< 1 Sarakuna 12 >

1 Rehobowam ya tafi Shekem, gama dukan Isra’ila sun je can don su naɗa shi sarki.
Och Rehabeam drog till Sichem; förty hela Israel var kommen till Sichem, till att göra honom till Konung.
2 Sa’ad da Yerobowam ɗan Nebat ya ji labari (gama har yanzu yana a Masar, inda ya gudu daga Sarki Solomon), sai ya dawo daga Masar.
Och då Jerobeam, Nebats son, det hörde, der han ännu i Egypten var, dit han för Konung Salomo flydd var, kom han igen utur Egypten.
3 Saboda haka mutane suka aika Yerobowam yă zo, sai shi da dukan taron Isra’ila suka tafi wurin Rehobowam, suka ce masa,
Och de sände bort, och läto kalla honom. Och Jerobeam samt med hela Israels menighet kommo, och talade med Rehabeam, och sade:
4 “Mahaifinka ya sa mana kaya mai nauyin gaske, amma yanzu ka sassauta wannan aiki mai zafi, da kuma kaya masu nauyin da ya sa a kanmu, mu kuwa za mu bauta maka.”
Din fader hafver gjort vårt ok för svårt; så gör nu du den hårda tjensten, och det svåra oket lättare, det han oss pålagt hafver, så vilje vi vara dig underdånige.
5 Rehobowam ya amsa, “Ku tafi, bayan kwana uku, ku dawo.” Sai mutane suka watse.
Men han sade till dem: Går edra färde intill tredje dagen, och kommer så till mig igen. Och folket gick sina färde.
6 Sai Sarki Rehobowam ya nemi shawarar dattawa waɗanda suka yi wa mahaifinsa Solomon, hidima a kwanakinsa. Ya ce, “Wace shawara ce za ku ba ni don in amsa wa waɗannan mutane?”
Och Konung Rehabeam höll råd med de äldsta, som för hans fader Salomo stodo, då han lefde, och sade: Huru råden I, att vi måge gifva desso folkena svar?
7 Suka amsa, “In a yau za ka zama bawan waɗannan mutane, ka kuma yi musu hidima, ka ba su amsa mai kyau, kullum za su kasance bayinka.”
De sade till honom: Om du i denna dag gör desso folkena en tjenst, och är dem till vilja, och hörer dem, och gifver dem god ord, så blifva de dig underdånige så länge du lefver.
8 Amma Rehobowam ya ƙi shawarar da dattawan suka ba shi, sai ya nemi shawarar matasa waɗanda suka yi girma tare, waɗanda kuma suke masa hidima.
Men han öfvergaf de äldstas råd, som de honom gifvit hade; och höll ett råd med de unga, som med honom uppväxte voro, och för honom stodo.
9 Ya tambaye su, “Mece ce shawararku? Yaya za mu amsa wa waɗannan mutane masu cewa, ‘Ka sassauta nauyin da mahaifinka ya sa a kanmu’?”
Och han sade till dem: Hvad råden I, det vi desso folkena svara skole, som till mig sagt hafva: Gör det oket lättare, som din fader uppå oss lagt hafver?
10 Matasan, waɗanda suka yi girma tare da shi, suka amsa, “Faɗa wa waɗannan mutanen da suka ce maka, ‘Mahaifinka ya sa kaya masu nauyi a kanmu, amma ka sassauta kayanka.’ Ka ce musu, ‘Ƙaramin yatsana ya fi ƙugun tsohona kauri.
Och de unge, som med honom uppväxte voro, sade till honom: Till folket, som till dig säger: Din fader hafver gjort vårt ok för svart, gör du oss det lättare; skall du säga: Mitt minsta finger skall tjockare vara än mins faders länder.
11 Mahaifina ya sa muku kaya masu nauyi; ni zan ma sa su fi haka nauyi. Mahaifina ya hore ku da bulala; ni kuwa zan hore ku da kunamai.’”
Min fader hafver lagt på eder ett svårt ok; men jag skall ännu föröka det öfver eder. Min fader hafver tuktat eder med gisslar; jag skall tukta eder med scorpioner.
12 Bayan kwana uku, Yerobowam da dukan mutane suka dawo wurin Rehobowam yadda sarki ya faɗa, “Ku dawo gare ni cikin kwana uku.”
Alltså kom Jerobeam med allo folkena till Rehabeam på tredje dagen, såsom Konungen talat hade, och sagt: Kommer igen till mig på tredje dagen.
13 Sai Sarki ya amsa wa mutane da zafi. Yana ƙin shawarar da dattawa suka ba shi.
Och Konungen gaf folkena ett hårdt svar, och öfvergaf det råd, som de äldste honom gifvit hade;
14 Ya bi shawarar matasa, ya ce, “Mahaifina ya sa muku kaya masu nauyi; ni zan ma sa su fi haka nauyi. Mahaifina ya hore ku da bulala; ni kuwa zan hore ku da kunamai.”
Och talade med dem efter de ungas råd, och sade: Min fader hafver gjort edart ok svårt; men jag vill ännu mer föröka det öfver eder. Min fader hafver tuktat eder med gisslar; men jag skall tukta eder med scorpioner.
15 Saboda haka sarki bai saurare mutane ba, gama wannan abin da ya faru daga wurin Ubangiji ne, don a cika maganar Ubangiji da ya yi wa Yerobowam ɗan Nebat ta wurin Ahiya, mutumin Shilo.
Alltså hörde Konungen intet folket; ty Herren vände det så, på det han skulle stadfästa sitt ord, som Herren genom Ahia af Silo sagt hade till Jerobeam, Nebats son.
16 Da dukan Isra’ila suka ga sarki ya ƙi yă saurare su, sai suka amsa wa sarki, “Ina ruwanmu da Dawuda! Ai! Ba mu da gādo wurin ɗan Yesse. Ya Isra’ila, kowa yă koma tentinsa! Dawuda, sai ka lura da gidanka!” Saboda haka Isra’ilawa suka watse zuwa gida.
Då nu hele Israel såg, att Konungen intet ville höra dem, gaf folket Konungenom ett svar, och sade: Hvad del hafve vi i David, eller arf i Isai son? Israel, gack i dina hyddor; så se nu du till ditt hus, David. Alltså gick Israel i sina hyddor;
17 Amma ga Isra’ilawan da suke zama a garuruwan Yahuda kuwa, Rehobowam ya ci gaba da mulki a kansu.
Så att Rehabeam rådde allenast öfver de Israels barn, som bodde i Juda städer.
18 Sarki Rehobowam ya aiki Adoniram wanda yake shugaban aikin gandu, amma Isra’ila suka jajjefe shi da dutse har ya mutu. Sarki Rehobowam, ya sullale ya hau keken yaƙinsa ya tsere zuwa Urushalima.
Och då Konung Rehabeam sände åstad Adoram räntomästaren, kastade hele Israel honom ihjäl med stenar; men Konungen Rehabeam steg med hast på en vagn, och flydde till Jerusalem.
19 Tun daga wannan ranar ne mutanen Isra’ila suka shiga gāba da gidan Dawuda har wa yau.
Alltså föll Israel ifrå Davids hus, allt intill denna dag.
20 Sa’ad da dukan Isra’ilawa suka ji Yerobowam ya dawo, sai suka aika, suka kira shi zuwa taro, suka kuma naɗa shi sarki bisa dukan Isra’ila. Kabila Yahuda kaɗai ta kasance mai biyayya ga gidan Dawuda.
Då nu hele Israel hörde, att Jerobeam var igenkommen, sände de bort, och läto kalla honom till alla menighetena, och gjorde honom till Konung öfver hela Israel; och ingen följde Davids hus, utan Juda slägt allena.
21 Da Rehobowam ya isa Urushalima, ya tattara dukan gidan Yahuda da kabilar Benyamin, ya sami sun kai mayaƙa dubu da tamanin. Sai aka shirya don su yaƙi gidan Isra’ila, su kuma mayar da masarautar wa Rehobowam ɗan Solomon.
Och då Rehabeam kom till Jerusalem, församlade han hela Juda hus, och BenJamins slägt, hundrade och åttatio tusend unga stridsamma män, till att strida emot Israels hus, och draga riket igen till Rehabeam, Salomos son.
22 Amma waɗannan kalmomin Allah suka zo wa Shemahiya, mutumin Allah, cewa,
Men Guds ord kom till den Guds mannen Semaja, och sade:
23 “Faɗa wa Rehobowam ɗan Solomon, sarkin Yahuda, ka faɗa wa dukan gidan Yahuda da Benyamin, da kuma dukan sauran mutane,
Tala till Rehabeam, Salomos son, Juda Konung, och till hela Juda hus, och BenJamin, och till det andra folket, och säg:
24 ‘Ga abin da Ubangiji ya ce, “Kada ku haura don ku yi yaƙi da’yan’uwanku, Isra’ilawa. Ku koma gida, kowannenku, gama wannan aikina ne.”’” Saboda haka suka yi biyayya da maganar Ubangiji, suka sāke watse zuwa gida, yadda Ubangiji ya umarta.
Detta säger Herren: I skolen icke draga upp, och strida emot edra bröder Israels barn; hvar och en gånge åter hem; ty detta är skedt af mig. Och de lydde Herrans ord, och vände om, och gingo sin väg, såsom Herren sagt hade.
25 Sai Yerobowam ya ƙara gina Shekem a ƙasar tudu ta Efraim, ya zauna a can. Daga can ya tafi ya gina Fenuwel.
Men Jerobeam byggde Sichem på Ephraims berg, och bodde deruti, och drog dädan ut, och byggde Pnuel.
26 Yerobowam ya yi tunani a ransa ya ce, “Mai yiwuwa mulkin yă koma gidan Dawuda.
Men Jerobeam tänkte i sitt hjerta: Nu varder riket fallandes till Davids hus igen;
27 In waɗannan mutane sun riƙa haurawa don su miƙa hadayu a haikalin Ubangiji a Urushalima. Za su sāke nuna biyayya ga mai girma, Rehobowam, sarkin Yahuda. Za su kashe ni su kuma koma ga Sarki Rehobowam.”
Om detta folk skall gå ditupp, till att offra i Herrans hus i Jerusalem, och detta folkets hjerta varder sig vändandes till deras herra Rehabeam, Juda Konung, och slå mig ihjäl, och falla igen till Rehabeam, Juda Konung.
28 Bayan ya nemi shawara, sai sarki ya yi siffofin’yan maruƙa biyu na zinariya. Ya ce wa mutane, “Kun daɗe kuna haurawa zuwa can Urushalima. Ga allolinku, ya Isra’ila, waɗanda suka fitar da ku daga ƙasar Masar.”
Och Konungen höll ett råd, och gjorde två gyldene kalfvar, och sade till dem: Det är eder för tungt gå upp till Jerusalem; si, der är din gud, Israel, som dig utur Egypti land fört hafver;
29 Sai ya kafa ɗaya a Betel, ɗaya kuma a Dan.
Och satte endera i BethEl, och den andra i Dan.
30 Wannan ya zama zunubi, gama mutane suna tafiya yin wa wannan da yake a Betel sujada, su kuma je har Dan don su yi wa ɗayan sujada.
Och det vardt till synd; ty folket gick bort för dem ena, allt intill Dan.
31 Yerobowam ya gina masujadai da suke kan tuddai, ya kuma naɗa firistoci barkatai daga cikin mutanen da ba na zuriyar Lawi ba.
Han gjorde också ett höjdars hus, och gjorde Prester utaf de ringesta i folket, de icke af Levi barnom voro.
32 Ya kafa biki a rana ta goma sha biyar ta watan takwas, kamar bikin da ake yi a Yahuda, ya kuma miƙa hadayu a bisa bagade. Ya yi haka a Betel, yana miƙa wa siffofin maruƙan da ya yi hadayu. A Betel kuma ya naɗa firistoci a wuraren tudun da ya yi.
Och han gjorde en högtid, på femtonde dagen i åttonde månadenom, såsom den högtiden i Juda, och offrade på altarena. Så gjorde han i BethEl, att man offrade kalfvomen, som han gjort hade; och skickade i BethEl Prester till höjderna, som han gjort hade;
33 A rana ta goma sha biyar ta watan takwas, watan da ya zaɓa, ya miƙa hadayu a bisa bagaden da ya gina a Betel. Saboda haka ya kafa biki don Isra’ilawa, ya kuma haura zuwa bagade don yă miƙa hadayu.
Och offrade på altaret, som han gjort hade i BethEl, på femtonde dagen i åttonde månadenom, hvilken han utu sitt hjerta upptänkt hade; och gjorde Israels barnom högtider, och offrade på altaret, det man röka skulle.

< 1 Sarakuna 12 >