe Nadab a shekara ta uku ta Asa sarkin Yahuda, ya kuma gāje shi a matsayin sarki.
So Baasa slew him in the third year of Asa king of Juda, and reigned in his place.
29 Nan da nan da ya fara mulki, sai ya kashe dukan iyalin Yerobowam. Bai bar wa Yerobowam wani da rai ba, amma ya hallaka su duka, bisa ga maganar Ubangiji da ya ba wa bawansa Ahiya, mutumin Shilo.
And when he was king he cut off all the house of Jeroboam: he left not so much as one soul of his seed, till he had utterly destroyed him, according to the word of the Lord, which he had spoken in the hand of Ahias the Silonite:
30 Wannan abu ya faru saboda zunuban da Yerobowam ya yi, ya kuma sa Isra’ila ya yi, kuma saboda ya tsokane Ubangiji, Allah na Isra’ila, ya yi fushi.
Because of the sin of Jeroboam, which he had sinned, and wherewith he had made Israel to sin, and for the offence, wherewith he provoked the Lord the God of Israel.
31 Game da sauran ayyukan mulkin Nadab da kuma dukan abin da ya yi, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Isra’ila.
But the rest of the acts of Nadab, and all that he did, are they not written in the book of the words of the days of the kings of Israel?
32 Aka yi yaƙi tsakanin Asa da Ba’asha sarkin Isra’ila dukan kwanakin mulkinsu.
And there was war between Asa and Baasa the king of Israel all their days.
33 A shekara ta uku ta Asa sarkin Yahuda, Ba’asha ɗan Ahiya ya zama sarkin dukan Isra’ila a Tirza, ya kuma yi sarauta shekara ashirin da huɗu.
In the third year of Asa king of Juda, Baasa the son of Ahias reigned over all Israel, in Thersa, four and twenty years.
34 Ya aikata mugunta a gaban Ubangiji, yana tafiya a hanyoyin Yerobowam da kuma cikin zunubinsa, wanda ya sa Isra’ila suka yi.
And he did evil before the Lord, and walked in the ways of Jeroboam, and in his sins, wherewith he made Israel to sin.

< 1 Sarakuna 15 >