< 1 Sarakuna 13 >
1 Bisa ga umarnin Ubangiji, sai wani mutumin Allah ya zo daga Yahuda zuwa Betel, yayinda Yerobowam yake tsaye kusa da bagade don yă miƙa hadaya.
And behold, there came a man of God from Judah, by the word of Jehovah, to Bethel; and Jeroboam stood by the altar to burn incense.
2 Sai mutumin Allah ya tā da murya a kan bagade bisa ga umarnin Ubangiji ya ce, “Ya bagade, bagade! Ubangiji ya ce, ‘Za a haifi ɗa mai suna Yosiya wa gidan Dawuda. A kanka zai miƙa firistoci na masujadai kan tuddai masu miƙa hadayu a nan, za a kuma ƙone ƙasusuwan mutane a kanka.’”
And he cried against the altar by the word of Jehovah, and said, O altar, altar! thus saith Jehovah: Behold, a child shall be born unto the house of David, Josiah by name; and upon thee shall he sacrifice the priests of the high places that burn incense upon thee, and men's bones shall be burned upon thee.
3 A wannan rana mutumin Allah ya ba da alama, “Ga alamar da Ubangiji ya furta. Wannan bagade zai tsage yă rabu kashi biyu, tokar da yake a kansa za tă zuba a ƙasa.”
And he gave a sign the same day, saying, This is the sign that Jehovah hath spoken: Behold, the altar shall be rent, and the ashes that are upon it shall be poured out.
4 Sa’ad da Yerobowam ya ji abin da mutumin Allah ya tā da murya ya faɗa game da bagaden Betel, sai ya miƙa hannunsa daga bagaden ya ce, “Ku kama shi!” Amma sai hannun da ya miƙa ya yanƙwane, har bai iya janye shi ba.
And it came to pass when the king heard the word of the man of God, which he cried against the altar in Bethel, that Jeroboam stretched forth his hand from the altar, saying, Lay hold on him. And his hand which he stretched out against him dried up, so that he could not bring it back again to him.
5 Haka ma, bagaden ya rabu, tokarsa kuma ya zuba, bisa ga alamar da mutumin Allah ya bayar, ta wurin kalmar Ubangiji.
And the altar was rent, and the ashes poured out from the altar, according to the sign that the man of God had given by the word of Jehovah.
6 Sai sarki ya ce wa mutumin Allah, “Ka roƙi Ubangiji Allahnka, ka kuma yi addu’a domina don hannuna ya warke.” Saboda haka mutumin Allah ya yi roƙo ga Ubangiji, hannun sarki kuwa ya warke, ya kuma zama kamar yadda yake a dā.
And the king answered and said to the man of God, Intreat now Jehovah thy God, and pray for me, that my hand may be restored to me again. And the man of God intreated Jehovah, and the king's hand was restored to him again, and became as before.
7 Sai sarki ya ce wa mutumin Allah, “Zo gida tare da ni, ka sami wani abu ka ci, zan kuwa yi maka kyauta.”
And the king said to the man of God, Come home with me, and refresh thyself, and I will give thee a present.
8 Amma mutumin Allah ya amsa wa sarki, “Ko da za ka ba rabin mallakarka, ba zan tafi tare da kai ba, ba kuwa zan ci abinci, ko in sha ruwa a can ba.
And the man of God said to the king, If thou wilt give me half thy house, I will not go in with thee, neither will I eat bread nor drink water in this place;
9 Gama an umarce ni ta wurin kalmar Ubangiji, aka ce, ‘Kada ka ci abinci, ko ka sha ruwa, ko ka koma ta hanyar da ka zo.’”
for so was it charged me by the word of Jehovah, saying, Thou shalt eat no bread, nor drink water, nor return by the way that thou shalt go.
10 Saboda haka ya ɗauki wata hanya, bai kuwa koma ta hanyar da ya zo Betel ba.
So he went another way, and returned not by the way that he had come to Bethel.
11 To, fa, akwai wani tsohon annabi yana zama a Betel, wanda’ya’yansa suka zo suka faɗa masa dukan abin da mutumin Allah ya yi a can, a ranar. Suka kuma faɗa wa mahaifinsu abin da ya faɗa wa sarki.
Now there dwelt a certain old prophet in Bethel; and his sons came and told him all the works that the man of God had done that day in Bethel; the words that he had spoken to the king, them they told also to their father.
12 Mahaifinsu ya tambaye su ya ce, “Wace hanya ce ya bi?” Sai’ya’yansa suka nuna masa hanyar da mutumin Allah daga Yahuda ya bi.
And their father said to them, Which way went he? for his sons had seen which way the man of God went, who came from Judah.
13 Sai ya ce wa’ya’yansa, “Ku yi wa jakina shimfiɗa.” Da suka yi wa jakin shimfiɗa, sai ya hau.
And he said to his sons, Saddle me the ass. So they saddled him the ass; and he rode thereon,
14 Ya bi bayan mutumin Allah. Ya same shi yana zama a ƙarƙashin itace oak, sai ya tambaye shi ya ce, “Kai ne mutumin Allah wanda ya zo daga Yahuda?” Ya amsa, “Ni ne.”
and went after the man of God, and found him sitting under a terebinth; and he said to him, Art thou the man of God that camest from Judah? And he said, I am.
15 Saboda haka annabin ya ce masa, “Zo gida tare da ni ka ci abinci.”
And he said to him, Come home with me, and eat bread.
16 Mutumin Allah ya ce, “Ba zan koma tare da kai ba, ko in ci abinci, ko in sha ruwa tare da kai a can ba.
And he said, I cannot return with thee, nor go in with thee; neither will I eat bread nor drink water with thee in this place.
17 An faɗa mini ta wurin maganar Ubangiji, ‘Kada ka ci abinci, ko ka sha ruwa a can, ko ka koma ta hanyar da ka zo.’”
For it was said to me by the word of Jehovah, Thou shalt eat no bread nor drink water there, nor turn again to go by the way that thou wentest.
18 Sai annabin ya amsa, “Ni ma annabi ne, kamar ka. Kuma mala’ika ya ce mini ta wurin kalmar Ubangiji, ‘Dawo da shi zuwa gidanka saboda yă ci abinci, yă kuma sha ruwa.’” (Amma yana masa ƙarya ne.)
And he said to him, I am a prophet also as thou art; and an angel spoke to me by the word of Jehovah saying, Bring him back with thee into thy house, that he may eat bread and drink water. He lied unto him.
19 Sai mutumin Allah ya koma tare da shi ya kuma ci ya sha a gidansa.
Then he went back with him, and ate bread in his house, and drank water.
20 Yayinda suke zaune a teburi, sai maganar Ubangiji ta zo wa tsohon annabin da ya dawo da mutumin Allah.
And it came to pass as they sat at the table, that the word of Jehovah came to the prophet that brought him back;
21 Sai tsohon annabin ya tā da murya wa mutumin Allah wanda ya zo daga Yahuda, “Ga abin da Ubangiji ya ce, ‘Ka ƙazantar da maganar Ubangiji, ba ka kuma kiyaye umarnin Ubangiji Allahnka ba.
and he cried to the man of God that came from Judah, saying, Thus saith Jehovah: Forasmuch as thou hast disobeyed the word of Jehovah, and hast not kept the commandment that Jehovah thy God commanded thee,
22 Ka dawo ka ci abinci, ka kuma sha ruwa a wurin da na faɗa maka kada ka ci, ko ka sha. Saboda haka ba za a binne jikinka a kabarin kakanninka ba.’”
but camest back, and hast eaten bread and drunk water in the place of which he said to thee, Eat no bread and drink no water; thy carcase shall not come to the sepulchre of thy fathers.
23 Sa’ad da mutumin Allah ya gama ci da sha, sai annabin da ya dawo da shi ya yi wa jakin mutumin Allah shimfiɗa.
And it came to pass, after he had eaten bread, and after he had drunk, that he saddled the ass for him, for the prophet that he had brought back;
24 Yayinda yake kan hanyarsa, sai wani zaki ya sadu da shi ya kashe shi, aka kuma jefar da jikinsa a kan hanya, jakin da zakin suka tsaya kusa da gawar.
and he departed. And a lion met him by the way and slew him; and his corpse was cast in the way, and the ass stood by it; the lion also stood by the corpse.
25 Waɗansu mutane masu wucewa suka ga an yar da gawar a can, zaki yana tsaye kusa da gawar, sai suka tafi suka ba da labarin a birni inda tsohon annabin nan yake zama.
And behold, men passed by, and saw the corpse cast in the way and the lion standing by the corpse; and they came and told it in the city where the old prophet dwelt.
26 Sa’ad da annabin da ya dawo da mutumin Allah ya ji, sai ya ce, “Mutumin Allah ne, wanda ya ƙazantar da maganar Ubangiji. Ubangiji ya bashe shi ga zaki, wanda ya yayyage shi ya kuma kashe shi, kamar yadda maganar Ubangiji ta gargaɗe shi.”
And the prophet that brought him back from the way heard [of it] and said, It is the man of God who was disobedient to the word of Jehovah; therefore Jehovah has delivered him to the lion, which has torn him and slain him, according to the word of Jehovah which he spoke to him.
27 Sai annabin ya ce wa’ya’yansa, “Ku yi wa jakina shimfiɗa.” Sai suka yi.
And he spoke to his sons saying, Saddle me the ass; and they saddled it.
28 Sai ya fita ya sami an jefar da gawar a hanya, jakin da zakin suna tsaye kusa da shi. Zakin bai ci gawar ko yă yayyage jakin ba.
And he went and found his corpse cast in the way, and the ass and the lion standing by the corpse: the lion had not eaten the corpse, nor torn the ass.
29 Saboda haka annabin ya ɗauki gawar mutumin Allah, ya shimfiɗa shi a kan jaki, ya koma da shi cikin birninsa don yă yi makokinsa yă kuma binne shi.
And the prophet took up the corpse of the man of God, and laid it upon the ass, and brought it back; and the old prophet came into the city, to mourn and to bury him.
30 Sai ya kwantar da gawar a kabarinsa, suka yi makoki a kansa, ya kuma ce, “Ayya, abokina!”
And he laid his corpse in his own sepulchre; and they mourned over him [saying], Alas, my brother!
31 Bayan an binne shi, sai ya ce wa’ya’yansa, “Sa’ad da na mutu, ku binne ni a kabarin da aka binne mutumin Allah; ku kwantar da ƙasusuwana kusa da ƙasusuwansa.
And it came to pass after he had buried him, that he spoke to his sons saying, When I am dead, bury me in the sepulchre in which the man of God is buried; lay my bones beside his bones.
32 Gama annabcin da ya yi ta maganar Ubangiji gāba da bagaden da yake cikin Betel da kuma wuraren sujada a tuddan da suke a biranen Samariya, ba shakka zai cika.”
For the word that he cried by the word of Jehovah against the altar in Bethel, and against all the houses of the high places that are in the cities of Samaria, shall certainly come to pass.
33 Har ma bayan wannan, Yerobowam bai canja daga mugayen hanyoyinsa ba, amma ya ƙara naɗa firistoci domin masujadai da suke kan tuddai daga kowane irin mutane. Duk wanda ya so yă zama firist sai yă naɗa shi don aiki a masujadai da suke kan tuddai.
After this thing Jeroboam turned not from his evil way, but made again from all classes of the people priests of the high places: whosoever would, he consecrated him, and he became [one] of the priests of the high places.
34 Wannan ne zunubin gidan Yerobowam da ya kai ga fāɗuwarsa da kuma hallakarsa daga fuskar duniya.
And by this thing there was sin on the house of Jeroboam, even to cut it off and to destroy it from off the face of the earth.