< 1 Sarakuna 14 >

1 A lokacin Abiya, ɗan Yerobowam ya kamu da ciwo,
At that time Abia the son of Jeroboam fell sick.
2 sai Yerobowam ya ce wa matarsa, “Ki tafi, ki ɓad da kama, don kada a gane ke a matsayin matar Yerobowam. Ki je Shilo. Annabi Ahiya yana a can, wannan wanda ya ce mini zan zama sarki a bisa wannan mutane.
And Jeroboam said to his wife: Arise, and change thy dress, that thou be not known to be the wife of Jeroboam, and go to Silo, where Ahias the prophet is, who told me, that I should reign over this people.
3 Ki ɗauki dunƙulen burodi goma tare da ke, da waina, da tulun zuma, ki tafi wurinsa. Zai faɗa miki abin da zai faru da yaron.”
Take also with thee ten leaves, and cracknels, and a pot of honey, and go to him: for he will tell thee what shall become of this child.
4 Saboda haka matar Yerobowam ta yi abin da ya faɗa, ta kuma tafi gidan Ahiya a Shilo. Yanzu dai Ahiya ba ya gani; idanunsa sun tafi saboda tsufa.
Jeroboam’s wife did as he told her: and rising up went to Silo, and came to the house of Ahias: but he could not see, for his eyes were dim by reason of his age.
5 Amma Ubangiji ya ce wa Ahiya, “Matar Yerobowam tana zuwa tă tambaye ka game da ɗanta, gama yana ciwo, za ka kuwa ba ta amsa kaza da kaza. Sa’ad da ta iso za tă yi kamar wata ce dabam.”
And the Lord said to Ahias: Behold the wife of Jeroboam cometh in, to consult thee concerning her son that is sick: thus and thus shalt thou speak to her. So when she was coming in, and made as if she were another woman,
6 Saboda haka sa’ad da Ahiya ya ji motsin sawunta a ƙofa, sai ya ce, “Ki shigo, matar Yerobowam. Me ya sa kike yi kamar wata ce dabam? An aiko ni wurinki da labari marar daɗi.
Ahias heard the sound of her feet coming in at the door, and said: Come in, thou wife of Jeroboam: why dost thou feign thyself to be another? But I am sent to thee with heavy tidings.
7 Je ki faɗa wa Yerobowam cewa ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila ya ce, ‘Na tā da kai daga cikin mutane, na mai da kai shugaba a bisa mutanena Isra’ila.
Go, and tell Jeroboam: Thus saith the Lord the God of Israel: Forasmuch as I exalted thee from among the people, and made thee prince over my people Israel:
8 Na yage mulki daga gidan Dawuda na ba da shi gare ka, amma ba ka zama kamar bawana Dawuda wanda ya kiyaye umarnaina ya kuma bi ni da dukan zuciyarsa, yana yin abin da yake daidai kaɗai a idanuna ba.
And rent the kingdom away from the house of David, and gave it to thee, and thou hast not been as my servant David, who kept my commandments, and followed me with all his heart, doing that which was well pleasing in my sight:
9 Ka aikata mugunta fiye da dukan waɗanda suka rayu kafin kai. Ka yi wa kanka waɗansu alloli, gumakan da aka yi da ƙarfe; ka tsokane ni na yi fushi, ka kuma juye mini baya.
But hast done evil above all that were before thee, and hast made thee strange gods and molten gods, to provoke me to anger, and hast cast me behind thy back:
10 “‘Saboda wannan, zan kawo masifa a gidan Yerobowam. Zan yanke kowane ɗa na ƙarshe a Isra’ila, bawa ko’yantacce. Zan ƙone gidan Yerobowam kamar yadda mutum yakan ƙone juji, sai duk ya ƙone ƙurmus.
Therefore behold I will bring evils upon the house of Jeroboam, and will cut of from Jeroboam him that pisseth against the wall, and him that is shut up, and the last in Israel: and I will sweep away the remnant of the house of Jeroboam, as dung is swept away till all be clean.
11 Karnuka za su ci waɗanda suka mutu na Yerobowam a cikin birni, kuma tsuntsayen sararin sama za su cinye waɗanda suka mutu a jeji. Ni Ubangiji na faɗa!’
Them that shall die of Jeroboam in the city, the dogs shall eat: and them that shall die in the field, the birds of the air shall devour: for the Lord hath spoken it.
12 “Ke kuma, ki koma gida. Sa’ad da kika taka ƙafa a birninki, yaron zai mutu.
Arise thou therefore, and go to thy house: and when thy feet shall be entering into the city, the child shall die,
13 Dukan Isra’ila kuwa za su yi makoki dominsa. Shi ne kaɗai na Yerobowam wanda za a binne, domin shi ne kaɗai a gidan Yerobowam wanda Ubangiji, Allah na Isra’ila ya sami wani ɗan abu mai kyau a kansa.
And all Israel shall mourn for him, and shall bury him: for he only of Jeroboam shall be laid in a sepulchre, because in his regard there is found a good word from the Lord the God of Israel, in the house of Jeroboam.
14 “Ubangiji zai tā da wani sarki wa kansa a bisa Isra’ila wanda zai hallaka iyalin Yerobowam. Ko yanzu ma, wannan zai fara faruwa.
And the Lord hath appointed himself a king over Israel, who shall cut off the house of Jeroboam in this day, and in this time:
15 Ubangiji kuma zai bugi Isra’ila, har tă zama kamar kyauro mai girgiza a bakin rafi. Zai tumɓuke Isra’ila daga wannan ƙasa mai kyau da ya ba wa kakanninsu, yă watsar da su gaba da Kogin Yuferites domin sun tsokane Ubangiji har ya yi fushi, ta wurin yin ginshiƙan Ashera.
And the Lord God shall strike Israel as a reed is shaken in the water: and he shall root up Israel out of this good land, which he gave to their fathers, and shall scatter them beyond the river: because they have made to themselves groves, to provoke the Lord.
16 Zai kuma ba da Isra’ila saboda zunuban da Yerobowam ya yi, da ya kuma sa Isra’ila suka yi.”
And the Lord shall give up Israel for the sins of Jeroboam, who hath sinned, and made Israel to sin.
17 Sai matar Yerobowam ta tashi ta tafi, ta kuwa tafi Tirza. Nan da nan da ta taka madogarar ƙofar gidan, sai yaron ya mutu.
And the wife of Jeroboam arose, and departed, and came to Thersa: and when she was coming in to the threshold of the house, the child died;
18 Suka binne shi, dukan Isra’ila kuwa suka yi makoki dominsa, yadda Ubangiji ya faɗa ta wurin bawansa annabi Ahiya.
And they buried him. And all Israel mourned for him according to the word of the Lord, which he spoke by the hand of his servant Ahias the prophet.
19 Sauran ayyukan sarautar Yerobowam, da yaƙe-yaƙensa, da yadda ya yi mulki, ba a rubuce suke a littafin tarihi na sarakunan Isra’ila ba?
And the rest of the acts of Jeroboam, how he fought, and how he reigned, behold they are written in the book of the words of the days of the kings of Israel.
20 Ya yi mulki shekaru ashirin da biyu, sai ya huta tare da kakanninsa. Sai Nadab ɗansa ya gāje shi a matsayin sarki.
And the days that Jeroboam reigned, were two and twenty years: and he slept with his fathers: and Nadab his son reigned in his stead.
21 Rehobowam ɗan Solomon ya zama sarki a Yahuda. Yana da shekara arba’in da ɗaya sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi mulki shekaru goma sha bakwai a Urushalima, birnin da Ubangiji ya zaɓa daga cikin dukan kabilan Isra’ila don yă sa Sunansa. Sunan mahaifiyarsa Na’ama, ita mutuniyar Ammon ce.
And Roboam the son of Solomon reigned in Juda: Roboam was one and forty years old when he began to reign: and he reigned seventeen years in Jerusalem the city, which the Lord chose out of all the tribes of Israel to put his name there. And his mother’s name wee Naama an Ammonitess.
22 Yahuda ya aikata mugunta a gaban Ubangiji. Ta wurin zunuban da suka yi, sun tā da fushin kishinsa fiye da yadda kakanninsu suka yi.
And Juda did evil in the sight of the Lord, and provoked him above all that their fathers had done, in their sins which they committed.
23 Sun kuma kafa wa kansu masujadai da suke kan tuddai, da a kan keɓaɓɓun duwatsu, suka kuma gina ginshiƙan Ashera a kowane tudu, da kuma a ƙarƙashin kowane duhuwar itace.
For they also built them altars, and statues, and groves upon every high hill and under every green tree:
24 Har ma akwai maza karuwai na masujada. Mutane suka sa kansu ga yin kowane abin ƙyama na al’umman da Ubangiji ya kora kafin Isra’ilawa.
There were also the effeminate in the land, and they did according to all the abominations of the people whom the Lord had destroyed before the face of the children of Israel.
25 A shekara ta biyar ta Sarki Rehobowam, Shishak sarkin Masar ya kai wa Urushalima yaƙi.
And in the fifth year of the reign of Roboam, Sesac king of Egypt came up against Jerusalem.
26 Ya kwashe dukiyar haikalin Ubangiji da kuma dukiyar fadan sarki. Ya ɗauki kome, har da dukan garkuwoyi na zinariya da Solomon ya yi.
And he took away the treasures of the house of the Lord, and the king’s treasures, and carried all off: as also the shields of gold which Solomon had made.
27 Saboda haka sarki Rehobowam ya yi garkuwoyin tagulla ya mayar da su. Ya kuma naɗa waɗannan shugabannin matsara ya sa su aiki a ƙofar zuwa fadan sarki.
And Roboam made shields of brass instead of them, and delivered them into the. hand of the captains of the shieldbearers, and of them that kept watch before the gate of the king’s house.
28 Duk sa’ad da sarki ya tafi wurin haikalin Ubangiji, matsara sukan riƙe garkuwoyinsu, daga baya kuma sai su mai da su ɗakin tsaro.
And when the king went into the house of the Lord, they whose office it was to go before him, carried them: and afterwards they brought them back to the armoury of the shieldbearers.
29 Game da sauran ayyukan mulkin Rehobowam kuwa, da kuma dukan abin da ya yi, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Yahuda.
Now the rest of the sets of Roboam, and all that he did, behold they are written in the book of the words of the days of the kings of Juda.
30 Aka ci gaba da yaƙe-yaƙe tsakanin Rehobowam da Yerobowam.
And there was war between Roboam and Jeroboam always.
31 Sai Rehobowam ya huta da kakanninsa, aka kuma binne shi tare da su a Birnin Dawuda. Sunan mahaifiyarsa Na’ama, ita kuwa mutuniyar Ammon ce. Sai Abiyam ɗansa ya gāje shi a matsayin sarki.
And Roboam slept with his fathers, and was buried with them in the city of David: and his mother’s name was Naama an Ammonitess: and Abiam his son reigned in his stead.

< 1 Sarakuna 14 >