< 1 Sarakuna 14 >
1 A lokacin Abiya, ɗan Yerobowam ya kamu da ciwo,
Naquela época Abijah, o filho de Jeroboam, adoeceu.
2 sai Yerobowam ya ce wa matarsa, “Ki tafi, ki ɓad da kama, don kada a gane ke a matsayin matar Yerobowam. Ki je Shilo. Annabi Ahiya yana a can, wannan wanda ya ce mini zan zama sarki a bisa wannan mutane.
Jeroboam disse a sua esposa: “Por favor, levante-se e disfarce-se, para que você não seja reconhecida como esposa de Jeroboam. Vá para Shiloh. Eis que Ahijah o profeta está lá, que disse que eu seria rei sobre este povo.
3 Ki ɗauki dunƙulen burodi goma tare da ke, da waina, da tulun zuma, ki tafi wurinsa. Zai faɗa miki abin da zai faru da yaron.”
Leve consigo dez pães, alguns bolos e um pote de mel, e vá até ele. Ele vos dirá o que será da criança”.
4 Saboda haka matar Yerobowam ta yi abin da ya faɗa, ta kuma tafi gidan Ahiya a Shilo. Yanzu dai Ahiya ba ya gani; idanunsa sun tafi saboda tsufa.
A esposa de Jeroboam o fez, levantou-se e foi para Shiloh, e veio para a casa de Ahijah. Agora Ahijah não podia ver, pois seus olhos estavam fixos por causa de sua idade.
5 Amma Ubangiji ya ce wa Ahiya, “Matar Yerobowam tana zuwa tă tambaye ka game da ɗanta, gama yana ciwo, za ka kuwa ba ta amsa kaza da kaza. Sa’ad da ta iso za tă yi kamar wata ce dabam.”
Yahweh disse a Ahijah: “Eis que a esposa de Jeroboão vem para lhe perguntar sobre seu filho, pois ele está doente. Diga-lhe tal e tal; pois será, quando ela entrar, que ela fingirá ser outra mulher”.
6 Saboda haka sa’ad da Ahiya ya ji motsin sawunta a ƙofa, sai ya ce, “Ki shigo, matar Yerobowam. Me ya sa kike yi kamar wata ce dabam? An aiko ni wurinki da labari marar daɗi.
Então quando Ahijah ouviu o som de seus pés ao entrar pela porta, ele disse: “Entre, mulher de Jeroboam! Por que você finge ser outra? Pois fui enviado a você com pesadas notícias.
7 Je ki faɗa wa Yerobowam cewa ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila ya ce, ‘Na tā da kai daga cikin mutane, na mai da kai shugaba a bisa mutanena Isra’ila.
Go, diga a Jeroboão: “Yahweh, o Deus de Israel, diz: “Porque te exaltei do meio do povo, e te fiz príncipe sobre meu povo Israel,
8 Na yage mulki daga gidan Dawuda na ba da shi gare ka, amma ba ka zama kamar bawana Dawuda wanda ya kiyaye umarnaina ya kuma bi ni da dukan zuciyarsa, yana yin abin da yake daidai kaɗai a idanuna ba.
e rasguei o reino da casa de Davi, e te dei a ti”; e ainda não foste como meu servo Davi, que guardou meus mandamentos, e que me seguiu de todo o coração, para fazer apenas o que estava certo aos meus olhos,
9 Ka aikata mugunta fiye da dukan waɗanda suka rayu kafin kai. Ka yi wa kanka waɗansu alloli, gumakan da aka yi da ƙarfe; ka tsokane ni na yi fushi, ka kuma juye mini baya.
mas fizeste o mal acima de todos que foram antes de ti, e foste e fizeste para ti outros deuses, imagens fundidas, para me provocar à ira, e me lançaram nas suas costas,
10 “‘Saboda wannan, zan kawo masifa a gidan Yerobowam. Zan yanke kowane ɗa na ƙarshe a Isra’ila, bawa ko’yantacce. Zan ƙone gidan Yerobowam kamar yadda mutum yakan ƙone juji, sai duk ya ƙone ƙurmus.
portanto, eis que trarei o mal sobre a casa de Jeroboão, e cortarei de Jeroboão todo aquele que urina em um muro, aquele que está calado e aquele que fica à solta em Israel, e varrerei completamente a casa de Jeroboão, como um homem varre o esterco até que tudo desapareça.
11 Karnuka za su ci waɗanda suka mutu na Yerobowam a cikin birni, kuma tsuntsayen sararin sama za su cinye waɗanda suka mutu a jeji. Ni Ubangiji na faɗa!’
Os cães comerão aquele que pertence a Jeroboão que morrer na cidade; e os pássaros do céu comerão aquele que morrer no campo, pois Yahweh o disse”'.
12 “Ke kuma, ki koma gida. Sa’ad da kika taka ƙafa a birninki, yaron zai mutu.
Levante-se, portanto, e vá para sua casa. Quando seus pés entrarem na cidade, a criança morrerá.
13 Dukan Isra’ila kuwa za su yi makoki dominsa. Shi ne kaɗai na Yerobowam wanda za a binne, domin shi ne kaɗai a gidan Yerobowam wanda Ubangiji, Allah na Isra’ila ya sami wani ɗan abu mai kyau a kansa.
Todo Israel chorará por ele e o enterrará; pois somente ele de Jeroboão virá à sepultura, porque nele se encontra algo de bom para Javé, o Deus de Israel, na casa de Jeroboão.
14 “Ubangiji zai tā da wani sarki wa kansa a bisa Isra’ila wanda zai hallaka iyalin Yerobowam. Ko yanzu ma, wannan zai fara faruwa.
Além disso, Javé levantará para si um rei sobre Israel que cortará a casa de Jeroboão. Este é o dia! O quê? Mesmo agora.
15 Ubangiji kuma zai bugi Isra’ila, har tă zama kamar kyauro mai girgiza a bakin rafi. Zai tumɓuke Isra’ila daga wannan ƙasa mai kyau da ya ba wa kakanninsu, yă watsar da su gaba da Kogin Yuferites domin sun tsokane Ubangiji har ya yi fushi, ta wurin yin ginshiƙan Ashera.
Pois Javé atacará Israel, enquanto uma cana é sacudida na água; e arrancará Israel desta boa terra que deu a seus pais, e os espalhará para além do rio, porque fizeram seus bastões de Aserah, provocando Javé à ira.
16 Zai kuma ba da Isra’ila saboda zunuban da Yerobowam ya yi, da ya kuma sa Isra’ila suka yi.”
Ele desistirá de Israel por causa dos pecados de Jeroboão, que ele pecou, e com os quais ele fez Israel pecar”.
17 Sai matar Yerobowam ta tashi ta tafi, ta kuwa tafi Tirza. Nan da nan da ta taka madogarar ƙofar gidan, sai yaron ya mutu.
A esposa de Jeroboam se levantou e partiu, e veio para Tirzah. Quando ela chegou ao limiar da casa, a criança morreu.
18 Suka binne shi, dukan Isra’ila kuwa suka yi makoki dominsa, yadda Ubangiji ya faɗa ta wurin bawansa annabi Ahiya.
Todo Israel o enterrou e chorou por ele, de acordo com a palavra de Javé, que ele falou por seu servo Ahijah, o profeta.
19 Sauran ayyukan sarautar Yerobowam, da yaƙe-yaƙensa, da yadda ya yi mulki, ba a rubuce suke a littafin tarihi na sarakunan Isra’ila ba?
O resto dos atos de Jeroboão, como ele lutou e como reinou, eis que estão escritos no livro das crônicas dos reis de Israel.
20 Ya yi mulki shekaru ashirin da biyu, sai ya huta tare da kakanninsa. Sai Nadab ɗansa ya gāje shi a matsayin sarki.
Os dias que Jeroboão reinou foram vinte e dois anos; depois ele dormiu com seus pais, e Nadab, seu filho, reinou em seu lugar.
21 Rehobowam ɗan Solomon ya zama sarki a Yahuda. Yana da shekara arba’in da ɗaya sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi mulki shekaru goma sha bakwai a Urushalima, birnin da Ubangiji ya zaɓa daga cikin dukan kabilan Isra’ila don yă sa Sunansa. Sunan mahaifiyarsa Na’ama, ita mutuniyar Ammon ce.
Rehoboam, filho de Salomão, reinou em Judá. Roboão tinha quarenta e um anos quando começou a reinar, e reinou dezessete anos em Jerusalém, a cidade que Javé havia escolhido de todas as tribos de Israel, para colocar seu nome lá. O nome de sua mãe era Naamah, a amonita.
22 Yahuda ya aikata mugunta a gaban Ubangiji. Ta wurin zunuban da suka yi, sun tā da fushin kishinsa fiye da yadda kakanninsu suka yi.
Judá fez o que era mau aos olhos de Iavé, e eles o provocaram a ciúmes com seus pecados que cometeram, sobretudo que seus pais tinham feito.
23 Sun kuma kafa wa kansu masujadai da suke kan tuddai, da a kan keɓaɓɓun duwatsu, suka kuma gina ginshiƙan Ashera a kowane tudu, da kuma a ƙarƙashin kowane duhuwar itace.
Pois eles também construíram para si mesmos lugares altos, pilares sagrados e varas de Asherah em cada colina alta e debaixo de cada árvore verde.
24 Har ma akwai maza karuwai na masujada. Mutane suka sa kansu ga yin kowane abin ƙyama na al’umman da Ubangiji ya kora kafin Isra’ilawa.
Havia também sodomitas na terra. Eles faziam de acordo com todas as abominações das nações que Javé expulsava diante dos filhos de Israel.
25 A shekara ta biyar ta Sarki Rehobowam, Shishak sarkin Masar ya kai wa Urushalima yaƙi.
No quinto ano do rei Roboão, Shishak, rei do Egito, enfrentou Jerusalém;
26 Ya kwashe dukiyar haikalin Ubangiji da kuma dukiyar fadan sarki. Ya ɗauki kome, har da dukan garkuwoyi na zinariya da Solomon ya yi.
e tirou os tesouros da casa de Iavé e os tesouros da casa do rei. Ele até tirou tudo, incluindo todos os escudos de ouro que Salomão havia feito.
27 Saboda haka sarki Rehobowam ya yi garkuwoyin tagulla ya mayar da su. Ya kuma naɗa waɗannan shugabannin matsara ya sa su aiki a ƙofar zuwa fadan sarki.
O rei Roboão fez escudos de bronze em seu lugar, e os entregou às mãos dos capitães da guarda, que guardavam a porta da casa do rei.
28 Duk sa’ad da sarki ya tafi wurin haikalin Ubangiji, matsara sukan riƙe garkuwoyinsu, daga baya kuma sai su mai da su ɗakin tsaro.
Foi assim que, tantas vezes quanto o rei entrava na casa de Yahweh, a guarda os aborrecia e os trazia de volta para a sala da guarda.
29 Game da sauran ayyukan mulkin Rehobowam kuwa, da kuma dukan abin da ya yi, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Yahuda.
Agora o resto dos atos de Rehoboam, e tudo o que ele fez, não estão escritos no livro das crônicas dos reis de Judá?
30 Aka ci gaba da yaƙe-yaƙe tsakanin Rehobowam da Yerobowam.
Havia uma guerra entre Roboão e Jeroboão continuamente.
31 Sai Rehobowam ya huta da kakanninsa, aka kuma binne shi tare da su a Birnin Dawuda. Sunan mahaifiyarsa Na’ama, ita kuwa mutuniyar Ammon ce. Sai Abiyam ɗansa ya gāje shi a matsayin sarki.
Rehoboam dormiu com seus pais, e foi enterrado com seus pais na cidade de David. O nome de sua mãe era Naamah, a amonita. Abijam, seu filho reinou em seu lugar.