< 1 Sarakuna 13 >

1 Bisa ga umarnin Ubangiji, sai wani mutumin Allah ya zo daga Yahuda zuwa Betel, yayinda Yerobowam yake tsaye kusa da bagade don yă miƙa hadaya.
Og se, på HERRENs Bud kom en Guds Mand fra Juda til Betel, netop som Jeroboam stod på Alteret for at tænde Offerild.
2 Sai mutumin Allah ya tā da murya a kan bagade bisa ga umarnin Ubangiji ya ce, “Ya bagade, bagade! Ubangiji ya ce, ‘Za a haifi ɗa mai suna Yosiya wa gidan Dawuda. A kanka zai miƙa firistoci na masujadai kan tuddai masu miƙa hadayu a nan, za a kuma ƙone ƙasusuwan mutane a kanka.’”
Og han råbte med HERRENs Ord imod Alteret: "Alter, Alter! Så siger HERREN: Der skal fødes Davids Hus en Søn ved Navn Josias, og på dig skal han ofre Højenes Præster, som tænder Offerild på dig, og han skal brænde Menneskeknogler på dig!"
3 A wannan rana mutumin Allah ya ba da alama, “Ga alamar da Ubangiji ya furta. Wannan bagade zai tsage yă rabu kashi biyu, tokar da yake a kansa za tă zuba a ƙasa.”
Og samtidig kundgjorde han et Tegn, idet han sagde: "Dette er Tegnet på, at HERREN har talet: Se, Alteret skal revne, så Asken derpå vælter ud!"
4 Sa’ad da Yerobowam ya ji abin da mutumin Allah ya tā da murya ya faɗa game da bagaden Betel, sai ya miƙa hannunsa daga bagaden ya ce, “Ku kama shi!” Amma sai hannun da ya miƙa ya yanƙwane, har bai iya janye shi ba.
Da nu Kongen hørte de Ord, den Guds Mand råbte mod Alteret i Betel, rakte Jeroboam sin Hånd ud fra Alteret og sagde: "Grib ham!" Men Hånden, han rakte ud imod ham, visnede, og han kunde ikke tage den til sig igen;
5 Haka ma, bagaden ya rabu, tokarsa kuma ya zuba, bisa ga alamar da mutumin Allah ya bayar, ta wurin kalmar Ubangiji.
og Alteret revnede, så Asken væltede ud fra Alteret - det Tegn, den Guds Mand havde kundgjort med HERRENs Ord.
6 Sai sarki ya ce wa mutumin Allah, “Ka roƙi Ubangiji Allahnka, ka kuma yi addu’a domina don hannuna ya warke.” Saboda haka mutumin Allah ya yi roƙo ga Ubangiji, hannun sarki kuwa ya warke, ya kuma zama kamar yadda yake a dā.
Da tog Kongen til Orde og sagde til den Guds Mand: "Bed dog HERREN din Gud om Nåde og gå i Forbøn for mig, at jeg kan tage Hånden til mig igen!" Og den Guds Mand bad HERREN om Nåde, og Kongen kunde tage Hånden til sig igen, og den var som før.
7 Sai sarki ya ce wa mutumin Allah, “Zo gida tare da ni, ka sami wani abu ka ci, zan kuwa yi maka kyauta.”
Derpå sagde Kongen til den Guds Mand: "Følg med mig hjem og vederkvæg dig, så vil jeg give dig en Gave!"
8 Amma mutumin Allah ya amsa wa sarki, “Ko da za ka ba rabin mallakarka, ba zan tafi tare da kai ba, ba kuwa zan ci abinci, ko in sha ruwa a can ba.
Men den Guds Mand svarede Kongen: "Om du så giver mig Halvdelen af dit Hus, vil jeg ikke følge med dig, og jeg vil hverken spise eller drikke på dette Sted;
9 Gama an umarce ni ta wurin kalmar Ubangiji, aka ce, ‘Kada ka ci abinci, ko ka sha ruwa, ko ka koma ta hanyar da ka zo.’”
thi det Bud har jeg fået med HERRENs Ord: Du må hverken spise eller drikke, og du må ikke vende hjem ad den Vej, du kom!"
10 Saboda haka ya ɗauki wata hanya, bai kuwa koma ta hanyar da ya zo Betel ba.
Derpå drog han bort ad en anden Vej og vendte ikke hjem ad den Vej, han var kommet til Betel.
11 To, fa, akwai wani tsohon annabi yana zama a Betel, wanda’ya’yansa suka zo suka faɗa masa dukan abin da mutumin Allah ya yi a can, a ranar. Suka kuma faɗa wa mahaifinsu abin da ya faɗa wa sarki.
Nu boede der i Betel en gammel Profet; hans Sønner kom og fortalte ham om alt, hvad den Guds Mand den Dag havde gjort i Betel, og om de Ord, han havde talt til Kongen. Men da de havde fortalt deres Fader det,
12 Mahaifinsu ya tambaye su ya ce, “Wace hanya ce ya bi?” Sai’ya’yansa suka nuna masa hanyar da mutumin Allah daga Yahuda ya bi.
spurgte han dem: "Hvilken Vej gik han?" Og hans Sønner viste ham, hvilken Vej den Guds Mand, der var kommet fra Juda, var gået.
13 Sai ya ce wa’ya’yansa, “Ku yi wa jakina shimfiɗa.” Da suka yi wa jakin shimfiɗa, sai ya hau.
Da sagde han til sine Sønner: "Læg Sadelen på mit Æsel!" Og da de havde sadlet Æselet, satte han sig op,
14 Ya bi bayan mutumin Allah. Ya same shi yana zama a ƙarƙashin itace oak, sai ya tambaye shi ya ce, “Kai ne mutumin Allah wanda ya zo daga Yahuda?” Ya amsa, “Ni ne.”
red efter den Guds Mand og traf ham siddende under Egetræet. Han spurgte ham da: "Er du den Guds Mand, der kom fra Juda?" Han svarede: "Ja!"
15 Saboda haka annabin ya ce masa, “Zo gida tare da ni ka ci abinci.”
Så sagde han til ham: "Kom med mig hjem og få noget at spise!"
16 Mutumin Allah ya ce, “Ba zan koma tare da kai ba, ko in ci abinci, ko in sha ruwa tare da kai a can ba.
Men han svarede: "Jeg kan ikke vende om og følge med dig, og jeg kan hverken spise eller drikke sammen med dig på dette Sted,
17 An faɗa mini ta wurin maganar Ubangiji, ‘Kada ka ci abinci, ko ka sha ruwa a can, ko ka koma ta hanyar da ka zo.’”
thi der er sagt mig med HERRENs Ord: Du må hverken spise eller drikke der, og du må ikke vende tilbage ad den Vej, du kom!"
18 Sai annabin ya amsa, “Ni ma annabi ne, kamar ka. Kuma mala’ika ya ce mini ta wurin kalmar Ubangiji, ‘Dawo da shi zuwa gidanka saboda yă ci abinci, yă kuma sha ruwa.’” (Amma yana masa ƙarya ne.)
Da sagde han til ham: "Også jeg er Profet som du, og en Engel har med HERRENs Ord sagt til mig: Tag ham med dig hjem, for at han kan få noget at spise og drikke!" Men han løj for ham.
19 Sai mutumin Allah ya koma tare da shi ya kuma ci ya sha a gidansa.
Så vendte han tilbage med ham og spiste og drak i hans Hus.
20 Yayinda suke zaune a teburi, sai maganar Ubangiji ta zo wa tsohon annabin da ya dawo da mutumin Allah.
Men medens de sad til Bords, kom HERRENs Ord til Profeten, der havde fået ham tilbage,
21 Sai tsohon annabin ya tā da murya wa mutumin Allah wanda ya zo daga Yahuda, “Ga abin da Ubangiji ya ce, ‘Ka ƙazantar da maganar Ubangiji, ba ka kuma kiyaye umarnin Ubangiji Allahnka ba.
og han råbte til den Guds Mand, der var kommet fra Juda: "Så siger HERREN: Fordi du har været genstridig mod HERRENs Ord og ikke holdt det Bud, HERREN din Gud pålagde dig,
22 Ka dawo ka ci abinci, ka kuma sha ruwa a wurin da na faɗa maka kada ka ci, ko ka sha. Saboda haka ba za a binne jikinka a kabarin kakanninka ba.’”
men vendte tilbage og spiste og drak på det Sted, hvor han sagde, du ikke måtte spise og drikke, derfor skal dit Lig ikke komme i dine Fædres Grav!"
23 Sa’ad da mutumin Allah ya gama ci da sha, sai annabin da ya dawo da shi ya yi wa jakin mutumin Allah shimfiɗa.
Efter at han havde spist og drukket, sadlede han Æselet til ham, og han gav sig på Hjemvjen.
24 Yayinda yake kan hanyarsa, sai wani zaki ya sadu da shi ya kashe shi, aka kuma jefar da jikinsa a kan hanya, jakin da zakin suka tsaya kusa da gawar.
Men en Løve kom imod ham på Vejen og dræbte ham. Og hans Lig lå henslængt på Vejen, og Æselet stod ved Siden af; også Løven stod ved Siden af Liget.
25 Waɗansu mutane masu wucewa suka ga an yar da gawar a can, zaki yana tsaye kusa da gawar, sai suka tafi suka ba da labarin a birni inda tsohon annabin nan yake zama.
Og se, nogle Mænd kom der forbi og så Liget ligge henslængt på Vejen, og Løven stå ved Siden af, og de kom og fortalte det i Byen, hvor den gamle Profet boede;
26 Sa’ad da annabin da ya dawo da mutumin Allah ya ji, sai ya ce, “Mutumin Allah ne, wanda ya ƙazantar da maganar Ubangiji. Ubangiji ya bashe shi ga zaki, wanda ya yayyage shi ya kuma kashe shi, kamar yadda maganar Ubangiji ta gargaɗe shi.”
og da Profeten, der havde fået ham til at vende om, hørte det, sagde han: "Det er den Guds Mand, som var genstridig mod HERRENs Ord; derfor har HERREN givet ham i Løvens Vold, og den har sønderrevet ham og dræbt ham efter det Ord, HERREN talede til ham!"
27 Sai annabin ya ce wa’ya’yansa, “Ku yi wa jakina shimfiɗa.” Sai suka yi.
Derpå sagde han til sine Sønner: "Læg Sadelen på mit Æsel!" Og da de havde gjort det,
28 Sai ya fita ya sami an jefar da gawar a hanya, jakin da zakin suna tsaye kusa da shi. Zakin bai ci gawar ko yă yayyage jakin ba.
red han hen og fandt hans Lig liggende henslængt på vejen og Æselet og Løven stående ved Siden af, uden at Løven havde ædt Liget eller sønderrevet Æselet.
29 Saboda haka annabin ya ɗauki gawar mutumin Allah, ya shimfiɗa shi a kan jaki, ya koma da shi cikin birninsa don yă yi makokinsa yă kuma binne shi.
Da løftede Profeten den Guds Mands Lig op, lagde ham på Æselet og førte ham tilbage til Byen for at holde Dødeklage og jorde ham;
30 Sai ya kwantar da gawar a kabarinsa, suka yi makoki a kansa, ya kuma ce, “Ayya, abokina!”
og da han havde lagt Liget i sin egen Grav, holdt de Dødeklage over ham og sagde: "Ak ve min Broder!"
31 Bayan an binne shi, sai ya ce wa’ya’yansa, “Sa’ad da na mutu, ku binne ni a kabarin da aka binne mutumin Allah; ku kwantar da ƙasusuwana kusa da ƙasusuwansa.
Og efter at have jordet ham sagde han til sine Sønner: "Når jeg dør, skal I lægge mig i samme Grav, som den Guds Mand ligger i; ved Siden af hans Ben skal I lægge mig, for at mine Ben kan blive skånet sammen md hans;
32 Gama annabcin da ya yi ta maganar Ubangiji gāba da bagaden da yake cikin Betel da kuma wuraren sujada a tuddan da suke a biranen Samariya, ba shakka zai cika.”
thi det Ord skal gå i Opfyldelse, som han med HERRENs Ord råbte mod Alteret i Betel og alle Offerhusene på Højene i Samarias Byer!"
33 Har ma bayan wannan, Yerobowam bai canja daga mugayen hanyoyinsa ba, amma ya ƙara naɗa firistoci domin masujadai da suke kan tuddai daga kowane irin mutane. Duk wanda ya so yă zama firist sai yă naɗa shi don aiki a masujadai da suke kan tuddai.
Heller ikke efter denne Begivenhed opgav Jeroboam sin onde Færd, men gjorde på ny alle Slags Folk til Præster på Højene, idet han indsatte enhver, der havde Lyst, til Præst på Højene.
34 Wannan ne zunubin gidan Yerobowam da ya kai ga fāɗuwarsa da kuma hallakarsa daga fuskar duniya.
Og det blev Jeroboams Hus til Synd og førte til, at det blev tilintetgjort og udryddet af Jorden.

< 1 Sarakuna 13 >