< 1 Sarakuna 15 >

1 A shekara ta goma sha takwas ta mulkin Yerobowam ɗan Nebat, Abiyam ya zama sarkin Yahuda,
Osamnaeste godine kraljevanja Jeroboama, sina Nebatova, zakraljio se Abijam u Judeji.
2 ya kuma yi mulki a Urushalima shekara uku. Sunan mahaifiyarsa Ma’aka ne,’yar Abisalom.
Tri je godine kraljevao u Jeruzalemu; njegova se majka zvala Maaka, a bila je kći Abšalomova.
3 Shi ma ya aikata dukan irin zunubai da tsohonsa ya yi. Zuciyarsa ba tă bi Ubangiji Allahnsa, kamar yadda zuciyar Dawuda kakansa ta yi ba.
On je hodio u svim grijesima što ih je njegov otac činio prije njega, i njegovo srce nije bilo potpuno odano Jahvi, Bogu svome, kao srce njegova praoca Davida.
4 Duk da haka, saboda Dawuda Ubangiji Allahnsa ya ba shi fitila a Urushalima ta wurin ta da wani da ya gāje shi, ta wurinsa kuma Urushalima ta yi ƙarfi.
Ipak, zbog Davida, dao mu je Jahve, Bog njegov, svjetiljku u Jeruzalemu, podigavši sinove njegove poslije njega i sačuvavši Jeruzalem.
5 Gama Dawuda ya yi abin da yake daidai a gaban Ubangiji, bai kuma fasa kiyaye wani daga umarnan Ubangiji ba dukan kwanakinsa, sai dai a batun Uriya mutumin Hitti.
Jer je David činio sve što je pravo u očima Jahvinim i za svega svoga života nije odstupio ni od čega što mu je zapovjedio, osim onog što je učinio Uriji Hetitu.
6 Aka yi yaƙi tsakanin Rehobowam da Yerobowam a duk kwanakin Abiya.
7 Game da sauran ayyukan mulkin Abiyam kuwa, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Yahuda. Aka yi yaƙi tsakanin Abiyam da Yerobowam.
Ostala povijest Abijamova, sve što je učinio, zar to nije zapisano u knjizi Ljetopisa kraljeva judejskih? A bijaše rat između Abijama i Jeroboama.
8 Sai Abiyam ya huta tare da kakanninsa, aka kuma binne shi a Birnin Dawuda. Asa kuwa ya gāje shi a matsayin sarki.
Potom je Abijam počinuo sa svojim ocima. Sahraniše ga u Davidovu gradu; na njegovo se mjesto zakralji sin mu Asa.
9 A shekara ta ashirin ta Yerobowam sarkin Isra’ila, Asa ya zama sarkin Yahuda,
Dvadesete godine Jeroboamova kraljevanja nad Izraelom postade Asa kraljem Judeje.
10 ya yi mulki a Urushalima shekara arba’in da ɗaya. Sunan mahaifiya mahaifiyarsa, Ma’aka ne’yar Abisalom.
Kraljevao je četrdeset i jednu godinu u Jeruzalemu; njegova se baka zvala Maaka, a bila je kći Abšalomova.
11 Asa ya yi abin da yake daidai a gaban Ubangiji, kamar yadda kakansa Dawuda ya yi.
Asa je činio što je pravo u očima Jahvinim, kao i njegov praotac David.
12 Ya kori dukan maza karuwai na masujadai daga ƙasar, ya kuma yi waje da dukan gumakan da mahaifinsa ya yi.
Protjerao je iz zemlje posvećene bludnice i uklonio sve idole koje njegovi oci bijahu načinili.
13 Ya tuɓe mahaifiya mahaifiyarsa Ma’aka daga matsayinta na mahaifiyar sarauniya, gama ta gina ƙazantaccen ginshiƙin Ashera. Asa ya yanke ginshiƙin, ya kuma ƙone shi a Kwarin Kidron.
Sam je uklonio svoju baku s dostojanstva velike kneginje, jer bijaše načinila gada Ašeri. Asa je sasjekao njezina gada i spalio ga u potoku Kidronu.
14 Ko da yake bai cire masujadai da suke kan tuddai ba, zuciyar Asa ta kasance da aminci ɗungum ga Ubangiji dukan kwanakinsa.
Ali uzvišice nisu bile uklonjene; ipak je Asino srce bilo privrženo Jahvi svega njegova života.
15 Ya kawo azurfa da zinariya da kayayyakin da shi da mahaifinsa suka keɓe a haikalin Ubangiji.
Unio je u Dom Jahvin posvećene darove svoga oca i svoje: srebro, zlato i posuđe.
16 Aka yi yaƙi tsakanin Asa da Ba’asha sarkin Isra’ila dukan kwanakin mulkinsu.
Bio je rat između Ase i Baše, kralja izraelskoga, u sve njihove dane.
17 Ba’asha sarkin Isra’ila ya haura, ya yi yaƙi da Yahuda, ya kuma gina Rama don yă hana wani daga fita ko shiga yankin Asa, sarkin Yahuda.
Izraelski kralj Baša navali na Judeju i stade utvrđivati Ramu da spriječi svako kretanje judejskom kralju Asi.
18 Sai Asa ya ɗauki dukan azurfa da kuma zinariyar da suka rage a ma’ajin haikalin Ubangiji da kuma nasa fadan, ya ba da su ga wani shugabansa, ya kuma aika da su zuwa ga Ben-Hadad ɗan Tabrimmon, ɗan Heziyon, sarkin Aram, wanda yake mulki a Damaskus.
Asa tada uze srebra i zlata koje je preostalo u riznicama Doma Jahvina i u riznicama kraljevskog dvora i dade ga svojim slugama te ih posla Ben-Hadadu, sinu Tabrimonovu, sinu Hezjonovu, aramejskom kralju, koji je stolovao u Damasku, i poruči mu:
19 Ya ce, “Bari yarjejjeniya ta kasance tsakanina da kai, kamar yadda ta kasance tsakanin mahaifina da mahaifinka. Duba, ina aika maka kyautai na azurfa da na zinariya. Yanzu fa sai ka janye yarjejjeniyarka da Ba’asha sarkin Isra’ila, don yă janye daga gare ni.”
“Neka bude savez između mene i tebe, između moga i tvoga oca; evo, šaljem ti na dar srebra i zlata: hajde, raskini savez s izraelskim kraljem Bašom da bi otišao od mene.”
20 Ben-Hadad ya yarda da maganar Sarki Asa, ya kuma aika shugabannin sojojin mayaƙansa ya yi yaƙi da garuruwan Isra’ila. Ya kame Iyon, Dan, Abel-Bet-Ma’aka da dukan Kinneret, haɗe da Naftali.
Ben-Hadad posluša kralja Asu i posla svoje vojskovođe na izraelske gradove te oni pokoriše Ijon, Dan, Abel Bet-Maaku, sav Kineret i svu zemlju Naftali.
21 Da Ba’asha ya ji haka, sai ya daina ginin Rama, ya janye zuwa Tirza.
A kada to Baša dozna, presta utvrđivati Ramu i vrati se u Tirsu.
22 Sai Sarki Asa ya ba da umarni ga dukan Yahuda, kuma babu wanda aka ware, kowa yă taimaka a kwashe duwatsu da katakan da Ba’asha yake amfani da su daga Rama. Da duwatsu da katakan ne Sarki Asa ya gina Geba a Benyamin da kuma Mizfa.
Kralj Asa sazva sve Judejce, bez izuzetka, i oni odnesoše kamenje i drvo kojima je Baša utvrđivao Ramu, i kralj Asa utvrdi time Gebu Benjaminovu i Mispu.
23 Game da sauran ayyukan mulkin Asa, dukan nasarorinsa, dukan abin da ya yi, da kuma biranen da ya gina, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Yahuda. A tsufansa, sai ƙafafunsa suka kamu da cuta.
Ostala povijest Asina, sve njegove pobjede i sve što je učinio i gradovi koje je utvrdio, zar to nije zapisano u knjizi Ljetopisa kraljeva judejskih? A u starosti bolovao je od nogu.
24 Sai Asa ya huta tare da kakanninsa, aka kuma binne shi tare da su a birnin kakansa Dawuda. Sai Yehoshafat ɗansa ya gāje shi a matsayin sarki.
Asa je počinuo sa svojim ocima i sahranjen je sa svojim ocima u gradu Davida, svoga praoca. Njegov sin Jošafat zakralji se mjesto njega.
25 Nadab ɗan Yerobowam ya zama sarkin Isra’ila a shekara ta biyu ta Asa sarkin Yahuda, ya kuma yi mulki a bisa Isra’ila shekara biyu.
Nadab, sin Jeroboamov, postade kraljem Izraela druge godine Asina kraljevanja Judejom i vladao je dvije godine Izraelom.
26 Ya yi mugunta a gaban Ubangiji, yana tafiya a hanyoyin mahaifinsa da kuma cikin zunubinsa, wanda ya sa Isra’ila suka yi.
Činio je zlo u očima Jahvinim. Hodio je putem svoga oca i oponašao njegov grijeh na koji je navodio Izraela.
27 Ba’asha ɗan Ahiya na gidan Issakar ya yi maƙarƙashiya gāba da shi, ya buge shi a Gibbeton, a wani garin Filistiyawa, yayinda Nadab da dukan Isra’ila suke wa garin kwanto.
Baša, sin Ahijin, iz kuće Jisakarove, uroti se protiv njega i ubi ga u Gibetonu, koji pripada Filistejcima i koji su opsjedali Nadab i sav Izrael.
28 Ba’asha ya kashe Nadab a shekara ta uku ta Asa sarkin Yahuda, ya kuma gāje shi a matsayin sarki.
Baša ga ubi treće godine Asina kraljevanja Judejom i zavlada mjesto njega.
29 Nan da nan da ya fara mulki, sai ya kashe dukan iyalin Yerobowam. Bai bar wa Yerobowam wani da rai ba, amma ya hallaka su duka, bisa ga maganar Ubangiji da ya ba wa bawansa Ahiya, mutumin Shilo.
Kad je postao kraljem, pobi svu kuću Jeroboamovu i ne poštedi nikoga od Jeroboamovih dokle sve ne istrijebi po riječi koju je Jahve rekao preko sluge svoga Ahije iz Šila.
30 Wannan abu ya faru saboda zunuban da Yerobowam ya yi, ya kuma sa Isra’ila ya yi, kuma saboda ya tsokane Ubangiji, Allah na Isra’ila, ya yi fushi.
Zbog grijeha što ih je učinio i na koje je naveo Izraela i zbog gnjeva kojim je raspalio Jahvu, Boga Izraelova.
31 Game da sauran ayyukan mulkin Nadab da kuma dukan abin da ya yi, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Isra’ila.
Ostala povijest Nadabova, i sve što je učinio, zar to nije zapisano u knjizi Ljetopisa kraljeva izraelskih?
32 Aka yi yaƙi tsakanin Asa da Ba’asha sarkin Isra’ila dukan kwanakin mulkinsu.
Između Ase i Izraelova kralja Baše vladao je rat u sve njihove dane.
33 A shekara ta uku ta Asa sarkin Yahuda, Ba’asha ɗan Ahiya ya zama sarkin dukan Isra’ila a Tirza, ya kuma yi sarauta shekara ashirin da huɗu.
Treće godine Asina kraljevanja Judejom postade Baša, sin Ahijin, kraljem nad svim Izraelom u Tirsi i vladao je dvadeset i četiri godine.
34 Ya aikata mugunta a gaban Ubangiji, yana tafiya a hanyoyin Yerobowam da kuma cikin zunubinsa, wanda ya sa Isra’ila suka yi.
Činio je zlo u očima Jahvinim i hodio je putem Jeroboama i njegovih grijeha kojima je zavodio Izraelce.

< 1 Sarakuna 15 >