< 1 Sarakuna 14 >
1 A lokacin Abiya, ɗan Yerobowam ya kamu da ciwo,
Te vaeng tue ah Jeroboam capa Abijah te tlo.
2 sai Yerobowam ya ce wa matarsa, “Ki tafi, ki ɓad da kama, don kada a gane ke a matsayin matar Yerobowam. Ki je Shilo. Annabi Ahiya yana a can, wannan wanda ya ce mini zan zama sarki a bisa wannan mutane.
Te dongah Jeroboam loh a yuu te, “Thoo lamtah thovael uh laeh. Te daengah ni nang te Jeroboam yuu la m'hmat pawt eh. Shiloh kah tonghma Ahijah taengah cet ne. Anih long ni he pilnam soah manghai la om ham kai taengah a thui.
3 Ki ɗauki dunƙulen burodi goma tare da ke, da waina, da tulun zuma, ki tafi wurinsa. Zai faɗa miki abin da zai faru da yaron.”
Na kut dongah buhham neh buhrhaeng cun rha, khoitui tuitang um at khuen. A taengla paan lamtah camoe taengah metla a om ham khaw amah loh nang taengah han thui bitni,” a ti nah.
4 Saboda haka matar Yerobowam ta yi abin da ya faɗa, ta kuma tafi gidan Ahiya a Shilo. Yanzu dai Ahiya ba ya gani; idanunsa sun tafi saboda tsufa.
Jeroboam yuu loh a saii van tangloeng. Thoo tih Shiloh la cet tih Ahijah im a pha. Ahijah khaw a patong neh a mik hmang tih hmu thai voel pawh.
5 Amma Ubangiji ya ce wa Ahiya, “Matar Yerobowam tana zuwa tă tambaye ka game da ɗanta, gama yana ciwo, za ka kuwa ba ta amsa kaza da kaza. Sa’ad da ta iso za tă yi kamar wata ce dabam.”
Tedae BOEIPA Ahijah taengah, “Jeroboam yuu ke a capa kah a tloh dongah nang taengah ol dawt ham ha pawk coeng. Anih te, 'He tlam ni, ke tlam ni, 'ti nah. Anih ha pawk khaw amah loha lah ko,” a ti nah.
6 Saboda haka sa’ad da Ahiya ya ji motsin sawunta a ƙofa, sai ya ce, “Ki shigo, matar Yerobowam. Me ya sa kike yi kamar wata ce dabam? An aiko ni wurinki da labari marar daɗi.
Thohka a pha vaengah a kho ol te Ahijah loh a yaak tih, “Jeroboam yuu ha kun saw, balae tih na muet uh? Kai he nang ham mangkhak la n'tueih coeng.
7 Je ki faɗa wa Yerobowam cewa ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila ya ce, ‘Na tā da kai daga cikin mutane, na mai da kai shugaba a bisa mutanena Isra’ila.
Cet lamtah Jeroboam taengah thui pah. Israel Pathen BOEIPA loh he ni a. thui. Nang he pilnam khui lamloh kan pomsang tih nang he ka pilnam Israel soah rhaengsang la kang khueh.
8 Na yage mulki daga gidan Dawuda na ba da shi gare ka, amma ba ka zama kamar bawana Dawuda wanda ya kiyaye umarnaina ya kuma bi ni da dukan zuciyarsa, yana yin abin da yake daidai kaɗai a idanuna ba.
Ram he David imkhui lamloh ka phen tih nang taengah kam paek coeng. Tedae ka olpaek aka ngaithuen tih ka mik ah a thuem bueng saii ham a thinko boeih neh kai hnukah aka pongpa ka sal David bangla na om moenih.
9 Ka aikata mugunta fiye da dukan waɗanda suka rayu kafin kai. Ka yi wa kanka waɗansu alloli, gumakan da aka yi da ƙarfe; ka tsokane ni na yi fushi, ka kuma juye mini baya.
Namah hmai kah aka om boeih lakah na saii khaw na thae aih. Na cet tih namah ham pathen tloe na saii. Mueihlawn neh kai nan veet tih kai he na nam la nan voeih.
10 “‘Saboda wannan, zan kawo masifa a gidan Yerobowam. Zan yanke kowane ɗa na ƙarshe a Isra’ila, bawa ko’yantacce. Zan ƙone gidan Yerobowam kamar yadda mutum yakan ƙone juji, sai duk ya ƙone ƙurmus.
Te dongah Jeroboam im ah boethae ka khuen coeng he. Jeroboam lamloh pangbueng aka yun thil tih a khoh khaw, Israel khuikah aka loeih khaw ka thup ni. Aekkhuel a cing hil a toih bangla Jeroboam imkhui hnukah ka toih ni.
11 Karnuka za su ci waɗanda suka mutu na Yerobowam a cikin birni, kuma tsuntsayen sararin sama za su cinye waɗanda suka mutu a jeji. Ni Ubangiji na faɗa!’
BOEIPA loh a thui coeng dongah Jeroboam kah a duek rhok te khopuei ah ui loh a caak vetih lohma ah aka duek te vaan kah vaa rhoek loh a caak ni.
12 “Ke kuma, ki koma gida. Sa’ad da kika taka ƙafa a birninki, yaron zai mutu.
Namah thoo lamtah na im la mael laeh. Na kho loh khopuei khuila a kun neh camoe te duek ni.
13 Dukan Isra’ila kuwa za su yi makoki dominsa. Shi ne kaɗai na Yerobowam wanda za a binne, domin shi ne kaɗai a gidan Yerobowam wanda Ubangiji, Allah na Isra’ila ya sami wani ɗan abu mai kyau a kansa.
Anih te Israel pum loh a rhaengsae vetih a up ni. Jeroboam im ah Israel Pathen BOEIPA kah hno then he a khuiah a hmuh dongah Jeroboam khui lamloh anih bueng he ni phuel khuila a pha eh.
14 “Ubangiji zai tā da wani sarki wa kansa a bisa Isra’ila wanda zai hallaka iyalin Yerobowam. Ko yanzu ma, wannan zai fara faruwa.
BOEIPA loh Israel soah manghai a pai sak ni. Anih loh tahae khohnin ah Jeroboam imkhui te a thup pawn ni.
15 Ubangiji kuma zai bugi Isra’ila, har tă zama kamar kyauro mai girgiza a bakin rafi. Zai tumɓuke Isra’ila daga wannan ƙasa mai kyau da ya ba wa kakanninsu, yă watsar da su gaba da Kogin Yuferites domin sun tsokane Ubangiji har ya yi fushi, ta wurin yin ginshiƙan Ashera.
BOEIPA loh Israel te tui dongkah capu a vikvawk bangla a ngawn vetih a napa rhoek taengah a paek he khohmuen then dong lamloh Israel te a phuk ni. Amamih kah Asherah a saii uh neh BOEIPA te a veet uh dongah amih te tuiva rhalvangan duela a haeh uh ni.
16 Zai kuma ba da Isra’ila saboda zunuban da Yerobowam ya yi, da ya kuma sa Isra’ila suka yi.”
Jeroboam kah tholhnah kong ah tholh tih Israel a tholh vanbangla Israel te a tloeng ni,” a ti nah.
17 Sai matar Yerobowam ta tashi ta tafi, ta kuwa tafi Tirza. Nan da nan da ta taka madogarar ƙofar gidan, sai yaron ya mutu.
Te phoeiah Jeroboam yuu te thoo tih mael. Tirzah la cet tih im kah cingkhaa te a cawt vaengah camoe te duek.
18 Suka binne shi, dukan Isra’ila kuwa suka yi makoki dominsa, yadda Ubangiji ya faɗa ta wurin bawansa annabi Ahiya.
BOEIPA ol loh a sal tonghma Ahijah kut ah a thui bangla camoe a up uh vaengah Israel pum loh anih te a rhaengsae uh.
19 Sauran ayyukan sarautar Yerobowam, da yaƙe-yaƙensa, da yadda ya yi mulki, ba a rubuce suke a littafin tarihi na sarakunan Isra’ila ba?
Ol noi la Jeroboam kah a vathoh neh a manghai te, Israel manghai rhoek kah khokhuen tue olka cabu dongah a daek uh ne.
20 Ya yi mulki shekaru ashirin da biyu, sai ya huta tare da kakanninsa. Sai Nadab ɗansa ya gāje shi a matsayin sarki.
A khohnin la Jeroboam he kum kul kum nit a manghai phoeiah tah a napa rhoek taengla khoem uh. Te phoeiah tah anih yueng la a capa Nadab tloep manghai.
21 Rehobowam ɗan Solomon ya zama sarki a Yahuda. Yana da shekara arba’in da ɗaya sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi mulki shekaru goma sha bakwai a Urushalima, birnin da Ubangiji ya zaɓa daga cikin dukan kabilan Isra’ila don yă sa Sunansa. Sunan mahaifiyarsa Na’ama, ita mutuniyar Ammon ce.
Solomon capa Rehoboam tah Judah ah manghai. Rehoboam a manghai vaengah kum sawmli kum khat lo ca coeng. Israel koca boeih khui lamloh amah ming te pahoi khueh ham BOEIPA loh a coelh Jerusalem khopuei ah kum hlai rhih manghai. A manu ming tah Ammoni nu Naamah ni.
22 Yahuda ya aikata mugunta a gaban Ubangiji. Ta wurin zunuban da suka yi, sun tā da fushin kishinsa fiye da yadda kakanninsu suka yi.
Judah khaw BOEIPA mikhmuh ah boethae a saii. A tholhnah neh a tholh uh te a napa rhoek kah a saii boeih lakah BOEIPA a thatlai sakuh.
23 Sun kuma kafa wa kansu masujadai da suke kan tuddai, da a kan keɓaɓɓun duwatsu, suka kuma gina ginshiƙan Ashera a kowane tudu, da kuma a ƙarƙashin kowane duhuwar itace.
Amih loh hmuensang neh kaam te amamih ham a thoh uh. Som a sang boeih neh thing hing hmui boeih ah Asherah a linguh.
24 Har ma akwai maza karuwai na masujada. Mutane suka sa kansu ga yin kowane abin ƙyama na al’umman da Ubangiji ya kora kafin Isra’ilawa.
BOEIPA loh Israel ca rhoek mikhmuh ah a haek namtom rhoek kah tueilaehkoi cungkuem bangla a saii uh tih khohmuen ah hlanghalh khaw om.
25 A shekara ta biyar ta Sarki Rehobowam, Shishak sarkin Masar ya kai wa Urushalima yaƙi.
Rehoboam manghai te a kum nga dongla a pha vaengah Egypt manghai Shishak loh Jerusalem te a paan.
26 Ya kwashe dukiyar haikalin Ubangiji da kuma dukiyar fadan sarki. Ya ɗauki kome, har da dukan garkuwoyi na zinariya da Solomon ya yi.
Te vaengah BOEIPA im kah thakvoh neh manghai im kah thakvoh khaw vik a phueih. Solomon loh a saii sui photling boeih te khaw a pum la a loh tih a khuen.
27 Saboda haka sarki Rehobowam ya yi garkuwoyin tagulla ya mayar da su. Ya kuma naɗa waɗannan shugabannin matsara ya sa su aiki a ƙofar zuwa fadan sarki.
Te dongah manghai Rehoboam loh a yueng la rhohum photling a saii tih manghai im thohka aka tawt imtawt mangpa kut ah a soep sak.
28 Duk sa’ad da sarki ya tafi wurin haikalin Ubangiji, matsara sukan riƙe garkuwoyinsu, daga baya kuma sai su mai da su ɗakin tsaro.
BOEIPA im la manghai a kun dingdoeng vaengah imtawt rhoek loh te te a muk uh. Te phoeiah tah imtawt kah tanhnaem la koep a khoem uh.
29 Game da sauran ayyukan mulkin Rehobowam kuwa, da kuma dukan abin da ya yi, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Yahuda.
Rehoboam kah ol noi neh a saii boeih te Judah manghai rhoek kah khokhuen olka cabu dongah a daek uh moenih a?
30 Aka ci gaba da yaƙe-yaƙe tsakanin Rehobowam da Yerobowam.
Rehoboam laklo neh Jeroboam laklo ah hnin takuem caemtloek om.
31 Sai Rehobowam ya huta da kakanninsa, aka kuma binne shi tare da su a Birnin Dawuda. Sunan mahaifiyarsa Na’ama, ita kuwa mutuniyar Ammon ce. Sai Abiyam ɗansa ya gāje shi a matsayin sarki.
Rehoboam te a napa rhoek taengla a khoem uh vaengah tah David khopuei kah a napa rhoek taengah a up. A manu ming he Ammoni Naamah ni. Te phoeiah anih yueng la a capa Abijam te manghai.