< 1 Sarakuna 14 >
1 A lokacin Abiya, ɗan Yerobowam ya kamu da ciwo,
Ved den Tid blev Jeroboams Søn Abija syg.
2 sai Yerobowam ya ce wa matarsa, “Ki tafi, ki ɓad da kama, don kada a gane ke a matsayin matar Yerobowam. Ki je Shilo. Annabi Ahiya yana a can, wannan wanda ya ce mini zan zama sarki a bisa wannan mutane.
Da sagde Jeroboam til sin Hustru: "Tag og forklæd dig, så man ikke kan kende, at du er Jeroboams Hustru, og begiv dig til Silo, thi der bor Profeten Ahija, som kundgjorde mig, at jeg skulde blive Konge over dette Folk;
3 Ki ɗauki dunƙulen burodi goma tare da ke, da waina, da tulun zuma, ki tafi wurinsa. Zai faɗa miki abin da zai faru da yaron.”
tag ti Brød, noget Bagværk og en Krukke Honning med og henvend dig til ham, så vil han sige dig, hvorledes det skal gå Drengen!"
4 Saboda haka matar Yerobowam ta yi abin da ya faɗa, ta kuma tafi gidan Ahiya a Shilo. Yanzu dai Ahiya ba ya gani; idanunsa sun tafi saboda tsufa.
Jeroboams Hustru gjorde nu således; hun begav sig til Silo og gik ind i Ahijas Hus. Ahija kunde ikke se, da hans Øjne var sløve af Alderdom;
5 Amma Ubangiji ya ce wa Ahiya, “Matar Yerobowam tana zuwa tă tambaye ka game da ɗanta, gama yana ciwo, za ka kuwa ba ta amsa kaza da kaza. Sa’ad da ta iso za tă yi kamar wata ce dabam.”
men HERREN havde sagt til Ahija: "Se, Jeroboams Hustru kommer til dig for at høre sig for hos dig angående sin Søn, da han er syg; det og det skal du svare hende; men når hun kommer, er hun forklædt."
6 Saboda haka sa’ad da Ahiya ya ji motsin sawunta a ƙofa, sai ya ce, “Ki shigo, matar Yerobowam. Me ya sa kike yi kamar wata ce dabam? An aiko ni wurinki da labari marar daɗi.
Da nu Ahija hørte Lyden af hendes Trin, som hun gik ind ad Døren, sagde han: "Kom kun ind, Jeroboams Hustru! Hvorfor er du forklædt? Mig er det pålagt at bringe dig en tung Tidende.
7 Je ki faɗa wa Yerobowam cewa ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila ya ce, ‘Na tā da kai daga cikin mutane, na mai da kai shugaba a bisa mutanena Isra’ila.
Gå hen og sig til Jeroboam: Så siger HERREN, Israels Gud: Jeg ophøjede dig af Folkets Midte og gjorde dig til Fyrste over mit Folk Israel
8 Na yage mulki daga gidan Dawuda na ba da shi gare ka, amma ba ka zama kamar bawana Dawuda wanda ya kiyaye umarnaina ya kuma bi ni da dukan zuciyarsa, yana yin abin da yake daidai kaɗai a idanuna ba.
og rev Riget fra Davids Hus og gav dig det; dog har du ikke været som min Tjener David, der holdt mine Bud og fulgte mig af hele sit Hjerte og kun gjorde, hvad der er ret i mine Øjne,
9 Ka aikata mugunta fiye da dukan waɗanda suka rayu kafin kai. Ka yi wa kanka waɗansu alloli, gumakan da aka yi da ƙarfe; ka tsokane ni na yi fushi, ka kuma juye mini baya.
men du har handlet værre end alle dine Forgængere; du gik hen og krænkede mig og gjorde dig andre Guder og støbte Billeder, men mig kastede du bag din Ryg;
10 “‘Saboda wannan, zan kawo masifa a gidan Yerobowam. Zan yanke kowane ɗa na ƙarshe a Isra’ila, bawa ko’yantacce. Zan ƙone gidan Yerobowam kamar yadda mutum yakan ƙone juji, sai duk ya ƙone ƙurmus.
se, derfor vil jeg bringe Ulykke over Jeroboams Hus og udrydde hvert mandligt Væsen, hver og en af Jeroboams Slægt i Israel, og jeg vil feje Jeroboams Hus bort, som man fejer Skarn bort, til der ikke er Spor tilbage!
11 Karnuka za su ci waɗanda suka mutu na Yerobowam a cikin birni, kuma tsuntsayen sararin sama za su cinye waɗanda suka mutu a jeji. Ni Ubangiji na faɗa!’
Den af Jeroboams Slægt, som dør i Byen, skal Hundene æde, og den, som dør på Marken, skal Himmelens Fugle æde, thi det er HERREN, der har talet!
12 “Ke kuma, ki koma gida. Sa’ad da kika taka ƙafa a birninki, yaron zai mutu.
Men gå nu hjem! Når din Fod betræder Byen, skal Barnet dø;
13 Dukan Isra’ila kuwa za su yi makoki dominsa. Shi ne kaɗai na Yerobowam wanda za a binne, domin shi ne kaɗai a gidan Yerobowam wanda Ubangiji, Allah na Isra’ila ya sami wani ɗan abu mai kyau a kansa.
og hele Israel skal holde Dødeklage over ham og jorde ham, thi han er den eneste af Jeroboams Slægt, der skal komme i en Grav; thi hos ham fandtes dog noget, der vandt HERREN Israels Guds Behag inden for Jeroboams Slægt.
14 “Ubangiji zai tā da wani sarki wa kansa a bisa Isra’ila wanda zai hallaka iyalin Yerobowam. Ko yanzu ma, wannan zai fara faruwa.
Men HERREN vil oprejse sig en Konge over Israel, der skal udrydde Jeroboams Hus på den Dag.
15 Ubangiji kuma zai bugi Isra’ila, har tă zama kamar kyauro mai girgiza a bakin rafi. Zai tumɓuke Isra’ila daga wannan ƙasa mai kyau da ya ba wa kakanninsu, yă watsar da su gaba da Kogin Yuferites domin sun tsokane Ubangiji har ya yi fushi, ta wurin yin ginshiƙan Ashera.
Men også siden vil HERREN slå Israel, så at de svajer hid og did som Sivet i Vandet, og rykke Israel op fra dette herlige Land, som han gav deres Fædre, og sprede dem hinsides Floden, fordi de har lavet sig Asjerastøtter og krænket HERREN;
16 Zai kuma ba da Isra’ila saboda zunuban da Yerobowam ya yi, da ya kuma sa Isra’ila suka yi.”
og han vil give Israel til Pris for de Synders Skyld, Jeroboam har begået og forledt Israel til."
17 Sai matar Yerobowam ta tashi ta tafi, ta kuwa tafi Tirza. Nan da nan da ta taka madogarar ƙofar gidan, sai yaron ya mutu.
Da gav Jeroboams Hustru sig på Vej og kom til Tirza; og da hun betrådte Husets Tærskel, døde Drengen;
18 Suka binne shi, dukan Isra’ila kuwa suka yi makoki dominsa, yadda Ubangiji ya faɗa ta wurin bawansa annabi Ahiya.
og man jordede ham, og hele Israel holdt Dødeklage over ham efter det Ord, HERREN havde talet ved sin Tjener, Profeten Ahija.
19 Sauran ayyukan sarautar Yerobowam, da yaƙe-yaƙensa, da yadda ya yi mulki, ba a rubuce suke a littafin tarihi na sarakunan Isra’ila ba?
Hvad der ellers er at fortælle om Jeroboam, hvorledes han førte Krig, og hvorledes han herskede står jo optegnet i Israels kongers Krønike.
20 Ya yi mulki shekaru ashirin da biyu, sai ya huta tare da kakanninsa. Sai Nadab ɗansa ya gāje shi a matsayin sarki.
Jeroboams Regeringstid udgjorde to og tyve År. Så lagde han sig til Hvile hos sine Fædre, og hans Søn Nadab blev Konge i hans Sted.
21 Rehobowam ɗan Solomon ya zama sarki a Yahuda. Yana da shekara arba’in da ɗaya sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi mulki shekaru goma sha bakwai a Urushalima, birnin da Ubangiji ya zaɓa daga cikin dukan kabilan Isra’ila don yă sa Sunansa. Sunan mahaifiyarsa Na’ama, ita mutuniyar Ammon ce.
Rehabeam, Salomos Søn, blev Kongei Juda. Rehabeam var een og fyrretyve År gammel, da han blev Konge, og han herskede sytten År i Jerusalem, den By, HERREN havde udvalgt af alle Israels Stammer for der at stedfæste sit Navn. Hans Moder var en ammonitisk Kvinde ved Navn Na'ama.
22 Yahuda ya aikata mugunta a gaban Ubangiji. Ta wurin zunuban da suka yi, sun tā da fushin kishinsa fiye da yadda kakanninsu suka yi.
Og Juda gjorde, hvad der var ondt i HERRENs Øjne, og med de Synder, de begik, vakte de hans Nidkærhed, mere end deres Fædre havde gjort.
23 Sun kuma kafa wa kansu masujadai da suke kan tuddai, da a kan keɓaɓɓun duwatsu, suka kuma gina ginshiƙan Ashera a kowane tudu, da kuma a ƙarƙashin kowane duhuwar itace.
Også de byggede sig Offerhøje, Stenstøtter og Asjerastøtter på alle høje Steder og under alle grønne Træer;
24 Har ma akwai maza karuwai na masujada. Mutane suka sa kansu ga yin kowane abin ƙyama na al’umman da Ubangiji ya kora kafin Isra’ilawa.
ja, der var endog Mandsskøger i Landet. De øvede alle de Vederstyggeligheder, som var begået af de Folk, HERREN havde drevet bort foran Israeliterne.
25 A shekara ta biyar ta Sarki Rehobowam, Shishak sarkin Masar ya kai wa Urushalima yaƙi.
Men i Kong Rebabeams femte Regeringsår drog Ægypterkongen Sjisjak op imod Jerusalem
26 Ya kwashe dukiyar haikalin Ubangiji da kuma dukiyar fadan sarki. Ya ɗauki kome, har da dukan garkuwoyi na zinariya da Solomon ya yi.
og tog Skattene i HERRENs Hus og i Kongens Palads; alt tog han, også de Guldskjolde, Salomo havde ladet lave.
27 Saboda haka sarki Rehobowam ya yi garkuwoyin tagulla ya mayar da su. Ya kuma naɗa waɗannan shugabannin matsara ya sa su aiki a ƙofar zuwa fadan sarki.
Kong Rehabeam lod da i Stedet lave Kobberskjolde og gav dem i Forvaring hos Høvedsmændene for Livvagten, der holdt Vagt ved Indgangen til Kongens Palads;
28 Duk sa’ad da sarki ya tafi wurin haikalin Ubangiji, matsara sukan riƙe garkuwoyinsu, daga baya kuma sai su mai da su ɗakin tsaro.
og hver Gang Kongen begav sig til HERRENs Hus, bentede Livvagten dem, og bagefter bragte de dem tilbage til Vagtstuen.
29 Game da sauran ayyukan mulkin Rehobowam kuwa, da kuma dukan abin da ya yi, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Yahuda.
Hvad der ellers er at fortælle om Rehabeam, alt, hvad han gjorde, står jo optegnet i Judas Kongers Krønike.
30 Aka ci gaba da yaƙe-yaƙe tsakanin Rehobowam da Yerobowam.
Rehabeam og Jeroboam lå i Krig med hinanden hele Tiden.
31 Sai Rehobowam ya huta da kakanninsa, aka kuma binne shi tare da su a Birnin Dawuda. Sunan mahaifiyarsa Na’ama, ita kuwa mutuniyar Ammon ce. Sai Abiyam ɗansa ya gāje shi a matsayin sarki.
Så lagde Rehabeam sig til Hvile hos sine Fædre og blev jordet hos sine Fædre i Davidsbyen. Hans Moder var en ammonitisk Kvinde ved Navn Na'ama. Og hans Søn Abija blev Konge i hans Sted.