< 1 Sarakuna 14 >
1 A lokacin Abiya, ɗan Yerobowam ya kamu da ciwo,
En ce temps-là, Ahiyya, fils de Jéroboam, tomba malade.
2 sai Yerobowam ya ce wa matarsa, “Ki tafi, ki ɓad da kama, don kada a gane ke a matsayin matar Yerobowam. Ki je Shilo. Annabi Ahiya yana a can, wannan wanda ya ce mini zan zama sarki a bisa wannan mutane.
Jéroboam dit à sa femme: "Va, je te prie, et déguise-toi, afin qu’on ne sache pas que tu es la femme de Jéroboam; tu te rendras à Silo, où demeure le prophète Ahiyya, celui qui a prédit que je régnerais sur ce peuple.
3 Ki ɗauki dunƙulen burodi goma tare da ke, da waina, da tulun zuma, ki tafi wurinsa. Zai faɗa miki abin da zai faru da yaron.”
Tu emporteras dix pains, des gâteaux et un pot de miel; tu te présenteras à lui, et il t’apprendra ce qui doit advenir de l’enfant."
4 Saboda haka matar Yerobowam ta yi abin da ya faɗa, ta kuma tafi gidan Ahiya a Shilo. Yanzu dai Ahiya ba ya gani; idanunsa sun tafi saboda tsufa.
Se conformant à cette parole, la femme de Jéroboam s’en alla à Silo et pénétra dans la maison d’Ahiyya. Or, celui-ci ne pouvait la voir, car la vieillesse avait paralysé ses yeux.
5 Amma Ubangiji ya ce wa Ahiya, “Matar Yerobowam tana zuwa tă tambaye ka game da ɗanta, gama yana ciwo, za ka kuwa ba ta amsa kaza da kaza. Sa’ad da ta iso za tă yi kamar wata ce dabam.”
Mais le Seigneur avait dit à Ahiyya: "La femme de Jéroboam va venir te consulter au sujet de son enfant malade; tu lui parleras de telle et telle façon; mais en t’abordant, elle se donnera comme étrangère."
6 Saboda haka sa’ad da Ahiya ya ji motsin sawunta a ƙofa, sai ya ce, “Ki shigo, matar Yerobowam. Me ya sa kike yi kamar wata ce dabam? An aiko ni wurinki da labari marar daɗi.
En entendant le bruit de ses pas lorsqu’elle franchissait le seuil, Ahiyya lui dit: "Entre, épouse de Jéroboam! Pourquoi le déguiser? J’Ai reçu pour toi un message sévère.
7 Je ki faɗa wa Yerobowam cewa ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila ya ce, ‘Na tā da kai daga cikin mutane, na mai da kai shugaba a bisa mutanena Isra’ila.
Va dire à Jéroboam: Ainsi parle l’Eternel, Dieu d’Israël: Je t’avais élevé du milieu du peuple, je t’avais fait chef de mon peuple Israël;
8 Na yage mulki daga gidan Dawuda na ba da shi gare ka, amma ba ka zama kamar bawana Dawuda wanda ya kiyaye umarnaina ya kuma bi ni da dukan zuciyarsa, yana yin abin da yake daidai kaɗai a idanuna ba.
j’avais arraché la royauté à la maison de David pour te l’octroyer à toi; mais tu n’as pas été comme mon serviteur David, qui a gardé mes commandements, qui m’a obéi de tout son cœur en faisant uniquement ce qui est droit à mes yeux.
9 Ka aikata mugunta fiye da dukan waɗanda suka rayu kafin kai. Ka yi wa kanka waɗansu alloli, gumakan da aka yi da ƙarfe; ka tsokane ni na yi fushi, ka kuma juye mini baya.
Surpassant en perversité tous tes devanciers, tu t’es fait des dieux étrangers et des idoles de métal, pour m’outrager, et tu m’as rejeté bien loin de toi!
10 “‘Saboda wannan, zan kawo masifa a gidan Yerobowam. Zan yanke kowane ɗa na ƙarshe a Isra’ila, bawa ko’yantacce. Zan ƙone gidan Yerobowam kamar yadda mutum yakan ƙone juji, sai duk ya ƙone ƙurmus.
C’Est pourquoi je susciterai le malheur à la maison de Jéroboam; je n’en épargnerai pas la plus infime créature, je ne lui laisserai ni retraite ni ressource en Israël, et je balaierai les derniers vestiges de la maison de Jéroboam comme on balaie à fond les ordures.
11 Karnuka za su ci waɗanda suka mutu na Yerobowam a cikin birni, kuma tsuntsayen sararin sama za su cinye waɗanda suka mutu a jeji. Ni Ubangiji na faɗa!’
Ceux de Jéroboam qui mourront dans la ville seront dévorés par les chiens, et ceux qui mourront dans les campagnes seront la proie des oiseaux de l’air: c’est l’Eternel qui l’a dit.
12 “Ke kuma, ki koma gida. Sa’ad da kika taka ƙafa a birninki, yaron zai mutu.
Pour toi, va, retourne en ta demeure; à ton premier pas dans la ville, l’enfant mourra.
13 Dukan Isra’ila kuwa za su yi makoki dominsa. Shi ne kaɗai na Yerobowam wanda za a binne, domin shi ne kaɗai a gidan Yerobowam wanda Ubangiji, Allah na Isra’ila ya sami wani ɗan abu mai kyau a kansa.
Tout Israël mènera son deuil quand on l’ensevelira, car, seul de la maison de Jéroboam, il aura une sépulture, parce que l’Eternel, Dieu d’Israël, l’en a trouvé seul digne dans cette famille.
14 “Ubangiji zai tā da wani sarki wa kansa a bisa Isra’ila wanda zai hallaka iyalin Yerobowam. Ko yanzu ma, wannan zai fara faruwa.
Mais l’Eternel suscitera un roi d’Israël qui anéantira la maison de Jéroboam ce même jour, que dis-je? dès aujourd’hui.
15 Ubangiji kuma zai bugi Isra’ila, har tă zama kamar kyauro mai girgiza a bakin rafi. Zai tumɓuke Isra’ila daga wannan ƙasa mai kyau da ya ba wa kakanninsu, yă watsar da su gaba da Kogin Yuferites domin sun tsokane Ubangiji har ya yi fushi, ta wurin yin ginshiƙan Ashera.
L’Eternel frappera Israël, comme le roseau est ballotté dans l’eau; il arrachera Israël de ce beau pays qu’il a donné à leurs pères, il les dispersera par delà le fleuve, parce qu’ils ont, avec leurs achêrot, irrité le Seigneur.
16 Zai kuma ba da Isra’ila saboda zunuban da Yerobowam ya yi, da ya kuma sa Isra’ila suka yi.”
Il traitera ainsi Israël, à cause des méfaits de Jéroboam, qu’il a commis et qu’il a fait commettre à Israël."
17 Sai matar Yerobowam ta tashi ta tafi, ta kuwa tafi Tirza. Nan da nan da ta taka madogarar ƙofar gidan, sai yaron ya mutu.
Là-dessus, la femme de Jéroboam se retira et se rendit à Tirça. Comme elle atteignit le seuil de la maison, le jeune garçon mourut.
18 Suka binne shi, dukan Isra’ila kuwa suka yi makoki dominsa, yadda Ubangiji ya faɗa ta wurin bawansa annabi Ahiya.
On l’ensevelit, et tout Israël mena son deuil, selon la parole du Seigneur, transmise par son serviteur, le prophète Ahiyya.
19 Sauran ayyukan sarautar Yerobowam, da yaƙe-yaƙensa, da yadda ya yi mulki, ba a rubuce suke a littafin tarihi na sarakunan Isra’ila ba?
Pour les autres faits concernant Jéroboam, ses guerres et son règne, ils sont consignés dans le livre des annales des rois d’Israël.
20 Ya yi mulki shekaru ashirin da biyu, sai ya huta tare da kakanninsa. Sai Nadab ɗansa ya gāje shi a matsayin sarki.
La durée du règne de Jéroboam fut de vingt-deux ans; après quoi, il s’endormit avec ses pères, et son fils Nadab lui succéda.
21 Rehobowam ɗan Solomon ya zama sarki a Yahuda. Yana da shekara arba’in da ɗaya sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi mulki shekaru goma sha bakwai a Urushalima, birnin da Ubangiji ya zaɓa daga cikin dukan kabilan Isra’ila don yă sa Sunansa. Sunan mahaifiyarsa Na’ama, ita mutuniyar Ammon ce.
Roboam, fils de Salomon, fut roi de Juda. Il avait quarante et un ans à son avènement, et il régna dix-sept ans à Jérusalem, la ville que le Seigneur avait choisie entre toutes les tribus d’Israël pour y faire dominer son nom. Sa mère se nommait Naama; elle était ammonite.
22 Yahuda ya aikata mugunta a gaban Ubangiji. Ta wurin zunuban da suka yi, sun tā da fushin kishinsa fiye da yadda kakanninsu suka yi.
Les Judaïtes firent ce qui déplaît au Seigneur, et ils l’irritèrent plus que n’avaient jamais fait leurs pères, par les péchés qu’ils commirent.
23 Sun kuma kafa wa kansu masujadai da suke kan tuddai, da a kan keɓaɓɓun duwatsu, suka kuma gina ginshiƙan Ashera a kowane tudu, da kuma a ƙarƙashin kowane duhuwar itace.
Ils érigèrent, eux aussi, des hauts-lieux, des monuments et des statues d’Astarté, sur toute colline élevée et sous tout arbre touffu.
24 Har ma akwai maza karuwai na masujada. Mutane suka sa kansu ga yin kowane abin ƙyama na al’umman da Ubangiji ya kora kafin Isra’ilawa.
Il y eut même des prostitués dans le pays, où l’on imita toutes les abominations des peuples que le Seigneur avait dépossédés en faveur des enfants d’Israël.
25 A shekara ta biyar ta Sarki Rehobowam, Shishak sarkin Masar ya kai wa Urushalima yaƙi.
Dans la cinquième année du règne de Roboam, Sésak, roi d’Egypte, vint attaquer Jérusalem.
26 Ya kwashe dukiyar haikalin Ubangiji da kuma dukiyar fadan sarki. Ya ɗauki kome, har da dukan garkuwoyi na zinariya da Solomon ya yi.
Il s’empara des trésors de la maison de Dieu, et de ceux de la maison du roi, et emporta le tout. Il enleva aussi tous les boucliers d’or qu’avait fait faire Salomon.
27 Saboda haka sarki Rehobowam ya yi garkuwoyin tagulla ya mayar da su. Ya kuma naɗa waɗannan shugabannin matsara ya sa su aiki a ƙofar zuwa fadan sarki.
Le roi Roboam les remplaça par des boucliers de cuivre, dont il confia la garde aux chefs des coureurs chargés de surveiller l’entrée du palais.
28 Duk sa’ad da sarki ya tafi wurin haikalin Ubangiji, matsara sukan riƙe garkuwoyinsu, daga baya kuma sai su mai da su ɗakin tsaro.
Chaque fois que le roi se rendait à la maison de Dieu, les coureurs portaient ces boucliers, puis les replaçaient dans leur salle de service.
29 Game da sauran ayyukan mulkin Rehobowam kuwa, da kuma dukan abin da ya yi, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Yahuda.
Pour le reste de l’histoire et des faits et gestes de Roboam, ils sont consignés dans le livre des annales des rois de Juda.
30 Aka ci gaba da yaƙe-yaƙe tsakanin Rehobowam da Yerobowam.
Roboam et Jéroboam furent constamment en guerre.
31 Sai Rehobowam ya huta da kakanninsa, aka kuma binne shi tare da su a Birnin Dawuda. Sunan mahaifiyarsa Na’ama, ita kuwa mutuniyar Ammon ce. Sai Abiyam ɗansa ya gāje shi a matsayin sarki.
Roboam s’endormit avec ses pères et fut enterré auprès d’eux dans la Cité de David. Sa mère, une Ammonite, s’appelait Naama. Il eut pour successeur son fils Abiam.