< 1 Sarakuna 14 >

1 A lokacin Abiya, ɗan Yerobowam ya kamu da ciwo,
Dans ce temps-là, Abija, fils de Jéroboam, fut malade.
2 sai Yerobowam ya ce wa matarsa, “Ki tafi, ki ɓad da kama, don kada a gane ke a matsayin matar Yerobowam. Ki je Shilo. Annabi Ahiya yana a can, wannan wanda ya ce mini zan zama sarki a bisa wannan mutane.
Et Jéroboam dit à sa femme: Lève-toi, je te prie, et déguise-toi, et qu’on ne sache pas que tu es la femme de Jéroboam, et va-t’en à Silo; voici, là est Akhija, le prophète, qui a dit de moi que je serais roi sur ce peuple.
3 Ki ɗauki dunƙulen burodi goma tare da ke, da waina, da tulun zuma, ki tafi wurinsa. Zai faɗa miki abin da zai faru da yaron.”
Et tu prendras avec toi dix pains, et des gâteaux, et une cruche de miel, et tu iras vers lui; il te dira ce qui arrivera à l’enfant.
4 Saboda haka matar Yerobowam ta yi abin da ya faɗa, ta kuma tafi gidan Ahiya a Shilo. Yanzu dai Ahiya ba ya gani; idanunsa sun tafi saboda tsufa.
Et la femme de Jéroboam fit ainsi, et elle se leva et s’en alla à Silo, et vint à la maison d’Akhija. Et Akhija ne pouvait voir, car ses yeux étaient fixes à cause de son âge.
5 Amma Ubangiji ya ce wa Ahiya, “Matar Yerobowam tana zuwa tă tambaye ka game da ɗanta, gama yana ciwo, za ka kuwa ba ta amsa kaza da kaza. Sa’ad da ta iso za tă yi kamar wata ce dabam.”
Et l’Éternel dit à Akhija: Voici, la femme de Jéroboam vient te demander quelque chose au sujet de son fils, car il est malade; tu lui diras ainsi et ainsi; et il arrivera, quand elle viendra, qu’elle feindra d’être une autre.
6 Saboda haka sa’ad da Ahiya ya ji motsin sawunta a ƙofa, sai ya ce, “Ki shigo, matar Yerobowam. Me ya sa kike yi kamar wata ce dabam? An aiko ni wurinki da labari marar daɗi.
Et il arriva, quand Akhija entendit le bruit de ses pieds, que, comme elle entrait par la porte, il dit: Entre, femme de Jéroboam, pourquoi feins-tu d’être une autre? Or je suis envoyé vers toi [pour t’annoncer] des choses dures.
7 Je ki faɗa wa Yerobowam cewa ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila ya ce, ‘Na tā da kai daga cikin mutane, na mai da kai shugaba a bisa mutanena Isra’ila.
Va, dis à Jéroboam: Ainsi dit l’Éternel, le Dieu d’Israël: Parce que je t’ai élevé du milieu du peuple, et que je t’ai établi prince sur mon peuple Israël,
8 Na yage mulki daga gidan Dawuda na ba da shi gare ka, amma ba ka zama kamar bawana Dawuda wanda ya kiyaye umarnaina ya kuma bi ni da dukan zuciyarsa, yana yin abin da yake daidai kaɗai a idanuna ba.
et que j’ai arraché le royaume de la maison de David, et que je te l’ai donné, et que tu n’as pas été comme mon serviteur David, qui gardait mes commandements et marchait après moi de tout son cœur pour ne faire que ce qui est droit à mes yeux,
9 Ka aikata mugunta fiye da dukan waɗanda suka rayu kafin kai. Ka yi wa kanka waɗansu alloli, gumakan da aka yi da ƙarfe; ka tsokane ni na yi fushi, ka kuma juye mini baya.
mais que tu as fait ce qui est mauvais, plus que tous ceux qui ont été avant toi, et que tu es allé et t’es fait d’autres dieux et des images de fonte pour me provoquer à colère, et que tu m’as jeté derrière ton dos, …
10 “‘Saboda wannan, zan kawo masifa a gidan Yerobowam. Zan yanke kowane ɗa na ƙarshe a Isra’ila, bawa ko’yantacce. Zan ƙone gidan Yerobowam kamar yadda mutum yakan ƙone juji, sai duk ya ƙone ƙurmus.
à cause de cela, voici, je vais faire venir du mal sur la maison de Jéroboam, et je retrancherai de Jéroboam tous les mâles, l’homme lié et l’homme libre en Israël, et j’ôterai la maison de Jéroboam comme on ôte le fumier, jusqu’à ce qu’il n’en reste plus rien.
11 Karnuka za su ci waɗanda suka mutu na Yerobowam a cikin birni, kuma tsuntsayen sararin sama za su cinye waɗanda suka mutu a jeji. Ni Ubangiji na faɗa!’
Celui de [la maison de] Jéroboam qui mourra dans la ville, les chiens le mangeront, et celui qui mourra dans les champs, les oiseaux des cieux le mangeront, car l’Éternel a parlé.
12 “Ke kuma, ki koma gida. Sa’ad da kika taka ƙafa a birninki, yaron zai mutu.
Et toi, lève-toi, va-t’en dans ta maison: quand tes pieds entreront dans la ville, l’enfant mourra.
13 Dukan Isra’ila kuwa za su yi makoki dominsa. Shi ne kaɗai na Yerobowam wanda za a binne, domin shi ne kaɗai a gidan Yerobowam wanda Ubangiji, Allah na Isra’ila ya sami wani ɗan abu mai kyau a kansa.
Et tout Israël mènera deuil sur lui et l’enterrera; car celui-ci seul, de [la maison de] Jéroboam, entrera dans le sépulcre, parce qu’en lui [seul], dans la maison de Jéroboam, a été trouvé quelque chose d’agréable à l’Éternel, le Dieu d’Israël.
14 “Ubangiji zai tā da wani sarki wa kansa a bisa Isra’ila wanda zai hallaka iyalin Yerobowam. Ko yanzu ma, wannan zai fara faruwa.
Et l’Éternel suscitera pour lui-même un roi sur Israël, qui retranchera la maison de Jéroboam ce jour-là; … mais quoi?… déjà maintenant!
15 Ubangiji kuma zai bugi Isra’ila, har tă zama kamar kyauro mai girgiza a bakin rafi. Zai tumɓuke Isra’ila daga wannan ƙasa mai kyau da ya ba wa kakanninsu, yă watsar da su gaba da Kogin Yuferites domin sun tsokane Ubangiji har ya yi fushi, ta wurin yin ginshiƙan Ashera.
Et l’Éternel frappera Israël comme quand le roseau est agité dans les eaux; et il arrachera Israël de dessus cette bonne terre qu’il donna à leurs pères, et il les dispersera au-delà du fleuve, parce qu’ils se sont fait des ashères, provoquant l’Éternel à la colère.
16 Zai kuma ba da Isra’ila saboda zunuban da Yerobowam ya yi, da ya kuma sa Isra’ila suka yi.”
Et il livrera Israël à cause des péchés de Jéroboam, qu’il a commis et par lesquels il a fait pécher Israël.
17 Sai matar Yerobowam ta tashi ta tafi, ta kuwa tafi Tirza. Nan da nan da ta taka madogarar ƙofar gidan, sai yaron ya mutu.
Et la femme de Jéroboam se leva et s’en alla, et vint à Thirtsa: comme elle arrivait sur le seuil de la maison, l’enfant mourut.
18 Suka binne shi, dukan Isra’ila kuwa suka yi makoki dominsa, yadda Ubangiji ya faɗa ta wurin bawansa annabi Ahiya.
Et on l’enterra, et tout Israël mena deuil sur lui, selon la parole de l’Éternel, qu’il avait dite par son serviteur Akhija, le prophète.
19 Sauran ayyukan sarautar Yerobowam, da yaƙe-yaƙensa, da yadda ya yi mulki, ba a rubuce suke a littafin tarihi na sarakunan Isra’ila ba?
Et le reste des actes de Jéroboam, comment il fit la guerre, et comment il régna, voici, cela est écrit dans le livre des chroniques des rois d’Israël.
20 Ya yi mulki shekaru ashirin da biyu, sai ya huta tare da kakanninsa. Sai Nadab ɗansa ya gāje shi a matsayin sarki.
Et les jours que Jéroboam régna furent 22 ans. Et il s’endormit avec ses pères, et Nadab, son fils, régna à sa place.
21 Rehobowam ɗan Solomon ya zama sarki a Yahuda. Yana da shekara arba’in da ɗaya sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi mulki shekaru goma sha bakwai a Urushalima, birnin da Ubangiji ya zaɓa daga cikin dukan kabilan Isra’ila don yă sa Sunansa. Sunan mahaifiyarsa Na’ama, ita mutuniyar Ammon ce.
Et Roboam, fils de Salomon, régna sur Juda. Roboam était âgé de 41 ans lorsqu’il commença de régner; et il régna 17 ans à Jérusalem, la ville que l’Éternel avait choisie d’entre toutes les tribus d’Israël pour y mettre son nom; et le nom de sa mère était Naama, une Ammonite.
22 Yahuda ya aikata mugunta a gaban Ubangiji. Ta wurin zunuban da suka yi, sun tā da fushin kishinsa fiye da yadda kakanninsu suka yi.
Et Juda fit ce qui est mauvais aux yeux de l’Éternel; et ils le provoquèrent à la jalousie plus que tout ce que leurs pères avaient fait par leurs péchés qu’ils commirent.
23 Sun kuma kafa wa kansu masujadai da suke kan tuddai, da a kan keɓaɓɓun duwatsu, suka kuma gina ginshiƙan Ashera a kowane tudu, da kuma a ƙarƙashin kowane duhuwar itace.
Et ils bâtirent, eux aussi, pour eux-mêmes, des hauts lieux, et des statues, et des ashères, sur toute haute colline et sous tout arbre vert;
24 Har ma akwai maza karuwai na masujada. Mutane suka sa kansu ga yin kowane abin ƙyama na al’umman da Ubangiji ya kora kafin Isra’ilawa.
il y avait aussi dans le pays des hommes voués à la prostitution. Ils firent selon toutes les abominations des nations que l’Éternel avait dépossédées devant les fils d’Israël.
25 A shekara ta biyar ta Sarki Rehobowam, Shishak sarkin Masar ya kai wa Urushalima yaƙi.
Et il arriva, en la cinquième année du roi Roboam, que Shishak, roi d’Égypte, monta contre Jérusalem.
26 Ya kwashe dukiyar haikalin Ubangiji da kuma dukiyar fadan sarki. Ya ɗauki kome, har da dukan garkuwoyi na zinariya da Solomon ya yi.
Et il prit les trésors de la maison de l’Éternel et les trésors de la maison du roi: il prit tout. Et il prit tous les boucliers d’or que Salomon avait faits.
27 Saboda haka sarki Rehobowam ya yi garkuwoyin tagulla ya mayar da su. Ya kuma naɗa waɗannan shugabannin matsara ya sa su aiki a ƙofar zuwa fadan sarki.
Et le roi Roboam fit à leur place des boucliers d’airain, et les confia aux mains des chefs des coureurs qui gardaient l’entrée de la maison du roi.
28 Duk sa’ad da sarki ya tafi wurin haikalin Ubangiji, matsara sukan riƙe garkuwoyinsu, daga baya kuma sai su mai da su ɗakin tsaro.
Et toutes les fois que le roi entrait dans la maison de l’Éternel, il arrivait que les coureurs les portaient, puis ils les rapportaient dans la chambre des coureurs.
29 Game da sauran ayyukan mulkin Rehobowam kuwa, da kuma dukan abin da ya yi, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Yahuda.
Et le reste des actes de Roboam, et tout ce qu’il fit, cela n’est-il pas écrit dans le livre des chroniques des rois de Juda?
30 Aka ci gaba da yaƙe-yaƙe tsakanin Rehobowam da Yerobowam.
Et il y eut guerre entre Roboam et Jéroboam, tous [leurs] jours.
31 Sai Rehobowam ya huta da kakanninsa, aka kuma binne shi tare da su a Birnin Dawuda. Sunan mahaifiyarsa Na’ama, ita kuwa mutuniyar Ammon ce. Sai Abiyam ɗansa ya gāje shi a matsayin sarki.
Et Roboam s’endormit avec ses pères, et il fut enterré avec ses pères dans la ville de David; et le nom de sa mère était Naama, une Ammonite. Et Abijam, son fils, régna à sa place.

< 1 Sarakuna 14 >